Sashe 11
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Yana zuwa d'aya daga cikin yaran shagon yace mishi. "Kana son ruwane?."
da sauri ya gyad'a mishi alamar eh.
shi kuwa yaro bud'e wani k'aton firiji yayi kana ya juyo ya kalleshi, sannan yace.
"Leda nawa kake so?."
hannunshi ya d'ago kana ya had'a yatsunshi biyu yayi mishi alama da leda biyu yakeso.
cikin mmki yaro ya kalleshi kana ya kawo mishi leda biyun sannan yace mushi.
"Kai kurmane?."
murmushi Saifuddeen yayi kana ya gyad'a mishi kai tare da mik'a mishi d'ari biyun,
amsa yayi tare da bashi canjinshi kana yace.
"Kuma naga kamar kana gane abinda nake fad'i ko?."
still kai ya gyad'a tare dasa lododin ruwan cikin bokatin daya saya d'in,
a take botikin yayi sanyi sabida ruwan yanada tsananin sanyi wasu har sun fara yin k'ank'ara,
shi kuwa yaron shagon ashirin ya kuma zarowa a al'jihunshi kana ya mik'a mishi tare da cewa.
"Gashi nayi maka ragin naira 10 cikin ko wanne leda akan yadda muke sararwa Allah ya baka sa'a inka k'arema kazo zan ajiye maka mai sanyi."
cikin murmushi Saifuddeen ya jujjuya mishi kai alamun baya son ragin, kana ya juya ya nuna mishi sauran yaran ya mishi alamun da sai dai in suma duk za'ayi musu ragin,
cikin sauk'e numfashi yaro yace.
"To sadaka na baka."
fuska ya had'e kana ya tsuguna gefe tare da rubuta mishi.
"Bara nazo makane da zakace sadaka ka bani? in sadaka kakeson badawa kaje gidan marayu da gajiyayyu, ni karka kashe min zuciya,
ka dai ajemin mai sanyi in wannan ya k'are zan kuma zuwa."
hannu yaron ya bashi sukayi musabaha lokacin daya karanta rubutun kana yace.
"To kayi hak'uri abokina sai ka dawo d'in."
kai ya jinjina kana ya juya hannunshi rik'e da botikin.
ya fara bin layi-layi yana yawo,
amman babu wanda yace mishi kawo,
har ruwan ya fara rage sanyi.
cikin gajiya ya dawo bakin shagon masu kayan kitchen inda ya huta jiyan nan, inda ya zauna jiyan yauma nan ya zauna ya tasa batikin a gabanshi.
yaron jiyan ne ya kula dashi cikin fara'a yace.
"Balarabe yauma ka zone?."
cikin gajiya ya lumshe mishi idanu alamar eh,
shi kuwa yaron shagon cikin karantar yanayinshi yace.
"To yau ma hutawa kazo yine ko zaka sayi abune?."
da ido ya nuna mishi botikin pure water enshin,
cikin sauri ya zaro ido tare da cewa.
"Wai kai dama tallan ruwa kakeyi ne?".
Kai ya gyad'a mishi tare gyara zamanshi,
cikin sanyi yace.
"To wai kai kurmane naga jiyama har ka tafi body language kakeyi min."
still sai ya d'aga mishi gira duka biyu alamun eh shi kurmane.
da sauri yaron ya kalli alajin shagon cikin tausayawa yace.
"Abba kalli wai wannan Balaraben kurmane kuma wai ruwa yake saidawa."
sai ya kuma kalli Saifuddeen tare da yin rau-rau kamar idanunshi zasu zubda hawaye,
ganin haka da sauri Saifuddeen ya jujjuya mishi kai sannan yasa hannunshi bisa idanunshi alamun kar yayi kuka.
still shima wanda ya kira da Abba sai ya zuba musu ido tare da cewa.
"To Hisham kafi ubangijin daya halicceshi a haka sonshi ne?
kada kayi kuka kasa mishi rauni,
ai ita Nakasa ba kasawa bace,
bare wannan mai nagartane Kaga dai jiya kun dad'e tare amman duk bamu gane kurma bane kuma kaga yana gane duk abinda muke cewa.
So shi bai sa nakasar jikinsa ta zamar mishi na zuciya ba."
Jin haka sai Hisham ya sharshe hawayenshi kana yayi murmushi tare da bawa Saifuddeen hannu yace.
