Sashe 29
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Koda yaje ya ciko botikinshi da kayan sanyin kai tsaye ya nufi shagon Alhaji Kabiru.
Yana zuwa sai ya samu suna can cikin shagon bisa dukkan alamu bak'i yayi kuma manyane masu cikar haiba.
Amir ne d'aya daga cikin yan gidan shagon Alhaji Kabirunne ya kalli Saifuddeen tare da cewa.
"Yauwa Balarabe tsallaka ka shiga can ciki yana tare da manyan bak'i ne su zaka kaiwa ruwan sanyin.
jin haka sai ya tsallaka ya shiga,
kai tsaye gefen da suke ya nufa,
yana isa Alhaji Kabirun yayi murmushi tare da cewa.
"Yauwa Saifuddeen balarabe, bamu ruwan sanyi Faro roba hud'u da molt roba hud'u sai ka mik'o min fanta d'aya kasan ni nafi son fanta."
cikin girmamawa fuska k'unshe da murmushi ya matso ya mik'a mishi fantan kana ya rusuna gabansu ya fara zaro gorunan Faro dana molt.
Yayinda tuni idanunshi yana kan d'aya daga cikin bak'in inda yake cewa.
"Gsky Alhaji Kabiru in dai kanada daman saran wannan kaya to wlh ka zuba jarinka domin kamfaninne ya kawo mana talla har gida,
sun bamu tabbacin tabbas akwai riba mai tarin yawa,
to ni kuma naga bazan iya yin harkallan ni d'aya ba."
ci gaba yayi da kallon bakin mutun tare da mik'a mishi roban Faro,
still yana kallon bakin mutum inda yake cewa.
"Koda bashi ne kaci muyi sarin nan in sha Allah zamuji dad'in hark'allan."
sai kuma ya juyo ya kalli d'aya daga ciki wanda ke cewa.
"Ni kaina last week nayi sari yanzu hakama bani da kud'i kuma wlh bashi zanci dan nasan in sha Allah zamu samu riba."
d'aya daga cikin sune yace.
"Kai bani ruwan nan zansha ka tsaya kana kallon bakin mutane."
Alhaji Kabirun ne yayi d'an murmushi tare da cewa.
"Alhaji Sani ai wannan yaron irin Isma'il nane kurmane baya ji."
jin haka yasa wanda aka kira da Alhaji Sani ya d'an tab'a Saifuddeen tare da mishi alamun ya bashi ruwan, juyowar da zaiyi ne yayi dai-dai da lokacin da Alhaji Sani yayi wata mgnar da ta sa Saifuddeen t...!
By
*GARKUWAR FULANI*
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 9*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
_Ga masu buƙatar sayan littafin Nakasa ba kasawa bace, turo katin mtn na 300 kacal ta wannan number 09097853276. Ko kuma ka/kiyi min transfer ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ka/ki turo screenshort na shaidar ka/kin biya_
~Wannan shafi nakune mutanen Group ɗin Nakasa ba kasawa bace fans two ina al'fahari daku~
Free page
Tsurawa fuskokinsu ido cikin hikima yake nazartan zantukan da sukeyi,
wanda ya rasa madosar zancen,
mik'ewa yayi a hankali ya fara nad'e gammon da yake sawa a kanshi kafin ya aza kwalin omon,
yana mai ci gaba da nazartan kalaman wanda aka kira da Alhaji Sani yana cewa.
"Nan da wata biyu zasu rufe sararwan,
dan haka muyi k'ok'ari mu samu mu sari koda kad'an-kad'an ne,
Company ya talla ta mana ne dan sanin mune manyan costumes d'insu na nan jihar Gombe,
sun kuma bani tabbacin tabbas nanda wata hud'u Maggi zaiyi tsada sosai kusan ninka kud'inshi zaiyi,
domin ya bani misalai da dama,
sun kuma ce wannan damace da aka bawa kuduncin Nigeria, to shiyasa suma musulmanmu suka nemi da a bawa arewacin Nigeria samun wannan garab'asar dan sanin arzik'in musulmi yanada fa'idoji da dama."
d'aya daga cikin sunne ya kuma cewa.
