← Book details Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 108 OF 116

Sashe 108

Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Habu ne ya watsa mata wani zazzafan harara tare da cewa.
"To ki mutu mana! In kin mutun sai me? Ko kina zaton mutuwarki zaisa muma mu mutu ne?."
Faɗawa  jikin Aunty Lubna dake raɓe agefe  tana zubda hawaye tayi, cikin kuka da raunin murya tace.
"Wayyo Allah na Aunty Lubna ki taimaka min ki faɗa musu inada wanda nake so, kice musu wlh bana son musakin can."
Cikin rauni Ahmad ya kalleta murya  a tausashe yace.
"To meyasa kika ce mishi kin amince dashi ya turo iyayenshi tunda kin san bakya sonshi?."
cikin kiɗima da gigita tace.
"Wallahi ban faɗaba wlh ƙarya yake min, to shida kurmane ta inama zaiji abinda zance mishi?."
cikin hatsala Habu yace.
"Ba text messages kika tura mishi ba, da wayarki."
Miƙewa tayi a hargitse ta kalli Mahaifinsu da ya zuba musu ido, yana murmushin ganin ƙuruciyar yaran nashi, ba abinda ke sashi murmushi kamar yadda Ahmad yake taya Zaleeha kuka kamar yaro,
yana jin daɗin zafin Habu dan yasan Habu Baban ya Aminu ya gado yayan Baba malam kenan,
cikin kuka Zaleeha tace.
"Wallahi ƙarya yake min ni bani da number shi ma."
Mama ce tayi kaffa tare da jan dogon tsuka.
Habu kuwa falon Mama ya koma,
jim kaɗan sai gashi da wayar Zaleeha riƙe a hannunshi,
cikin takaici ya cire wayar a key dan yasan komai na wayar,  hakan kuma tsarinshine dan bincikar woyoyin ƙannenshi yasa su duk yasan komai na wayarsu.
kai tsaye inbox nata ya shiga ai kuwa text biyar ya duba, ana shida sai ga text ɗin gama number shi da Saifuddeen yayi seven da My happiness.
Cikin zafin rai ya nuna mata wayar tare da cewa.
"Meye wannan?".
Ido ta zaro gaba ɗaya, ganin abinda ke rubuce da kuma haƙiƙa ita ta rubuta, kuma ta turawa number da aka sawa suna da my happiness, sai kawai ta miƙe ta koma can gefe nesa da mahaifin nasu ta fara buga tsalle tare da yarfa hannu tare da kurma ihu kana tana cewa.
"Sharri! Sharri!! Sharri!!! Sharrine yayi min wallahi ƙarya ne ni bana sonshi!!!."

Ganin yanda takeyifa yasa Baba malam yin wani murmushi mai kama da dariya.
Saura kuma gaba ɗaya ido suka zuba mata.
Habu kuwa belt ɗin ƙugunshi ya zaro tare da yin kanta.
ai fa tana ganin haka ta juya a guje tayi cikin gidan, shi kuma ya mara mata baya a guje,
radadada kake jinsu a guje.
ganin yadda Habu ya bita yasa Ahmad binsu da gudu hakama Aunty Lubna da Zahira.

Zaleeha kuwa gudu take da iya ƙarfinta dan tasan Habu ba mutunci ne dashi ba. In ya kama duka kamar mara imani.
Kai tsaye ɗakinta ta shiga cikin sa'a ta samu ta maida ƙofar garam ta rufe,
tun kafin ya iso,
ganin haka yayi kwaffa ya juya tare da cewa.
"Yar iska kawai da ki tsaya mana."
Ita kuwa a cikin ɗakin wani irin fitininan nen kuka tasa da iya ƙarfinta, tana kuka da surutai cewa.
Ita dai bata sonshi ta tsaneshi zata mutu in an aura mata shi.
Ahmad kuwa da Lubna rarrashinta sukayi tayi da bata baki amman ina.
ranar haka ta kwana a rufe tana kuka da al'washin ciwa Saifuddeen zarafi.

Mama kuwa sosai taji daɗin abinda Zaleeha tayi,
ta kuma yi niyar yaƙi da wannan auren.

Ƙarfe takwas dai-dai na safiyar ranar asabar Zaleeha fito cikin d'akinta inanun ta a kumbure tayi ja alamu tayi kukan  mai yawa.
gefen Mamanta ta zauna cikin sanyi tace.
"Ina kwana Mama".
"Lfy."
ta bata amsa a tak'aice.
kai ta d'an sunkuyar ida nunta cike da hawaye tace.
"Mama wlh k'arya yake min sharri ne, ni bance ina sonshi ba." kai Mama ta gyad'a mata cikin alamun gamsuwa tace.
"To yanzu ya zakiyi?."
cikin k'arifin hali tace.
"Zan yi mgnin abun in sha Allah shida kanshi zai dawo yace ya fasa."
Cikin jin dad'in Mama tace.
"Ke dai ki kafa ki tsare cewa bakya sonshi ni kuwa zan san abinda zanyi a kai."
To tace kana ta kira Zahira tare da cewa.
"Je parlour Baba Malam ki d'auko min wayata".
Juyawa tayi ta nufi bedroom d'in Mama tare da cewa.
"Gashi nan na d'aukoshi tun jiyan ai."
Amsar wayar tayi kana ta koma d'aakinta.
Ita kuwa Mama murmushin jin k'arfin guiwa tayi tare da cewa.
"Bazaki auri gurgu ba kam ko kina sonshi zan hana kuma wlh bazan bari kiyababanki boyayya kan arennamba dole zanyiwa boka bayanin yadda nake son yasa ki bijirewa wannaɓin da BAban naki ya miki, don ko sama zata had'e da k'asa zaki auri Abdussalam dan shine dai-dai dake."
Tana kaiwa nan ta kira wayar Abdussalam yana d'agawa suka gaisa kana tace mishi,
ya had'o komi da komai na aure ya turo iyayenshi Zaleeha ta yarda dashi.