"Daga yau kai aboki nane."
shima Saifuddeen murmushi yayi,
shi kuwa Alhaji Ibrahim al'barka ya samusu.
Sai ya kuma kalli costumers insu da suke cike da shagon inda d'aya daga cikinsu ta kalli botikin ruwa tare da cewa.
"Yauwa mai ruwa bani biyu, wlh tun d'azu nakeji k'ishin kamar zai karni."
gane abinda tace yasa Saifuddeen d'auko guda biyu ya mik'a mata,
amsa tayi tare da bashi ashirin d'in,
shi kuwa Alhaji Ibrahim cikin iya kula da bak'inshi yace.
"A a Hajia bar kud'in."
sai ya kuma kalli Saifudddeen tare da cewa.
"Basu ruwan kowa ya d'auki yadda zai isheshi."
ai nan matan nan kowa ta d'auka wasu bibbiyu wasu d'addaya wasuma cikin hand bags nasu suke ajiye ruwan,
tuni sun d'auke yafi rabi.
lissafi akayi don lokacin ne forko-forkon da pure water ya tashi daga d'aya biyar ya koma d'aya goma,
to nanfa had'a lissafi inda kud'inshi ya kama d'ari da hamtsin.
aifa sai yaji k'arfin guiwa ya mik'e yabi layin masu saida gonjo wanda kusan a rana suke,
cikin k'udurar ubangiji ya saida ruwan tsab,
ba tare da yin k'asa a guiwaba yaje ya kuma saro leda biyu,
nan sai ya fito bakin kasuwa nanfa 'yan acab'a suka rink'a saya wani a take yake shanye leda biyu wani har leda uku ya saya bar masu sayan d'ad'd'aya,
kana masu taxi ma wasu sai su sayi lada hud'u su aje cikin yar durowar motar nasu.
Cikin awa d'aya wannan leda biyun suka k'are,
ai da sauri ya kuma komawa ganin azahar tayi sai ya amso leda d'aya,
kafin kace kobo ya k'are dan masuyin Al'walene sukayi ta kiranshi suna saya,
ganin saura d'aya sai yayi Al'wala dashi ganin a layin shagonsu Jabeer yake sai yaje ya ajiye botikin a barandar shagunsun gefen gadajen jarirai,
sahun salla ya shiga,
bayan an idarne ya yi addu'o'inshi sannan yaje d'aukan botikin nashi, Jabeer na ganinshi yace.
"Aboki balarabe dama har yanzu kana k'asar tamu ne?."
hararan wasa Saifuddeen ya cilla mishi dan ya gaya mishi shi bafullatanine ba balarabeba, so da yake Jabeer yanada far-far da jama da wasa da dariya sai yace shi dai yasan sai in satoshi akayi daga saudia.
botikin ya d'auka kana ya d'an harari Jabeer tare da tsuke fuska irin na abokai sannan ya bashi hannu.
da sauri Jabeer ya kamo hannunshi tare da cewa.
"Yoh ai dole ma in baka hannu ko zan samu ka rab'a min farinka da laushin hannunka."
dariya yaran shagon sukayi baki d'aya,
kana sai ogansun yace.
"Gashi dai duk muna inuwa fanka na kad'awa muci abinda mukeso, shi kuma gararamba kawai yake a kasuwa amman in ka ganshi sai kace daga fadar masarautar saudia ya fito."
cikin had'e fuska Saifuddeen ya zaro biron dake aljihun rigar Jabeer kana ya fara rubutu a tafin hannunshi yana gamawa ya nunawa ogan nasu tafin hannun nashi,
kusan a tare suka lek'o da idanunsu bisa tafin hannunshi cikin mmki suke karanta rubutun da yayi da fillanci.
"Oga ba gararamba nakeyiba fa inada sa'a ta nima ba yawon banza nake a kasuwarba pure water nike saidawa."
cikin mmki suka kalli juna tare da had'a baki wurin cewa.
"Ikon Allah kunga wlh da gaskene fa bafillacene."
shi kuwa ogan nasu murmushi yayi tare da cewa.
"Eh gskyarka ba gararamba kakeyiba ai shi mai sana'a ba matsiyaci ba,
yanzu je ka kawo mana ruwan dan yanzu zamuci abinci."
aifa da jin haka ya juya ya fita su kuwa sai Al'ajabi sukeyi,
yanzu dai sun tabbatar shi kurmane kuma bafillatanine kana yana gane abinda ake fad'i in yana ganin bakin mutun.
da sauri ya gyad'a mishi alamar eh.
shi kuwa yaro bud'e wani k'aton firiji yayi kana ya juyo ya kalleshi, sannan yace.
