Sashe 30
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Washe garin da rana irin rana tayi fed'e-fed'e d'innan lokacin gari ya d'anyi zafi sai inuwan gajimare kad'an-kad'an,
sosai ya saida kayan sanyin koda ya gama kafa na uku, sai ya wuce shagon su Jabeer nan sukayi ta hira har aka kira salla bayan sunyi salla kuma sai ya wuce shagon Alhaji Kabiru yana isa ya samu yaran shagon duk sunata hidiman jera kayayyakinsu bisa dukkan alamu sarin da sukayi ne ya iso,
shi kuwa Alhaji Kabiru yana cikin shagon bisa alamu lissafi yakeyi,
ganin haka sai Saifuddeen ya tsallaka ya shiga ciki can kusa da shi ya zauna cikin body language ya gaida Alhaji Kabiru da tuni ya gama lissafin ya had'a takardun wuri d'aya,
cikin mutuntaka da dattaku ya amsa gaisuwar Saifuddeen,
sai ya kuma kalleshi ganin yana mishi alamun tambyar ina woyarshi,
murmushi yayi tare da cewa.
"Wayata gata a aljihuna."
kai ya jinjina mishi kana ya mishi alamun ya fitar da ita zasuyi mgna,
gane hakan ya sashi zaro woyar,
daga nan ya suka fara mgna ta inbox nasu suna musanyan text messages,
sosai Alhaji Kabiru ya nitsu yana kallon text d'in da Saifuddeen ya tura mishi inda yake cewa.
"Assalamu alaikum, Alhaji ya gida ya kasuwa,
Allah ya taimaka."
sai ya rubuta mishi amsa da.
"Wa alaikassalam lfy lau Saifuddeen, Amin Amin. Naga kamar muhimmiyar mgna kakeson muyi, kada ka damu ka d'aukeni kamar mahaifinka ni ina ina jinka tamkar Isma'il d'ina."
Sosai Saifuddeen yaji dad'i mgnar hakan ya sashi murmusawa tare da rubuta mishi.
"Ngd matuk'a Alhaji." sai ya kuma yi shiru bai kuma rubuta komaiba ya rasa ta ina zai faro zancen gane haka yasa Alhaji Kabiru dafa kafad'unshi cikin bashi k'arfin guiwa yace.
"Ina jinka."
shi kuwa rusunar da kai yayi tare da rubuta mishi.
"Kayi hak'uri Alhaji ka gafarceni ranan asabar d'in da ya gabata, ka kirani na kawo maka ruwan sanyi, inda nazo na sameka da bak'i to nayi laifin fahimtar maganganunku, sai dai kuma naji ina sha'awar sanin kasuwancin da suke tallata maka,
in akwai damar da nima zan iya sa hannuna a ciki nima zanyi."
yana tura text d'in sai ya sunkuyar da kanshi,
shi kuwa Alhaji Kabiru murmushi yayi bayan ya gama karantawa cikin kekyawan fahimta ya dafa kafad'un Saifuddeen wanda ya sashi d'ago kai ya zuba mishi ido alamun jin na bakinshi.
Gyara zama yayi tare da zuba mishi idanu cikin sanyin sauti alamun yana son su sirranta zancen yace.
"Me zai hana zaka iya mana, ai duk abinda mai ji zai iya na kasuwanci in sha Allah zaka iya,
sai dai kuma fa wannan al'amarin da kamar wuya."
da sauri Saifuddeen ya gyara zama tare da fuskantarshi yana mai kallon motsin bakinshi ta yadda zai fahimceshi da kyau shi kuwa Alhaji Kabiru cikin tsarkakan zuciya ya fara mishi bayanin kasuwancin.
"Company Maggi ne suka kawo mana tallan Maggi a sirrance a matsayinmu na manyan dilolin maggi,
sun tallatama mana ne dan suna mana sha'awar ci gaba,
sun bamu sirrin company cewa nanda wata biyar magi zaiyi tsadan da bai tab'a yiba,
sun k'ara da ce mana mu fito da kud'ad'enmu mu sari maggin mu ajiye sun sanar damu cikin wata biyar zuwa bakwai company zai k'ara tsadan magi sun bamu tabbacin in sha Allah babu batun fad'uwa sai dai cin riba,
in dai bamuci riba ba toko bazamuyi asaraba."
sai ya kuma d'an tsagaita tare da kallon kekyawan fuskar Saifuddeen kana cikin tausayawa yace.