"Ni kam in sha Allah zan k'ok'arta in samu koda kad'an ne."
gyara zama Alhaji Kabiru yayi tare da zaro kud'i yana mik'awa Saifuddeen yayinda hankalinshi ke kan abo kan nashi,
cikin nitsuwarsa yace.
"To zanyi k'ok'ari inga ko zan samu wasu 'yan kud'ad'e na da nike bin bashi sai in sa hannu a ciki."
cikin farin ciki sukace.
"Alhamdulillahi to Allah yasa ka samesu."
Amin Amin yace tare da kallon Saifuddeen da ya juya ya fita zuciyarshi cike da sak'e-sak'e haka kawai yake son yaji tushen zancen.
Su kuwa bayan sun gama tattauna yadda abin zai wakana.
Nan suka sallami Alhaji Kabiru suka tafi.
Saifuddeen kuwa yana fita yaci gaba da zageyenshi na tallan omo da kayan sanyin nashi,
bai fito kasuwarba har k'arfe shida na yamma dan tunda azumi ya wuce suka dawo kamar da sai bayan sallan isha suke komawa.
Yana fitowa yayi al'wala yayi sallan magrib yana fitowa ya samu Salisu na jiranshi,
daga nan bakin Al'kasim suka tsaya nan suka d'anci abinda ya sauwak'a sannan suka wuce Dukku.
Bayan kwana uku da zuwan su Alhaji Sani wurin Alhaji kabiru suka kuma zuwa,
kan su jaddada da mishi batun kadafa ya d'auki abun a shirme ya dai ce musu yana nan yana tabin wad'anda yake bin kud'in.
Iya bukku kuwa ,tun randa suka koma ko mai sunan Saifuddeen taji an kira sai gabanta ya faɗi.
A cewarta ba ita ba dukku har gaban abadan, dannan wannan kurman matashin daya zubda mata haƙora biyu a karonsu na forko. Tofa tabbas in antayi artabu dashi a karo na biyu kanta zai sare ya bata a tafin hannunta, Goggo Ummi kuwa da Bappan ta sunji daɗin hakan a ransu, kuma sunada niyar sake ziyartarsu.
Yau tunda Saifuddeen ya gama raba ledanshi kana ya yawata da tallanshi har la'asar bayan anyi salla ne ya nufi gidansu Ishaq dan sunyi dashi zaije su Ahmad da Saminu da Mudassir ma duk sunyi dasu zasuje dan sun kwana biyu basu had'uba,
Hud'u dai-dai duk suna had'e a d'akin Ishaq yayinda gari yayi duhu sabida tasowan hadari,
Mama kuwa tuni tai ta musu hidima dan dama sun ce mata danbun zogale sukeso,
nan suka zube suna hira sunaci,
Ahmad ne ya kalli Saifuddeen da yayi shiru alamun nazari had'iye abincin bakinshi yayi sannan ya kalli Saifuddeen tare da cewa.
"Saifuddeen kaci dambun mana."
Kai ya jujjuya mishi alamun bazai cima,
cikin kula yace mishi.
"Meyasa bazaka ciba?."
Mudassir ne ya d'auki ledan pure water ya b'ula kana yashanye fiye da rabi sannan ya kalli Ahmad tare da cewa.
"Ka manna Saifuddeen da zab'en abinci ai baicin dambu."
jin haka yasa Ishaq mik'ewa tare da cewa.
"Yes haka nefa kaga ni nama mance bari inje in gayawa Mama tayi mishi d'anwake dan na lura yana son abincin mata."
dariya sukayi baki d'aya sannan ya fita,
Saminu kuwa gyatsa ya d'anyi tare da cewa.
"Au ashe dama d'an wake cimar matane?."
kai Saifuddeen ya jujjuya mishi alamun a a kam.
fitan Ishaq ba jimawa sai gashi ya dawo nan sukaci gaba da hira.
Bayan kamar awa d'aya da rabi sai ga Imran ya shigo da tire,
kai tsaye gaban Saifuddeen ya ajiye,
sannan ya juya ya fita,
shi kuwa Saifuddeen tiren ya jawo wanda aka cika d'an madaidaicin pilet da d"anwake sai dafaffan kwai guda uku a sama sai mai da magi da yaji,
nan ya fara ci sosai yaji dad'in d'anwaken,
Mudassir ne ya kalleshi tare da cewa.