"Leda nawa kake so?."
hannunshi ya d'ago kana ya had'a yatsunshi biyu yayi mishi alama da leda biyu yakeso.
cikin mmki yaro ya kalleshi kana ya kawo mishi leda biyun sannan yace mushi.
"Kai kurmane?."
murmushi Saifuddeen yayi kana ya gyad'a mishi kai tare da mik'a mishi d'ari biyun,
amsa yayi tare da bashi canjinshi kana yace.
"Kuma naga kamar kana gane abinda nake fad'i ko?."
still kai ya gyad'a tare dasa lododin ruwan cikin bokatin daya saya d'in,
a take botikin yayi sanyi sabida ruwan yanada tsananin sanyi wasu har sun fara yin k'ank'ara,
shi kuwa yaron shagon ashirin ya kuma zarowa a al'jihunshi kana ya mik'a mishi tare da cewa.
"Gashi nayi maka ragin naira 10 cikin ko wanne leda akan yadda muke sararwa Allah ya baka sa'a inka k'arema kazo zan ajiye maka mai sanyi."
cikin murmushi Saifuddeen ya jujjuya mishi kai alamun baya son ragin, kana ya juya ya nuna mishi sauran yaran ya mishi alamun da sai dai in suma duk za'ayi musu ragin,
cikin sauk'e numfashi yaro yace.
"To sadaka na baka."
fuska ya had'e kana ya tsuguna gefe tare da rubuta mishi.
"Bara nazo makane da zakace sadaka ka bani? in sadaka kakeson badawa kaje gidan marayu da gajiyayyu, ni karka kashe min zuciya,
ka dai ajemin mai sanyi in wannan ya k'are zan kuma zuwa."
hannu yaron ya bashi sukayi musabaha lokacin daya karanta rubutun kana yace.
"To kayi hak'uri abokina sai ka dawo d'in."
kai ya jinjina kana ya juya hannunshi rik'e da botikin.
ya fara bin layi-layi yana yawo,
amman babu wanda yace mishi kawo,
har ruwan ya fara rage sanyi.
cikin gajiya ya dawo bakin shagon masu kayan kitchen inda ya huta jiyan nan, inda ya zauna jiyan yauma nan ya zauna ya tasa batikin a gabanshi.
yaron jiyan ne ya kula dashi cikin fara'a yace.
"Balarabe yauma ka zone?."
cikin gajiya ya lumshe mishi idanu alamar eh,
shi kuwa yaron shagon cikin karantar yanayinshi yace.
"To yau ma hutawa kazo yine ko zaka sayi abune?."
da ido ya nuna mishi botikin pure water enshin,
cikin sauri ya zaro ido tare da cewa.
"Wai kai dama tallan ruwa kakeyi ne?".
Kai ya gyad'a mishi tare gyara zamanshi,
cikin sanyi yace.
"To wai kai kurmane naga jiyama har ka tafi body language kakeyi min."
still sai ya d'aga mishi gira duka biyu alamun eh shi kurmane.
da sauri yaron ya kalli alajin shagon cikin tausayawa yace.
"Abba kalli wai wannan Balaraben kurmane kuma wai ruwa yake saidawa."
sai ya kuma kalli Saifuddeen tare da yin rau-rau kamar idanunshi zasu zubda hawaye,
ganin haka da sauri Saifuddeen ya jujjuya mishi kai sannan yasa hannunshi bisa idanunshi alamun kar yayi kuka.
still shima wanda ya kira da Abba sai ya zuba musu ido tare da cewa.
"To Hisham kafi ubangijin daya halicceshi a haka sonshi ne?
kada kayi kuka kasa mishi rauni,
ai ita Nakasa ba kasawa bace,
bare wannan mai nagartane Kaga dai jiya kun dad'e tare amman duk bamu gane kurma bane kuma kaga yana gane duk abinda muke cewa.
So shi bai sa nakasar jikinsa ta zamar mishi na zuciya ba."
Jin haka sai Hisham ya sharshe hawayenshi kana yayi murmushi tare da bawa Saifuddeen hannu yace.
"Daga yau kai aboki nane."
shima Saifuddeen murmushi yayi,
shi kuwa Alhaji Ibrahim al'barka ya samusu.