"Tabbas nasan akwai riba dan yar daddunmu ne suka sanar mana dan son ci gaban junanmu,
to matsalar uku daga cikinmu duk last week mukayi sari bamu da kud'i a k'asa asalima kaga sai yau kayan ya isomu,
sannan masu zuwa sari su zo su sara wanda yawanci bayan wata d'aya suke dawo da kud'in.
To da fari company wata biyu suka bada k'a'idar rufe sarin dan kamar bonanza ne zasuyi mana to sai kuma suka maida k'a'idar wata d'aya.
to shi kanshi uban gidanmu Alhaji Sani wata uku da suka gabata ne ya gama ginin sabon gidanshi inda ya k'aura ya koma yanzu,
to bashi da kud'i sosai a k'asa da zai ranta mana."
ganin yayi shirune yasa Saifuddeen gyara zamanshi tare rubuta mishi.
"To magin kuma kamar na k'asa da nawa zasu bada sarin?."
Numfashi Alhaji Kabiru ya furzar tare da cewa.
"To ai anan gizo ke sak'a domin sun san in sukace kad'an-kad'anne da yawa zasu iya sara,
so sai suka d'an saka hikimar da suma zasu samu wani abu,
sun bada tabbacin cewa mafi k'arancin sarin da zasu bada shine na 2 million,
tofa shisa duk jikinmu yayi sanyi da abun."
cikin d'imuwa Saifuddeen ya maimaita 2 million to shi tunda aka haifeshi yazo duniya baima tab'a ganin dubu dari biyar cikakku bama,
kai ya rink'a jujjuyawa da a zatonshi ko irin d'an sarin 100k ne zuwa 200k nan zai iya zaton zai samesu in ya fasa asusunshi,
tab'ashi da Alhaji Kabiru yayine ya dawo dashi daga duniyar tunanin daya tafi kai ya rink'a jujjuyawa jin tambayar da Alhaji Kabirun ya masa cewa.
"Kanada kud'in sari ne?."
ganin yanata jujjuya mishi kaine yace.
"Shiyasa nace abin da wuya ni du'du du yanzu dubu d'ari biyar nake dashi,
in samu wanda zamu had'a hannu muyi sarinma abin ya gagara ya rigada yanzu cinikaiya ta d'anyi k'asa, amman kaje kayi shawara in kanada yadda zaka samu 500k d'in kamar nawa sai mu had'a in sha Allah zan samu su Alhaji Sani sai mu had'a da wasu in an samu."
Cikin rauni da sanyi Saifuddeen ya jujjuya mishi kai tare rubuta mishi.
"Kud'in sunfi k'arfina bani da hanyarsu ko dalilinsu.
Ngd matuk'a da bani kulawa da shawara naji dad'in yadda kamin kekyawar fahimta."
Cikin kula ya kalleshi ganin yana shirin aza kwalin omonshi a kai alamun zai tafi murya a tausashe yace.
"Ba komai Saifuddeen wlh ni ina jinka tamkar d'ana na cikina,
na kuma yarda da amincinka,
muyi ta Addu'a Allah ya bamu sa'a."
A saman labb'anshi ya amsa da Amin Amin kana ya juya ya fita shagon.
Daga nan yaci gaba da tallanci yanayi cikin nasara,
randa yayi kwana biyu da zuwa wurin Alhaji Kabiru, da dare ya sake yin wani mafarki ma kamacin wanda yayi ranan,
sosai abin ya d'aure mishi kai al'wala yayi sannan yayi ta karatun Qur'an washe gari, ana fitowa sallan asuba yaga Sabir k'anin Saminu yazo gaban Bappa Ali inda ya shaida mishi wai babanshine ya aikeshi kan yazo ya gaya mishi yana son ganinshi anjima shida Saifuddeen.
jin haka bai wani damu Bappa Ali ba dan akwai alak'ar zumunci a tsaka ninsu in abi ya shafi na addini to ana nemanshi.