"Oga ba tayine?."
hararanshi ya d'anyi tare da nuna mishi kulan dambun cikin mishi alamun kunci nabanku.
Ahmad kuma tab'e baki yayi tare da cewa.
"Ahab barshi da d'anwake ko rabi nai bazai ciba zaice ya k'oshi, sai dai ka ganshi yana ture pilet d'in."
ana cikin haka Allah ya sako iska mai sanyi wanda yake nuni da hadarin ya watse lokaci d'aya gari ya washe.
Shi kuwa Saifuddeen baici rabinba ya ture pilet d'in kana ya mik'e ya shiga bathroom,
nan sukayi ta mishi tsiya wai yana nan kamar kifi,
wonka yayi yana fitowa ya bud'e durowan Ishaq ya canza kaya sannan ya kallesu tare da musu alamun shi zai tafi,
sai ya kuma kamo hannun ishaq tare da mishi alamun ya tafi,
nan suka mik'e duk suka fita daga nan duk suka salami juna.
K'arfe 11:15 pm Saifuddeen ya mik'e tsaye tare da ninke sallayan da yayi sallan shafa'i da wutiri, a kanshi
bakin katifarshi ya zauna tare da yin addu'a ya shafa a jikinshi sannan ya kwanta ta b'arin dama.
Can misalin k'arfe biyu dai-dai ya farka bakinshi d'auke da addu'a,
a hankali ya bud'e idanunshi yana mai tuno mafarkin da yayi,
salati ya kumayi ya sanarwa mahaliccinshi,
jingina yayi da jikin pillow sai ya kuma lumshe idanunshi tare da son nazartan mafarkin nashi,
sai ya kumayi saurin bud'e idanun nashi dan ganin abin ya dawo mishi tamkar yana ganinshi a majigi,
a hankali ya mik'e ya fito tsakar gidan nasu inda ya samu ashe anyi musu ruwan sama kamar da bakin gwarya,
cikin nitsuwa ya wuce bandaki fitsarin da ya matseshi yayi sannan ya fito bakin barandan k'ofan d'akinshi ya tsuguna yayi al'wala sannan ya mik'e ya shiga d'akin kana yayi ta nafilfilinshi.
Yana zuwa sai ya samu suna can cikin shagon bisa dukkan alamu bak'i yayi kuma manyane masu cikar haiba.
Amir ne d'aya daga cikin yan gidan shagon Alhaji Kabirunne ya kalli Saifuddeen tare da cewa.
"Yauwa Balarabe tsallaka ka shiga can ciki yana tare da manyan bak'i ne su zaka kaiwa ruwan sanyin.
jin haka sai ya tsallaka ya shiga,
kai tsaye gefen da suke ya nufa,
yana isa Alhaji Kabirun yayi murmushi tare da cewa.
"Yauwa Saifuddeen balarabe, bamu ruwan sanyi Faro roba hud'u da molt roba hud'u sai ka mik'o min fanta d'aya kasan ni nafi son fanta."
cikin girmamawa fuska k'unshe da murmushi ya matso ya mik'a mishi fantan kana ya rusuna gabansu ya fara zaro gorunan Faro dana molt.
Yayinda tuni idanunshi yana kan d'aya daga cikin bak'in inda yake cewa.
"Gsky Alhaji Kabiru in dai kanada daman saran wannan kaya to wlh ka zuba jarinka domin kamfaninne ya kawo mana talla har gida,
sun bamu tabbacin tabbas akwai riba mai tarin yawa,
to ni kuma naga bazan iya yin harkallan ni d'aya ba."
ci gaba yayi da kallon bakin mutun tare da mik'a mishi roban Faro,
still yana kallon bakin mutum inda yake cewa.
"Koda bashi ne kaci muyi sarin nan in sha Allah zamuji dad'in hark'allan."
sai kuma ya juyo ya kalli d'aya daga ciki wanda ke cewa.
"Ni kaina last week nayi sari yanzu hakama bani da kud'i kuma wlh bashi zanci dan nasan in sha Allah zamu samu riba."
d'aya daga cikin sune yace.
"Kai bani ruwan nan zansha ka tsaya kana kallon bakin mutane."
Alhaji Kabirun ne yayi d'an murmushi tare da cewa.
