Sashe 53
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Zata ai watar da...!".
Shiru yayi ba tare daya k'arishe mgnar tashi ba sabida, jin Dr Aliyu na cewa.
"Ya isa! in yasan hakan zai sa mishi fargaba."
sai ya kumo judo ya fuskanci Saifuddeen dan dama da zaiwa Dr Ayman mgna kauda kanshi yayi tunda yasan in Saifuddeen d'in yaga motsin lab'b'anshi zai gane me yake fad'in.
shi kuwa Saifuddeen kai ya jujjuya tare da d'ago hannunshi a hankali ya d'aura kan mararshi,
sai ya kuma janye hannun tare da kallon fuskar Dr Aliyu kana ya nuna mishi kan mararshi zuwa kan joystick inshi,
sannan ya had'e girarshi wuri d'aya tare da tsuke jajayen lips enshi, kana ya fara mutsu-mutsu alamun Yana son tashi zaune,
cikin saurin fahimta Dr Aliyu yace.
"Mararka ta cika ne?." kai ya gyad'a mishi alamar eh,
ganin haka Dr Ayman yayi saurin jawo wani d'an abu ya mik'a Dr Aliyu, amsa yayi tare da kamo joystick en nashi ya mana bakin robar.
Ido ya rumtse tare da girgiza musu kai kana ya had'a yatsunshi biyu alamun a cire mishi, fahimtar haka yasa Dr Aliyu janye robar kana ya bud'a bakinta sannan ya zura kan kaciyarshi cikin bakin robar daya bud'a sannan ya kalleshi tare da cewa.
"Kayi."
ido ya lumshe cikin tarin kunya duk da yasan Dr Aliyu ya kai sa'an mahaifinshi hakama Dr Ayman zai girmeshi matuk'a kuma duk mazane yan uwanshi, sai kuma Dr Batulu da yasan tabbas zata haifi kamarshi, sannan kuma tama juya baya bata ganinshi,
amman duk da haka yana mai matuk'ar jin kunya duk da ya gane halin da ya ke ciki na kasantuwar wata sabuwar nakasa wani irin suya da maƙaƙi da ɗaci zuciyarshi ke mushi to amman ya yarda da wannan sabuwar ƙaddara tasa yasan tun ran gini tun ran zane.
Su kuwa likitovin hakan ya sasu karsashi domin alamace ta nuna cutarsa batayi tsauri ba, alamace ta nuna bai samu damage sosai a jikin ba.
Bayan ya gama yin fitsarin Dr Ayman ya gyara mishi jikinshi ne,
sannan suka fara shirin yi mishi aikin taimakon gaggawa, kafin asan matakin da za'a d'auka, yayinda Dr Aliyu ya fara mishi nasiha cikin taushin lafazi yace.
"Saifuddeen kayi addu'a da fatan Allah ya bamu sa'an aiki, kana kasa a ranka nakasa ba kasawa bace, ka jajircewa zuciyarka, kasa a ranka wannan jarrabawace da ubangiji kan iya jarabtan dukkan bawanshi,
kaga misali a kaina gani bana iya mik'ewa tsaye kuma rana tsaka larurar ta sameni sakamakon had'arin mota,
wanda lokacin ina ganiyar k'uruciya ta, na gama karatu na kenan na fara aiki da mako biyu nayi hatsarin, wanda saida akayi tsawon shekaru biyu ana jinyata kafin na fara tashi zaune da kaina, kumani a lokacinma nakasata ta shafi lafiyata a matsayina na d'a namiji, koda na yarda da k'addara, nasan cewa jarrabawace bayan shekara 8 da faruwar abun lfyar mazan takana ya fara dawowa cikin ikon Allah kafin na cika 10 years da yin had'ari har nayi aure
sai da muka shekara 7 da ita kafin Allah ya bamu ciki a lokacin har na cire tsamnani,
Allah da ikonshi ciki nada wata 5 ya bare.
Nayi matuk'ar shiga damuwa a lokacin ashe abinda bamu saniba, cikin tagwaye ne d'ayan nan bai bareba,
bayan wata hud'u aka haifa min d'iya mace, daga kanta kuma Allah bai bamu waniba,
to nima kenan da nakasata tafi taka in sha Allah kai muna sa ran zaka samu lfy kuma Alhamdulillahi kaga kai matsalar bata shafi mazantakan kaba.
kasa a ranka kana nan da lfyarka."
kai ya rausayar tare da lumshe ido kana ya gyad'a kanshi kai alamar.