Jin haka yasa Abdussalam jin k'arfin guiwa nanfa yaci gaba da shirya lefenshi dai-dai da matsayinshi.

Ita kuwa Zaleeha konciya tayi kan gadonta sannan ta fara rubuta text kamar haka.

```Kai baka cancanci inyi makasa sallama ba, domin ita sallama ta masu amincine ba mak'aryata azzalumai irinka ba. nace maka bana sonka na tsaneka bazan soka ba har abadan,
dan haka kayi maza ka turo wad'anda ka aiko suka kawo wannan tarkacen suyi maza su zo su kwashe gaiyar dukiyarka```
murmushi tayi lokacin da ta tura text d'in a ganinta ta k'unsa mishi bak'ak'en maganganu.

Saifuddeen kuwa yana zaune bisa kujerar wheelchair d'inshi Amman a dinning table,
Ummi na had'a mishi tea yayinda yake cin soyayyan doya da kwai,
jin wayarshi dake cikin al'jihunshi ta bashi wani alamun sak'o ya shigo kamar bazai duba ba,
sai ya kuma zaro wayar ganin number tane ya sashi yin murmushin mugunta dan yasan,
Kwanan zancen.
ganin yanata murmushi Ummi yin murmushi dan farin cikinsa shine nata.
Raliya kuwa da Hayatuddeen suma murmushin suke tayasu.

Bai bud'e text d'inba saida ya koma side d'inshi sannan ya bud'e ganin abinda ta rubuta ne yasashi yin maganar zuci.
"Hmmmm wasa farin girki, yarinya kinga ta kanki." a zahiri kuwa yi yayi kamar baiga text d'inta ba bare ya bata amsa.

Ita kuwa ganin shiru-shuru bai maida mata martini bane yasa da azahar ta sake tura mishi wani text d'in wanda yafi na safe zafi.

Shiru ba amsa har dare, ganin haka ta kuma tura mishi wani text d'in.

Har kusan k'arfe d'ayan dare tana jiran amsa amman cib ba amsa.

Washe gari haka da asuban fari ta kuma tura mishi wani zazzafan text ,
Still ba amsa.

Abu fa ya isha Zaleeha yau kusan kwana uku kenan ba amsa,
kuma bata fasa tura mishi bak'ak'en maganganu ba.

A gidan kuwa babu wanda ya sake mgnar auren Baba malam kuwa duk nacin Mama bata jin ta bakinsa.

Habu kuwa shida Zaleeha hararace a tsakaninsu.

Zahira kuwa munafuka yar koren Mama ce.

Aunty Lubna kuwa ita ke hillace Zaleeha,
har take mantar da ita batun wani aure.

Ita kam Zaleeha ta fara sakewa dan ganin baya maida mata amsa sai take zaton yayi mubaya'a ne,
koda wasa bata shiga d'akin Mama dan bata son ganin jerin akwatunan.

Ya Ahmad yanata shirin gobe zai tafi.

Suna cikin hira ya kalli Zaleeha da ta d'an sake a hankali yace.
"Ke Zaleeha kayan d'aki dana kitchen na wanne k'asane kikafi so kikega sunada ink'anci.
cikin rashin fahimtar mgnar tashi tace.
Gada je dai da kujeru Dubai komansu nada ink'anci da tsari.
Kayan kitchen kuwa na Chaina sunfi kyau." murmushi yayi tare da salonta yadda gaba d'aya hankalin ta na kan wak'ar da takeji a wayar Lubna, har tana cewa.
"Yauwa Aunty Lubna tura min wannan wak'ar mana ina sonta tamin dad'i."
To Lubna tace tare da yiwa mijinta signal alamun sam fa Zaleeha bata gane komai ba.

Mama kuwa a sashinta ta kira yayarta Ruda ta shaida mata abinda ke faruwa,
Jin haka yasa Ruda cewa cikin satin nan zata shigo gombe.

Maryam kuwa duk abinda akeyi bata saniba.
shiyasa har ta kira Anty Aisha k'anwar mama ta shaida mata an kawo lefen Zaleeha biki kuma 27 next month.
Itama tace zata zo ganin lefe.

Saifuddeen kuwa Ishaq kadai ya gayawa abinda Zaleeha ke rubuto mishi nan Ishaq yace mishi ya barta sai tazo har inda suke,
dan yasan zata zo.

Ya  Ahmad ya tafi harkan aikinsa, tunima ya bar k'asar.
in da ya bud'a bakin aljihunshi yake kashewa Zaleeha mahaukatan kud'ad'e na ban mmki wurin saya mata dukkan abin buk'atan amare.

Tafiya dai ta mik'a a lissafin yau saura mako d'aya ne auren.
tuni shirye-shirye sun kankama ta gefen ango da amarya.
Chapter 108 · 0% Book details