"Alhaji Sani ai wannan yaron irin Isma'il nane kurmane baya ji."
jin haka yasa wanda aka kira da Alhaji Sani ya d'an tab'a Saifuddeen tare da mishi alamun ya bashi ruwan, juyowar da zaiyi ne yayi dai-dai da lokacin da Alhaji Sani yayi wata mgnar da ta sa Saifuddeen t...!
By
*GARKUWAR FULANI*
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 9*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
_Ga masu buƙatar sayan littafin Nakasa ba kasawa bace, turo katin mtn na 300 kacal ta wannan number 09097853276. Ko kuma ka/kiyi min transfer ta asusuna 0005388578 jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ka/ki turo screenshort na shaidar ka/kin biya_
~Wannan shafi nakune mutanen Group ɗin Nakasa ba kasawa bace fans two ina al'fahari daku~
Free page
Tsurawa fuskokinsu ido cikin hikima yake nazartan zantukan da sukeyi,
wanda ya rasa madosar zancen,
mik'ewa yayi a hankali ya fara nad'e gammon da yake sawa a kanshi kafin ya aza kwalin omon,
yana mai ci gaba da nazartan kalaman wanda aka kira da Alhaji Sani yana cewa.
"Nan da wata biyu zasu rufe sararwan,
dan haka muyi k'ok'ari mu samu mu sari koda kad'an-kad'an ne,
Company ya talla ta mana ne dan sanin mune manyan costumes d'insu na nan jihar Gombe,
sun kuma bani tabbacin tabbas nanda wata hud'u Maggi zaiyi tsada sosai kusan ninka kud'inshi zaiyi,
domin ya bani misalai da dama,
sun kuma ce wannan damace da aka bawa kuduncin Nigeria, to shiyasa suma musulmanmu suka nemi da a bawa arewacin Nigeria samun wannan garab'asar dan sanin arzik'in musulmi yanada fa'idoji da dama."
d'aya daga cikin sunne ya kuma cewa.
"Ni kam in sha Allah zan k'ok'arta in samu koda kad'an ne."
gyara zama Alhaji Kabiru yayi tare da zaro kud'i yana mik'awa Saifuddeen yayinda hankalinshi ke kan abo kan nashi,
cikin nitsuwarsa yace.
"To zanyi k'ok'ari inga ko zan samu wasu 'yan kud'ad'e na da nike bin bashi sai in sa hannu a ciki."
cikin farin ciki sukace.
"Alhamdulillahi to Allah yasa ka samesu."
Amin Amin yace tare da kallon Saifuddeen da ya juya ya fita zuciyarshi cike da sak'e-sak'e haka kawai yake son yaji tushen zancen.
Su kuwa bayan sun gama tattauna yadda abin zai wakana.
Nan suka sallami Alhaji Kabiru suka tafi.
Saifuddeen kuwa yana fita yaci gaba da zageyenshi na tallan omo da kayan sanyin nashi,
bai fito kasuwarba har k'arfe shida na yamma dan tunda azumi ya wuce suka dawo kamar da sai bayan sallan isha suke komawa.
Yana fitowa yayi al'wala yayi sallan magrib yana fitowa ya samu Salisu na jiranshi,
daga nan bakin Al'kasim suka tsaya nan suka d'anci abinda ya sauwak'a sannan suka wuce Dukku.
Bayan kwana uku da zuwan su Alhaji Sani wurin Alhaji kabiru suka kuma zuwa,
kan su jaddada da mishi batun kadafa ya d'auki abun a shirme ya dai ce musu yana nan yana tabin wad'anda yake bin kud'in.
Iya bukku kuwa ,tun randa suka koma ko mai sunan Saifuddeen taji an kira sai gabanta ya faɗi.
A cewarta ba ita ba dukku har gaban abadan, dannan wannan kurman matashin daya zubda mata haƙora biyu a karonsu na forko. Tofa tabbas in antayi artabu dashi a karo na biyu kanta zai sare ya bata a tafin hannunta, Goggo Ummi kuwa da Bappan ta sunji daɗin hakan a ransu, kuma sunada niyar sake ziyartarsu.