"To, ngd."
daga nan suka fara aikinsu ba kama hannun yaro, babu mgna sai nuneneniya, tuk'uru suka duk'ufa kanshi.
A can waje kuwa Ummi aje carbin hannunta tayi kana ta jawo wayarta ta fara karatun qura'an tanayi tana nemawa gudan jinin ta lfy a wurin mai rayawa mai kashewa mai badawa mai hanawa, Allahu wahidun k'ahharar.
Ya Rabi'u kuwa ya d'auki Aunty Mami sun tafi ya maidata gida, dan tayiwa bak'in nasu abinci, kana shi kuwa ya wuce ma'aikatansu.
Ishaq kuwa da Ahmad suna nan zaune suna dakon fitowan doctors dan suji menene matsalar Saifuddeen d'in.
Kana Hayatunddeen kuwa ya tafi Airport dan tarbo Dr Adnan.
Bayan kamar awa biyu suka fito a jere, Dr Ayman yana turawa weelchair d'in da Dr Aliyu ke zaune, yayinda, Dr Batulu ke biye dasu a baya.
Suna fitowa Dr Adnan da suka ise bada jimawa ba, ya mik'e da sauri, ya nufi inda suke hakama Ahmad da Ishaq wanda kunnuwanshi ke mishi jagora duk inda sautin muryarsu da sautin takun Ahmad yake bi, kai baka tab'a cewa makaho bane, domin mutunne mai cikar zarrah da zati kekyawane mai tarin tsabta da yawa sukance suna ɗan kama da Saifuddeen.
cikin girmamawa Dr Adnan ya d'an rusuno ya bawa Dr Aliyu hannu tare da cewa.
"Barka da hantsi sir."
cikin kula da dottaku Dr Aliyu yayi murmushi irin nasu na manyan doctors kana yace.
"Barka dai Adnan ashe har ka iso, ya hanya."
"Alhamdulillahi ya aiki?." Adnan yace yana bin bayansu shida Ishaq da Ahmad suka shiga tamfatsetsen office d'in Dr Aliyun.
Ummi kuwa addu'a tayi kana ta kife wayar bisa cinyarta,
ido ta zuwaba Hayatuddeen dake tsaye gaban Dr Batulu yana neman a barshi ya shiga yaga d'an uwan nashi.
cikin kula tace.
"Kayi hak'uri bayan mun gama aikin bashi taimakon gaggawa an mishi allurar bacci so ana buk'atar ya huta."
sai ta kuma matso gaban Ummi da idanunta suka cika da hawaye,
ganin tazo gabanta Ummi tace.
"Dan Allah Dr ki gaya min halin da yake ciki? koda baya rayene kada ki boye min, tunda abinnnan ya farufa bangashi ba sai dai in haggoshi daga nesa, ke uwace kinsan abinda uwa kanji in makamancin wannan ya faru da d'anta please me ya sameshi?."
a hankali Dr Batulu ta zauna gefenta kana ta dafa kafad'arta tare da cewa.
"Abinda ma muke zaton zaiyi tsanani sai muka sameshi da sauk'i,
Saifuddeen bai mutuba yana raye kuma insha Allah da yamma ni da kaina zan shigar dake inda yake, kafin nan ya farka zaki ganshi ya ganki kuyi mgna dashi, yanzu dai da ku koma gida domin nan akwai masu kula dashi.
wadanda Dr Aliyu ya tanatar su zasu mishi komai,
sannan batun abinci ma karku damu akwai d'iyar Dr d'in duk abinda za'a bashi damar ci ita zata shirya mishi komai.
Yanzu kuje gida da yamma Ku dawo,zaku ganshi kuma Dr Aliyu zai gaya muku duk abinda ke damushi da matakin daya kamata ku dauka dama yadda zaku kula dashi."
sosai Ummi ta gamsu da bayananta kana taji sanyi a ranta, haka yasa tace.
