← Book details Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 9 OF 116

Sashe 9

Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

koda magrib ta kawo kai sai yaga anata rurrufe shaguna hakan yasa ya fita,
bakin inda Salisu ya ajiyeshi,
yana tsaye a wurin ya hango tsallaken titin anata Al'wala haka yasa shima yayi Al'wala kana ya tsallaka yaje akayi sallah dashi.
yana dawowa Salisu na isawa,
babu b'ata lokaci ya hau suka fara tafiya,
sunzo dai-dai wani wurin masu tuwo-tuwo Salisu ya tsaya kana yacewa Saifuddeen.
"Zo muje muci abinci kafin mu tafi naga alamun kamar ba abinda kaci."
juyawa yayi kalli wurin da Salisu ya nuna mishi,
baki ya tab'e kana ya girgiza mishi kai tare da nuna alamar kamar yana kekyamin abincin wurin.
murmushi Salisu yayi dan tabbas yasan Saifuddeen mutunne mai tsananin tsabta da gayu kuma yanada kyakyani,
dan yasan iya tsawon yarintansu bai tab'a ganin ya sayi koda ko kosai ko wani abuba cikin abubuwan da ake kawowa a yar majalisar k'ofar gidansu ba.
So dan haka sai ya hau machine d'in yaja tafiya kad'an suka isa wurin mai shayi, kana yace.
"To mu shiga nan kasha koda shayine."
Still tab'e baki yayi tare da juya kai,
alamun bazai shaba.
ganin haka Sakisu ya kuma jan machine d'in, kai tsaye hanyar tashan Dukku ya nufa dashi,
suna zuwa dai-dai bakin gate d'in Abba bakery yayi parking kana ya sauk'a sannan,
yacewa Saifuddeen.
"Zo muje nan ko zaka iya cin gashin wannan."
a tare suka shiga inda daga mashigar wurin mai naman yake,
ganin wurin fes komai a killacene yasa,
Saifuddeen yarda ya zauna a wurin,
naman d'ari biyar Salisu ya saya musu, kana ya shiga cikin asalin Abba bekery ya sayo musu yogurt k'ananun robabin guda biyu.
nan sukaci duk da Saifuddeen bai wani ci mai yawaba yanka hud'u yaci bai kuma k'arawaba sai yogurt yasha.
Tuni kafin lokacin an kira isha'i haka yasa sukayi sallan
kafin suka nufi hanyar Dukku.

Suna isa gida Ummi tai ta murna ganin ya dawo lfy kuma gashi babu alamun wahala,
shi kuwa Saifuddeen yaki yace mata komai sabida gudun kada ta hanashi zuwa gobe.

Washe garima kamar jiya suka shirya suka tafi bayan Umminshi tayi ta mishi addu'ar samun nasara.

A inda Salisu ya ajiyeshi jiya yauma nan ya ajeshi,
bayan yaja ya tafine shi kuma ya nufi bakin mashigar kasuwar,
yauma kamar jiya saida yayi addu'a kafin ya shiga da k'afan dama.
Kai tsaye layin masu kayan yara ya shiga a hankali yake bin shagunan daki-daki yana kallon yadda suke gudanar da kasuwancin su, mata masu ciki nata shege da fice, a hankali yake taku cikin nitsuwa.
duk wanda ya ganshi sai ya k'ara juyawa ya kalleshi sabida bak'ak'en kayan da ya saka ba k'aramin haskashi sukayiba farinshi ya k'ara fitowa hancin nan har baki, uwa uba sumar kanshi tafi sawa ana kallonshi sabida duk wanda yaga sumar zai tunanin balarabe ne,
fatar k'afafunshi da tafin hannunshi kuwa sunyi jazir, in ya taka k'afar tamkar jini zai tsillo.
Dai dai bakin wani k'aton shago ya tsaya,
yana tsayuwa kenan yaji an.....!

By

*NAKASA BA KASAWA BACE*

*PAGE 4*

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

Free page

*Wannan page ɗin kuma nakunw ƴan Hukuncin Allah fans two, ina al'fahari daku,*

*Ga masu son saya turo katin Mtn na 300 ta nan 09097853276 ko ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa*