Sai ya kuma kalli costumers insu da suke cike da shagon inda d'aya daga cikinsu ta kalli botikin ruwa tare da cewa.
"Yauwa mai ruwa bani biyu, wlh tun d'azu nakeji k'ishin kamar zai karni."
gane abinda tace yasa Saifuddeen d'auko guda biyu ya mik'a mata,
amsa tayi tare da bashi ashirin d'in,
shi kuwa Alhaji Ibrahim cikin iya kula da bak'inshi yace.
"A a Hajia bar kud'in."
sai ya kuma kalli Saifudddeen tare da cewa.
"Basu ruwan kowa ya d'auki yadda zai isheshi."
ai nan matan nan kowa ta d'auka wasu bibbiyu wasu d'addaya wasuma cikin hand bags nasu suke ajiye ruwan,
tuni sun d'auke yafi rabi.
lissafi akayi don lokacin ne forko-forkon da pure water ya tashi daga d'aya biyar ya koma d'aya goma,
to nanfa had'a lissafi inda kud'inshi ya kama d'ari da hamtsin.
aifa sai yaji k'arfin guiwa ya mik'e yabi layin masu saida gonjo wanda kusan a rana suke,
cikin k'udurar ubangiji ya saida ruwan tsab,
ba tare da yin k'asa a guiwaba yaje ya kuma saro leda biyu,
nan sai ya fito bakin kasuwa nanfa 'yan acab'a suka rink'a saya wani a take yake shanye leda biyu wani har leda uku ya saya bar masu sayan d'ad'd'aya,
kana masu taxi ma wasu sai su sayi lada hud'u su aje cikin yar durowar motar nasu.
Cikin awa d'aya wannan leda biyun suka k'are,
ai da sauri ya kuma komawa ganin azahar tayi sai ya amso leda d'aya,
kafin kace kobo ya k'are dan masuyin Al'walene sukayi ta kiranshi suna saya,
ganin saura d'aya sai yayi Al'wala dashi ganin a layin shagonsu Jabeer yake sai yaje ya ajiye botikin a barandar shagunsun gefen gadajen jarirai,
sahun salla ya shiga,
bayan an idarne ya yi addu'o'inshi sannan yaje d'aukan botikin nashi, Jabeer na ganinshi yace.
"Aboki balarabe dama har yanzu kana k'asar tamu ne?."
hararan wasa Saifuddeen ya cilla mishi dan ya gaya mishi shi bafullatanine ba balarabeba, so da yake Jabeer yanada far-far da jama da wasa da dariya sai yace shi dai yasan sai in satoshi akayi daga saudia.
botikin ya d'auka kana ya d'an harari Jabeer tare da tsuke fuska irin na abokai sannan ya bashi hannu.
da sauri Jabeer ya kamo hannunshi tare da cewa.
"Yoh ai dole ma in baka hannu ko zan samu ka rab'a min farinka da laushin hannunka."
dariya yaran shagon sukayi baki d'aya,
kana sai ogansun yace.
"Gashi dai duk muna inuwa fanka na kad'awa muci abinda mukeso, shi kuma gararamba kawai yake a kasuwa amman in ka ganshi sai kace daga fadar masarautar saudia ya fito."
cikin had'e fuska Saifuddeen ya zaro biron dake aljihun rigar Jabeer kana ya fara rubutu a tafin hannunshi yana gamawa ya nunawa ogan nasu tafin hannun nashi,
kusan a tare suka lek'o da idanunsu bisa tafin hannunshi cikin mmki suke karanta rubutun da yayi da fillanci.
"Oga ba gararamba nakeyiba fa inada sa'a ta nima ba yawon banza nake a kasuwarba pure water nike saidawa."
cikin mmki suka kalli juna tare da had'a baki wurin cewa.
"Ikon Allah kunga wlh da gaskene fa bafillacene."
shi kuwa ogan nasu murmushi yayi tare da cewa.
"Eh gskyarka ba gararamba kakeyiba ai shi mai sana'a ba matsiyaci ba,
yanzu je ka kawo mana ruwan dan yanzu zamuci abinci."
aifa da jin haka ya juya ya fita su kuwa sai Al'ajabi sukeyi,
yanzu dai sun tabbatar shi kurmane kuma bafillatanine kana yana gane abinda ake fad'i in yana ganin bakin mutun.