"To ba matsala ngd matuk'a Dr in sha zanyita addu'a zamu koma biyar na yamma zamu juyo."
cikin fara samun nitsuwa Hayatuddeen yace,
"Dr zai gane mu ko? numfashi sa ya dai ta ko?."
kai ta gyad'a mishi tare da cewa.
"Sosai ma har magna fa yanayi mana da body language alamun yana gane duk abinda muke cewa."
a tare sukace Alhamdulillahi.
sannan Dr Batulu ta bawa Ummi number ta kan in sun dawo da yamma su nemata.
Su Abban Farida kuwa, da Dr Adnan da Ishaq bayasu shiga sun so Dr Aliyu yayi musu bayanin matsalar Saifuddeen, so amman sai ya basu hak'uri sabida ya gaji yana buk'atan hutu ya dai ce suje da yamma su dawo dukansu yana son ganinsu dan zai musu cikekken bayanin matsalar Saifuddeen d'in da basu shawara da da gaya musu dabarun kula dashi.
dole suka hak'ura kan saida yamman in sun dawo.
Kai tsaye gidan Ya Rabi'u suka wuce dan Ishaq ya k'i su Ahmad da Adnan suje su kama hotel.
A motar da Ya Rabi'u ya bari a hannun Hayatuddeen suka tafi,
amman Ahmad ya karb'i tukin a cewarshi Hayatuddeen d'an koyone bazai yarda ya jasuba,
Ummi na gaba kusa da Ahmad kana Ishaq da Adnan da Hauatudeen suna baya a haka suka tafi.
Aunty Mami kuwa tuni ta shirya musu abinci tasa an gyara BQ ensu.
*A garin Gombawa d'iban fari*
Yau tunda sanyin safiya Zaleeha ta shirya domin zata je kaltingo don zantawa da nakasassun wannan yankin.
Amman har zuwa ƙarfe taƙwas na safiyar ta gaza yin komai, ji takeyi tamkar tayi ta kurma ihu ta faɗi abinda folisawannan suka haneta faɗi tare dayi mata barazana da ranshi,
kukan da takeyi ya sanya ida nunta kumbura sukayi jazir ga wani fitinennen ciwon kai, ya zatayi a duniya ko wacw ƴa in tanada matsala uwarta take fara tinkara ,amman sam Mama itama bayan folisawan tabi.
tafin hannunta tasa ta share hawayenta a karo na barkatai, a hankali ta miƙe kana ta zari car key ɗinta, a falo ta samu Mama a hankali ta gaiseda da muryarta dake disashe, cikin haɗe fuska tace.
"Wato dai bazaki bar koke-koken nan ba ko, so kike sai an gane wani abu ya faru da ke ko?."
Kai ta jinjina cikin sanyi tace.
"Mama ai wani abu kam yama faru, sanadi nane fa akayi mishi komai, ban saniba yana raye ko ya mutu wani hali yake? tun randa abin ya faru da dare washegari naje asibitoci sunfi bakwai babushi ba dalilinshi, ni badan raina da sukayi min barazana da shiba, a a shida yake hannunsu nakeji kar su ƙara cutarmin dashi." ta ƙarishe maganar wasu zafafan hawaye na kwaranyo mata,
ita kuwa Mama kasake tayi tare da cewa.
"eyeh sannu uwarshi harda su wani kada su ƙara cutar miki dashi kamar kece uwarsa ko ƙanwarsa ko matarsa lallai Zaleeha kifa kiyayeni tam!."
tana faɗin haka tayi cikin kitchen, ita kuwa Zaleeha rumtse ido tayi hawayen dake ciki suka silalo kana ta fita ta nufi falon Baba Malam ,bayan sun gaisane ta ɗan gyara zama ciin disashewar murya tace.
"Baba Malam bari in fita zanje gidan Adda Maryam daga nan zanje asibiti dubo wani mara lfy, Baba Malam a sashi a addu'a Allah ya bashi lfy ya kareshi da sharrin masu sharri."
murmushi dottijon yayi tare da cewa,
"To Mamana in sha Allah zan sashi a addu'a Allah ya bashi lfy, kuma in kinje asibitin bashi kaɗai zaki duba ki ɗan zazzagaya ki tuba wasuma dan ki samu ladan dake cikin hakan." kai ta gyaɗa kana tamiƙe tare da sallamanshi ta
tafi.