Yaji An d'an matso kusa dashi har jikin wanda ya matso kusa da shid'in na gogan nashi jikin hakan ya sashi juyowa a hankali ya d'an kalli matashin da bazai zarta sa'anshi ba,
ganin d'an saurayin yana murmushi ya sashi d'an murmusawa,
shi kuwa saurayin cikin fara'a ya mik'a mishi hannu ganin haka shima Saifuddeen ya bashi hannu, fuska cike da fara matashin ya fara mgna cikin bagwariyar larabcin, dan a zatonsa Saifuddeen balarabene,
sosai Saifuddeen ya zuba mishi ido tare da mmki dan ya gane zaton saurayin, haka yasashi k'ara tsurawa bakin matashin ido lokacin daya kuma ci gaba da mgna cikin larabcin shuwa'arab yace.
"Barka da zuwa, shigo daga ciki, me kake so?."
kai kawai Saifuddeen yake jujjuya mishi alamun a a ba abinda zai saya,
shi kuwa saurayin murmishi ya kumayi dan a zatonsa Saifuddeen baya gane irin nashi larabcin ne haka ya sashi juya harshe eh zuwa hausa yece.
"Kai wannan balarabe ba dai kyauba Masha Allah, ko me kakeso ne oho."
wani dake cikin shagon ne yace.
"Jabeer wai me yake sone, jiya mafa na ganshi a bakin shagon Alhaj ishaq."
murmushi wanda aka kira da Jabeer yayi kana yace.
"Ai bai gane larabcina."
cikin zuba mishi ido wancan din yace.
"To yaje gaba wala Allah a samu mai iya mishi irin yarenshi."
daga nan ya juya yaci gaba da sabgogin jera kayayyakin.
Shi kuwa Saifuddeen gane abinda suka cene ya sashi juyawa ya ci gaba da tafiya.
daga nan yayi ta bulayi har azahar koda yaga ana al'wala shima ya zaro goma ya sai pure water yayi al'wala kana ya nufi inda ya hango ana jam'i yana zuwa ana tada ik'a.
Bayan an idar da salla ya d'an jima a zaune yana addu'oi saida yaga an fara nannad'e taburman sai ya mik'e yaci gaba da yawatawa.
kanshi ya kule ya rasa ya zaiyi dan sam cikin kasuwar babu mai kula kowa kowa sabgar gabanshi keyi, kana duk bakin shagon da yaje ya tsaya sai ai ta mishi gwarancin larabci, duk da yana ganewa to amman dame zai basu amsa tunda shi kurmane,
haka yasa ake zaton bai gane larabcin ne tunda yawanci yan koyone ke gwada iyawarsu.
jin ya gaji da yawone yasashi shiga layin masu kayan kitchen nan ya samu inuwa dai dai bakin wani babban shago ya tsaya bencin dake gefe yaja ya zauna,
yana kallon yadda ma'aikatan keta cinikaiya da masu sayyya kasan cewar ramadan ya kusa baifi wata biyu ya rageba shiyasa kasuwan masu kayan kitchen ke gudu,
sabida mata kan sabunta ababen aiki dan samun yalwatuwarsu.
d'aya daga cikin yaran shagon ne ya kalleshi da kyau kana yace.
"Mai gida Allah yasa dai kana jin hausa?."
da sauri ya gyad'a mishi kai alamar. "Eh inaji."
shi kuwa murmushi yayi sannan yace.
"To me kakeso?." da sauri ya jujjuya mishi kai alamar.
"Ba abinda nakeso."
gane abinda yake nufi yasa yaron shagon yace.
"Hutawa kakeyi kenan?." still kai ya gyad'a mishi alamar eh.
ganin kamar baison mgnane yasa yaron ya shareshi yaci gaba da sabgoginshi.
Shiko Saifuddeen gyara zamanshi yayi tare jingina da jikin k'ofar shagon.
mata nata shiga da fita,
sai ya kuma tsargu ganin yadda aketa kallonshi,
har ya mik'e zai tafi sai ya kuma tsayawa ganin wani kekyawan Dottijo fari k'al dashi dake bisa keke bayan keken wani k'aton kwaline dake cike da lododi manya-manya irin k'atti sosai d'innan wanda in kayi sayayya mai yawa ake saka maka kayanka ciki,
sai kuma tsaka-tsakiya sai yan saffa-saffa sai k'anana kana sai masu layi-layin nan sai kuma k'ananu irin mai gida ya kasa d'inna.
hannu ya mik'a ganin wannan kekyawan dottijon yana mik'o mishi kullunan lododin yana ce mishi.
"Tai maka min mana yarona mik'a musu lododin,
ka amso min kud'in na jiya, ba sai na sauk'a bisa motar tawa ba".
ya k'arishe mgnar cikin fara'a,
shima murmushi yayi kana ya amshi ledodin ya juya cikin shagon inda yagga babban ogansu ya zaro kud'i ya irga gudan dubu guda uku kana da d'ari biyar,
yana mik'owa Saifuddeen d'in yana kuma kallon Dottijon tare da cewa.
"Barka da yamma baba Bello, kaga ko kamar kasan lododinmu sun k'are."
cikin sakin fuska dottijon yace.
"Kace nazo a dai-dai kenan?."
shiko mai shagon bayan ya karb'i lododin da Saifuddeen yake mik'o mishi sai ya kuma kalleshi kana ya kalli Dottijon tare da cewa.
"Kai Baba yau kam inaga a bamu na dubu biyar,
sabida kar muzo gobe bakazo da wuriba su gaza mana."
da sauri tsohon yace.
"To ba matsala."
bayan ya amshi kud'in da Saifuddeen yake mik'o mishi ne sai ya kuma bashi wasu banduran lododin,
da sauri ya amsa kana ya bawa mai shagon.
ganin alamun bakin mai shagon yana cewa.
"To Baba bello Allah bada kasuwa sai gobe kuma."
da sauri ya juya, ganin Dottijon na ce mishi.
"Ngd ko d'an saurayi."
kai ya gyad'a mishi tare da zura mushi ido ganin yaja keke nai ya tafi.

A hankali ya juya yaci gaba da tafiya bai jima da fara bulayinba yaga anata shirin Sallan la'asar daga nan shima yayi harama.
Bayan an idarne ya koma layin masu robobi nan yayi ta yawatawa,
hardai aka kira magrib ganin anata rurrufe shaguna ya sashi fitowa, inda yayi sallan magrib jiya anan yauma yayi salla yana dawowa kuma ya samu Salisu ya iso.

Daga nan bakin kasuwan bakin General hospital sukana nufa,
inda daga bakin titin ta d'aya gefen akwai wata mai saida abinci sanin tanada tsabta ne yasa Salisu kawosu nan,
amman Saifuddeen k'in ci yayi,
sai dai Salisu yaci kana ya nuna mishi wani shagon fura da nono,
gane yana sone yasa Salisu shiga ya seyo mishi k'aramar roba saida yasha sukayi sallan isha kafin suka d'auki hanyar dukku.
Chapter 9 · 0% Book details