Yau tunda Saifuddeen ya gama raba ledanshi kana ya yawata da tallanshi har la'asar bayan anyi salla ne ya nufi gidansu Ishaq dan sunyi dashi zaije su Ahmad da Saminu da Mudassir ma duk sunyi dasu zasuje dan sun kwana biyu basu had'uba,
Hud'u dai-dai duk suna had'e a d'akin Ishaq yayinda gari yayi duhu sabida tasowan hadari,
Mama kuwa tuni tai ta musu hidima dan dama sun ce mata danbun zogale sukeso,
nan suka zube suna hira sunaci,
Ahmad ne ya kalli Saifuddeen da yayi shiru alamun nazari had'iye abincin bakinshi yayi sannan ya kalli Saifuddeen tare da cewa.
"Saifuddeen kaci dambun mana."
Kai ya jujjuya mishi alamun bazai cima,
cikin kula yace mishi.
"Meyasa bazaka ciba?."
Mudassir ne ya d'auki ledan pure water ya b'ula kana yashanye fiye da rabi sannan ya kalli Ahmad tare da cewa.
"Ka manna Saifuddeen da zab'en abinci ai baicin dambu."
jin haka yasa Ishaq mik'ewa tare da cewa.
"Yes haka nefa kaga ni nama mance bari inje in gayawa Mama tayi mishi d'anwake dan na lura yana son abincin mata."
dariya sukayi baki d'aya sannan ya fita,
Saminu kuwa gyatsa ya d'anyi tare da cewa.
"Au ashe dama d'an wake cimar matane?."
kai Saifuddeen ya jujjuya mishi alamun a a kam.
fitan Ishaq ba jimawa sai gashi ya dawo nan sukaci gaba da hira.
Bayan kamar awa d'aya da rabi sai ga Imran ya shigo da tire,
kai tsaye gaban Saifuddeen ya ajiye,
sannan ya juya ya fita,
shi kuwa Saifuddeen tiren ya jawo wanda aka cika d'an madaidaicin pilet da d"anwake sai dafaffan kwai guda uku a sama sai mai da magi da yaji,
nan ya fara ci sosai yaji dad'in d'anwaken,
Mudassir ne ya kalleshi tare da cewa.
"Oga ba tayine?."
hararanshi ya d'anyi tare da nuna mishi kulan dambun cikin mishi alamun kunci nabanku.
Ahmad kuma tab'e baki yayi tare da cewa.
"Ahab barshi da d'anwake ko rabi nai bazai ciba zaice ya k'oshi, sai dai ka ganshi yana ture pilet d'in."
ana cikin haka Allah ya sako iska mai sanyi wanda yake nuni da hadarin ya watse lokaci d'aya gari ya washe.
Shi kuwa Saifuddeen baici rabinba ya ture pilet d'in kana ya mik'e ya shiga bathroom,
nan sukayi ta mishi tsiya wai yana nan kamar kifi,
wonka yayi yana fitowa ya bud'e durowan Ishaq ya canza kaya sannan ya kallesu tare da musu alamun shi zai tafi,
sai ya kuma kamo hannun ishaq tare da mishi alamun ya tafi,
nan suka mik'e duk suka fita daga nan duk suka salami juna.
K'arfe 11:15 pm Saifuddeen ya mik'e tsaye tare da ninke sallayan da yayi sallan shafa'i da wutiri, a kanshi
bakin katifarshi ya zauna tare da yin addu'a ya shafa a jikinshi sannan ya kwanta ta b'arin dama.
Can misalin k'arfe biyu dai-dai ya farka bakinshi d'auke da addu'a,
a hankali ya bud'e idanunshi yana mai tuno mafarkin da yayi,
salati ya kumayi ya sanarwa mahaliccinshi,
jingina yayi da jikin pillow sai ya kuma lumshe idanunshi tare da son nazartan mafarkin nashi,
sai ya kumayi saurin bud'e idanun nashi dan ganin abin ya dawo mishi tamkar yana ganinshi a majigi,
a hankali ya mik'e ya fito tsakar gidan nasu inda ya samu ashe anyi musu ruwan sama kamar da bakin gwarya,
cikin nitsuwa ya wuce bandaki fitsarin da ya matseshi yayi sannan ya fito bakin barandan k'ofan d'akinshi ya tsuguna yayi al'wala sannan ya mik'e ya shiga d'akin kana yayi ta nafilfilinshi.