Shiru yayi ba tare daya k'arishe mgnar tashi ba sabida, jin Dr Aliyu na cewa.
"Ya isa! in yasan hakan zai sa mishi fargaba."
sai ya kumo judo ya fuskanci Saifuddeen dan dama da zaiwa Dr Ayman mgna kauda kanshi yayi tunda yasan in Saifuddeen d'in yaga motsin lab'b'anshi zai gane me yake fad'in.
shi kuwa Saifuddeen kai ya jujjuya tare da d'ago hannunshi a hankali ya d'aura kan mararshi,
sai ya kuma janye hannun tare da kallon fuskar Dr Aliyu kana ya nuna mishi kan mararshi zuwa kan joystick inshi,
sannan ya had'e girarshi wuri d'aya tare da tsuke jajayen lips enshi, kana ya fara mutsu-mutsu alamun Yana son tashi zaune,
cikin saurin fahimta Dr Aliyu yace.
"Mararka ta cika ne?." kai ya gyad'a mishi alamar eh,
ganin haka Dr Ayman yayi saurin jawo wani d'an abu ya mik'a Dr Aliyu, amsa yayi tare da kamo joystick en nashi ya mana bakin robar.
Ido ya rumtse tare da girgiza musu kai kana ya had'a yatsunshi biyu alamun a cire mishi, fahimtar haka yasa Dr Aliyu janye robar kana ya bud'a bakinta sannan ya zura kan kaciyarshi cikin bakin robar daya bud'a sannan ya kalleshi tare da cewa.
"Kayi."
ido ya lumshe cikin tarin kunya duk da yasan Dr Aliyu ya kai sa'an mahaifinshi hakama Dr Ayman zai girmeshi matuk'a kuma duk mazane yan uwanshi, sai kuma Dr Batulu da yasan tabbas zata haifi kamarshi, sannan kuma tama juya baya bata ganinshi,
amman duk da haka yana mai matuk'ar jin kunya duk da ya gane halin da ya ke ciki na kasantuwar wata sabuwar nakasa wani irin suya da maƙaƙi da ɗaci zuciyarshi ke mushi to amman ya yarda da wannan sabuwar ƙaddara tasa yasan tun ran gini tun ran zane.
Su kuwa likitovin hakan ya sasu karsashi domin alamace ta nuna cutarsa batayi tsauri ba, alamace ta nuna bai samu damage sosai a jikin ba.
Bayan ya gama yin fitsarin Dr Ayman ya gyara mishi jikinshi ne,
sannan suka fara shirin yi mishi aikin taimakon gaggawa, kafin asan matakin da za'a d'auka, yayinda Dr Aliyu ya fara mishi nasiha cikin taushin lafazi yace.
"Saifuddeen kayi addu'a da fatan Allah ya bamu sa'an aiki, kana kasa a ranka nakasa ba kasawa bace, ka jajircewa zuciyarka, kasa a ranka wannan jarrabawace da ubangiji kan iya jarabtan dukkan bawanshi,
kaga misali a kaina gani bana iya mik'ewa tsaye kuma rana tsaka larurar ta sameni sakamakon had'arin mota,
wanda lokacin ina ganiyar k'uruciya ta, na gama karatu na kenan na fara aiki da mako biyu nayi hatsarin, wanda saida akayi tsawon shekaru biyu ana jinyata kafin na fara tashi zaune da kaina, kumani a lokacinma nakasata ta shafi lafiyata a matsayina na d'a namiji, koda na yarda da k'addara, nasan cewa jarrabawace bayan shekara 8 da faruwar abun lfyar mazan takana ya fara dawowa cikin ikon Allah kafin na cika 10 years da yin had'ari har nayi aure
sai da muka shekara 7 da ita kafin Allah ya bamu ciki a lokacin har na cire tsamnani,
Allah da ikonshi ciki nada wata 5 ya bare.
Nayi matuk'ar shiga damuwa a lokacin ashe abinda bamu saniba, cikin tagwaye ne d'ayan nan bai bareba,
bayan wata hud'u aka haifa min d'iya mace, daga kanta kuma Allah bai bamu waniba,
to nima kenan da nakasata tafi taka in sha Allah kai muna sa ran zaka samu lfy kuma Alhamdulillahi kaga kai matsalar bata shafi mazantakan kaba.
kasa a ranka kana nan da lfyarka."
kai ya rausayar tare da lumshe ido kana ya gyad'a kanshi kai alamar.