Sai dai da yaji yace shida Saifuddeen shiyasa ya hana Saifuddeen tafiya cikin gombe yace Salisu yaje kawai shi Saifuddeen yau bazai jeba sai gobe in Allah ya kaimu da haka Salisu ya tafi.
sosai ya saida kayan sanyin koda ya gama kafa na uku, sai ya wuce shagon su Jabeer nan sukayi ta hira har aka kira salla bayan sunyi salla kuma sai ya wuce shagon Alhaji Kabiru yana isa ya samu yaran shagon duk sunata hidiman jera kayayyakinsu bisa dukkan alamu sarin da sukayi ne ya iso,
shi kuwa Alhaji Kabiru yana cikin shagon bisa alamu lissafi yakeyi,
ganin haka sai Saifuddeen ya tsallaka ya shiga ciki can kusa da shi ya zauna cikin body language ya gaida Alhaji Kabiru da tuni ya gama lissafin ya had'a takardun wuri d'aya,
cikin mutuntaka da dattaku ya amsa gaisuwar Saifuddeen,
sai ya kuma kalleshi ganin yana mishi alamun tambyar ina woyarshi,
murmushi yayi tare da cewa.
"Wayata gata a aljihuna."
kai ya jinjina mishi kana ya mishi alamun ya fitar da ita zasuyi mgna,
gane hakan ya sashi zaro woyar,
daga nan ya suka fara mgna ta inbox nasu suna musanyan text messages,
sosai Alhaji Kabiru ya nitsu yana kallon text d'in da Saifuddeen ya tura mishi inda yake cewa.
"Assalamu alaikum, Alhaji ya gida ya kasuwa,
Allah ya taimaka."
sai ya rubuta mishi amsa da.
"Wa alaikassalam lfy lau Saifuddeen, Amin Amin. Naga kamar muhimmiyar mgna kakeson muyi, kada ka damu ka d'aukeni kamar mahaifinka ni ina ina jinka tamkar Isma'il d'ina."
Sosai Saifuddeen yaji dad'i mgnar hakan ya sashi murmusawa tare da rubuta mishi.
"Ngd matuk'a Alhaji." sai ya kuma yi shiru bai kuma rubuta komaiba ya rasa ta ina zai faro zancen gane haka yasa Alhaji Kabiru dafa kafad'unshi cikin bashi k'arfin guiwa yace.
"Ina jinka."
shi kuwa rusunar da kai yayi tare da rubuta mishi.
"Kayi hak'uri Alhaji ka gafarceni ranan asabar d'in da ya gabata, ka kirani na kawo maka ruwan sanyi, inda nazo na sameka da bak'i to nayi laifin fahimtar maganganunku, sai dai kuma naji ina sha'awar sanin kasuwancin da suke tallata maka,
in akwai damar da nima zan iya sa hannuna a ciki nima zanyi."
yana tura text d'in sai ya sunkuyar da kanshi,
shi kuwa Alhaji Kabiru murmushi yayi bayan ya gama karantawa cikin kekyawan fahimta ya dafa kafad'un Saifuddeen wanda ya sashi d'ago kai ya zuba mishi ido alamun jin na bakinshi.
Gyara zama yayi tare da zuba mishi idanu cikin sanyin sauti alamun yana son su sirranta zancen yace.
"Me zai hana zaka iya mana, ai duk abinda mai ji zai iya na kasuwanci in sha Allah zaka iya,
sai dai kuma fa wannan al'amarin da kamar wuya."
da sauri Saifuddeen ya gyara zama tare da fuskantarshi yana mai kallon motsin bakinshi ta yadda zai fahimceshi da kyau shi kuwa Alhaji Kabiru cikin tsarkakan zuciya ya fara mishi bayanin kasuwancin.
"Company Maggi ne suka kawo mana tallan Maggi a sirrance a matsayinmu na manyan dilolin maggi,
sun tallatama mana ne dan suna mana sha'awar ci gaba,
sun bamu sirrin company cewa nanda wata biyar magi zaiyi tsadan da bai tab'a yiba,
sun k'ara da ce mana mu fito da kud'ad'enmu mu sari maggin mu ajiye sun sanar damu cikin wata biyar zuwa bakwai company zai k'ara tsadan magi sun bamu tabbacin in sha Allah babu batun fad'uwa sai dai cin riba,
in dai bamuci riba ba toko bazamuyi asaraba."
sai ya kuma d'an tsagaita tare da kallon kekyawan fuskar Saifuddeen kana cikin tausayawa yace.