"To, ngd."
daga nan suka fara aikinsu ba kama hannun yaro, babu mgna sai nuneneniya, tuk'uru suka duk'ufa kanshi.
A can waje kuwa Ummi aje carbin hannunta tayi kana ta jawo wayarta ta fara karatun qura'an tanayi tana nemawa gudan jinin ta lfy a wurin mai rayawa mai kashewa mai badawa mai hanawa, Allahu wahidun k'ahharar.
Ya Rabi'u kuwa ya d'auki Aunty Mami sun tafi ya maidata gida, dan tayiwa bak'in nasu abinci, kana shi kuwa ya wuce ma'aikatansu.
Ishaq kuwa da Ahmad suna nan zaune suna dakon fitowan doctors dan suji menene matsalar Saifuddeen d'in.
Kana Hayatunddeen kuwa ya tafi Airport dan tarbo Dr Adnan.
Bayan kamar awa biyu suka fito a jere, Dr Ayman yana turawa weelchair d'in da Dr Aliyu ke zaune, yayinda, Dr Batulu ke biye dasu a baya.
Suna fitowa Dr Adnan da suka ise bada jimawa ba, ya mik'e da sauri, ya nufi inda suke hakama Ahmad da Ishaq wanda kunnuwanshi ke mishi jagora duk inda sautin muryarsu da sautin takun Ahmad yake bi, kai baka tab'a cewa makaho bane, domin mutunne mai cikar zarrah da zati kekyawane mai tarin tsabta da yawa sukance suna ɗan kama da Saifuddeen.
cikin girmamawa Dr Adnan ya d'an rusuno ya bawa Dr Aliyu hannu tare da cewa.
"Barka da hantsi sir."
cikin kula da dottaku Dr Aliyu yayi murmushi irin nasu na manyan doctors kana yace.
"Barka dai Adnan ashe har ka iso, ya hanya."
"Alhamdulillahi ya aiki?." Adnan yace yana bin bayansu shida Ishaq da Ahmad suka shiga tamfatsetsen office d'in Dr Aliyun.
Ummi kuwa addu'a tayi kana ta kife wayar bisa cinyarta,
ido ta zuwaba Hayatuddeen dake tsaye gaban Dr Batulu yana neman a barshi ya shiga yaga d'an uwan nashi.
cikin kula tace.
"Kayi hak'uri bayan mun gama aikin bashi taimakon gaggawa an mishi allurar bacci so ana buk'atar ya huta."
sai ta kuma matso gaban Ummi da idanunta suka cika da hawaye,
ganin tazo gabanta Ummi tace.
"Dan Allah Dr ki gaya min halin da yake ciki? koda baya rayene kada ki boye min, tunda abinnnan ya farufa bangashi ba sai dai in haggoshi daga nesa, ke uwace kinsan abinda uwa kanji in makamancin wannan ya faru da d'anta please me ya sameshi?."
a hankali Dr Batulu ta zauna gefenta kana ta dafa kafad'arta tare da cewa.
"Abinda ma muke zaton zaiyi tsanani sai muka sameshi da sauk'i,
Saifuddeen bai mutuba yana raye kuma insha Allah da yamma ni da kaina zan shigar dake inda yake, kafin nan ya farka zaki ganshi ya ganki kuyi mgna dashi, yanzu dai da ku koma gida domin nan akwai masu kula dashi.
wadanda Dr Aliyu ya tanatar su zasu mishi komai,
sannan batun abinci ma karku damu akwai d'iyar Dr d'in duk abinda za'a bashi damar ci ita zata shirya mishi komai.
Yanzu kuje gida da yamma Ku dawo,zaku ganshi kuma Dr Aliyu zai gaya muku duk abinda ke damushi da matakin daya kamata ku dauka dama yadda zaku kula dashi."
sosai Ummi ta gamsu da bayananta kana taji sanyi a ranta, haka yasa tace.
"To ba matsala ngd matuk'a Dr in sha zanyita addu'a zamu koma biyar na yamma zamu juyo."
cikin fara samun nitsuwa Hayatuddeen yace,
"Dr zai gane mu ko? numfashi sa ya dai ta ko?."
kai ta gyad'a mishi tare da cewa.
"Sosai ma har magna fa yanayi mana da body language alamun yana gane duk abinda muke cewa."
a tare sukace Alhamdulillahi.
sannan Dr Batulu ta bawa Ummi number ta kan in sun dawo da yamma su nemata.
Su Abban Farida kuwa, da Dr Adnan da Ishaq bayasu shiga sun so Dr Aliyu yayi musu bayanin matsalar Saifuddeen, so amman sai ya basu hak'uri sabida ya gaji yana buk'atan hutu ya dai ce suje da yamma su dawo dukansu yana son ganinsu dan zai musu cikekken bayanin matsalar Saifuddeen d'in da basu shawara da da gaya musu dabarun kula dashi.
dole suka hak'ura kan saida yamman in sun dawo.
Kai tsaye gidan Ya Rabi'u suka wuce dan Ishaq ya k'i su Ahmad da Adnan suje su kama hotel.
A motar da Ya Rabi'u ya bari a hannun Hayatuddeen suka tafi,
amman Ahmad ya karb'i tukin a cewarshi Hayatuddeen d'an koyone bazai yarda ya jasuba,
Ummi na gaba kusa da Ahmad kana Ishaq da Adnan da Hauatudeen suna baya a haka suka tafi.
Aunty Mami kuwa tuni ta shirya musu abinci tasa an gyara BQ ensu.
*A garin Gombawa d'iban fari*
Yau tunda sanyin safiya Zaleeha ta shirya domin zata je kaltingo don zantawa da nakasassun wannan yankin.
Amman har zuwa ƙarfe taƙwas na safiyar ta gaza yin komai, ji takeyi tamkar tayi ta kurma ihu ta faɗi abinda folisawannan suka haneta faɗi tare dayi mata barazana da ranshi,
kukan da takeyi ya sanya ida nunta kumbura sukayi jazir ga wani fitinennen ciwon kai, ya zatayi a duniya ko wacw ƴa in tanada matsala uwarta take fara tinkara ,amman sam Mama itama bayan folisawan tabi.
tafin hannunta tasa ta share hawayenta a karo na barkatai, a hankali ta miƙe kana ta zari car key ɗinta, a falo ta samu Mama a hankali ta gaiseda da muryarta dake disashe, cikin haɗe fuska tace.
"Wato dai bazaki bar koke-koken nan ba ko, so kike sai an gane wani abu ya faru da ke ko?."
Kai ta jinjina cikin sanyi tace.
"Mama ai wani abu kam yama faru, sanadi nane fa akayi mishi komai, ban saniba yana raye ko ya mutu wani hali yake? tun randa abin ya faru da dare washegari naje asibitoci sunfi bakwai babushi ba dalilinshi, ni badan raina da sukayi min barazana da shiba, a a shida yake hannunsu nakeji kar su ƙara cutarmin dashi." ta ƙarishe maganar wasu zafafan hawaye na kwaranyo mata,
ita kuwa Mama kasake tayi tare da cewa.
"eyeh sannu uwarshi harda su wani kada su ƙara cutar miki dashi kamar kece uwarsa ko ƙanwarsa ko matarsa lallai Zaleeha kifa kiyayeni tam!."
tana faɗin haka tayi cikin kitchen, ita kuwa Zaleeha rumtse ido tayi hawayen dake ciki suka silalo kana ta fita ta nufi falon Baba Malam ,bayan sun gaisane ta ɗan gyara zama ciin disashewar murya tace.
"Baba Malam bari in fita zanje gidan Adda Maryam daga nan zanje asibiti dubo wani mara lfy, Baba Malam a sashi a addu'a Allah ya bashi lfy ya kareshi da sharrin masu sharri."
murmushi dottijon yayi tare da cewa,
"To Mamana in sha Allah zan sashi a addu'a Allah ya bashi lfy, kuma in kinje asibitin bashi kaɗai zaki duba ki ɗan zazzagaya ki tuba wasuma dan ki samu ladan dake cikin hakan." kai ta gyaɗa kana tamiƙe tare da sallamanshi ta
tafi.