"Tabbas nasan akwai riba dan yar daddunmu ne suka sanar mana dan son ci gaban junanmu,
to matsalar uku daga cikinmu duk last week mukayi sari bamu da kud'i a k'asa asalima kaga sai yau kayan ya isomu,
sannan masu zuwa sari su zo su sara wanda yawanci bayan wata d'aya suke dawo da kud'in.
To da fari company wata biyu suka bada k'a'idar rufe sarin dan kamar bonanza ne zasuyi mana to sai kuma suka maida k'a'idar wata d'aya.
to shi kanshi uban gidanmu Alhaji Sani wata uku da suka gabata ne ya gama ginin sabon gidanshi inda ya k'aura ya koma yanzu,
to bashi da kud'i sosai a k'asa da zai ranta mana."
ganin yayi shirune yasa Saifuddeen gyara zamanshi tare rubuta mishi.
"To magin kuma kamar na k'asa da nawa zasu bada sarin?."
Numfashi Alhaji Kabiru ya furzar tare da cewa.
"To ai anan gizo ke sak'a domin sun san in sukace kad'an-kad'anne da yawa zasu iya sara,
so sai suka d'an saka hikimar da suma zasu samu wani abu,
sun bada tabbacin cewa mafi k'arancin sarin da zasu bada shine na 2 million,
tofa shisa duk jikinmu yayi sanyi da abun."
cikin d'imuwa Saifuddeen ya maimaita 2 million to shi tunda aka haifeshi yazo duniya baima tab'a ganin dubu dari biyar cikakku bama,
kai ya rink'a jujjuyawa da a zatonshi ko irin d'an sarin 100k ne zuwa 200k nan zai iya zaton zai samesu in ya fasa asusunshi,
tab'ashi da Alhaji Kabiru yayine ya dawo dashi daga duniyar tunanin daya tafi kai ya rink'a jujjuyawa jin tambayar da Alhaji Kabirun ya masa cewa.
"Kanada kud'in sari ne?."
ganin yanata jujjuya mishi kaine yace.
"Shiyasa nace abin da wuya ni du'du du yanzu dubu d'ari biyar nake dashi,
in samu wanda zamu had'a hannu muyi sarinma abin ya gagara ya rigada yanzu cinikaiya ta d'anyi k'asa, amman kaje kayi shawara in kanada yadda zaka samu 500k d'in kamar nawa sai mu had'a in sha Allah zan samu su Alhaji Sani sai mu had'a da wasu in an samu."
Cikin rauni da sanyi Saifuddeen ya jujjuya mishi kai tare rubuta mishi.
"Kud'in sunfi k'arfina bani da hanyarsu ko dalilinsu.
Ngd matuk'a da bani kulawa da shawara naji dad'in yadda kamin kekyawar fahimta."
Cikin kula ya kalleshi ganin yana shirin aza kwalin omonshi a kai alamun zai tafi murya a tausashe yace.
"Ba komai Saifuddeen wlh ni ina jinka tamkar d'ana na cikina,
na kuma yarda da amincinka,
muyi ta Addu'a Allah ya bamu sa'a."
A saman labb'anshi ya amsa da Amin Amin kana ya juya ya fita shagon.
Daga nan yaci gaba da tallanci yanayi cikin nasara,
randa yayi kwana biyu da zuwa wurin Alhaji Kabiru, da dare ya sake yin wani mafarki ma kamacin wanda yayi ranan,
sosai abin ya d'aure mishi kai al'wala yayi sannan yayi ta karatun Qur'an washe gari, ana fitowa sallan asuba yaga Sabir k'anin Saminu yazo gaban Bappa Ali inda ya shaida mishi wai babanshine ya aikeshi kan yazo ya gaya mishi yana son ganinshi anjima shida Saifuddeen.
jin haka bai wani damu Bappa Ali ba dan akwai alak'ar zumunci a tsaka ninsu in abi ya shafi na addini to ana nemanshi.
Sai dai da yaji yace shida Saifuddeen shiyasa ya hana Saifuddeen tafiya cikin gombe yace Salisu yaje kawai shi Saifuddeen yau bazai jeba sai gobe in Allah ya kaimu da haka Salisu ya tafi.