← Book details Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 101 OF 116

Sashe 101

Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cak ya tsaya daga tafiyan da yakeyi, amma saidai ko motsawa baiyi ba balle tasa ran cewa zai juyo ta kalli fuskarsa.
Ahankali tashiga takawa zuwa garesa, taku biyu kacal ya rage taƙarasa garesa,  ahankali yaɗan juyo gareta,  idanunta ne suka sauƙa akan kyawawan laɓɓansa wanda ke ɗauke da kalar red, yayinda wasu kwantattun gargasa sukayiwa bakinnasa ƙawanya, wani irin sheƙi da shinnig gashin dake kwance akan fuskar tasa keyi, idanunta taɗaga daniyar kallon full face ɗinsa, kafun ta sauƙe ganinta akansa wani irin haske wanda batasan daga ina yafito ba ya cika gaba ɗaya idanunta.
Azabure ta-tashi daga baccin da takeyi, cikin ƙaraji tace "Dan Allah kada katafi pleaseee help me!!!."
Buɗe idanunta wanda suka kaɗa sukai jajur tayi, lokaci guda wani irin gumi ya shiga keto mata,  ƙirjinta ne yashiga bugawa da sauri sauri,    aƙalla taɗauki kusan 3 minute kafun taɗan soma dawowa cikin hayyacinta gane cewa mafarki take yasanyata sakin kuka mai ciwo, jikinta ta takure waje ɗaya tare da cusa kanta tsakankanun cinyoyinta, kuka take rerawa sosai mai ɗauke da tsanin ciwon so, cikin rufewar ido haɗi da sambatu tace.

"Shikenan katafi kabarni? yazanyi? shin tayaya kake tunanin zan iya jure rashinka? nazautu akan sonka, nakai ƙololuwa,  nazama kurma, makauniya,  har wasu suna mini kallon zautacciya duk akan sonka,  Ina sonka! Ina sonka! Ina tsananin sonka!!!."  Taƙare maganar tana me rushewa da kuka, sosai Zaleeha tayi kuka awannan dare har da shiɗewa,  daƙyar ta iya jan jikinta ta wuce toilet, wanke fuskarta tayi kana ta ɗauro alwala, sosai wani irin zazzafan zazzaɓi da ciwon kai suka rufeta asakamakon kukan da tayi, wata zumbuleliyar hijab ta sanya ajikinta, inda ta hau kan shunfuɗaɗɗen dardumanta, cikin tsananin ciwon da kanta keyi mata tagabatar da sallan Nafila raka'a huɗu,  zama tayi akan praymad  tare da jingina bayanta da jikin bango, idanunta ta lumshe, ahankali wasu zafafan hawaye suka shiga kwaranyowa daga cikin idanun nata, ji take kamar zuciarta zata fashe saboda soyayyarsa, ashe dama haka so yake? ada taɗauki batun so wasa sai gashi kuma yanzu yana shirin yi mata ɓarin kwan makauniya, haƙiƙa gangar jiki da zuciyarta na azabtuwa, Inama da ace yin so baizama ɗaya daga cikin Ƙaddarorinta ba,  kuka tacigaba dayi sannu ahankali wani wahalallen bacci ya samu nasaran ɗaukarta..

Kamar yanda ya ƙudurta aransa hakance ta kasance, zuwa yanzu yasanar dasu Baffa Ali gaba ɗaya abun dake faruwa.

5 million ya ware daga cikin ribarsa,  ayau yau yake da buƙatar haɗa kayan lefe, inda Baffa Ali yace ya ɗauke masa nauyin biyan sadaki.
Aunty  Kubra matar yayan Abokinsa Jabeer dakuma Adda Rahama sune suka shiga cikin babban kantin nan na San Hussain Super Market don haɗo masa kayan aure nagani na faɗa,  dayake Aunty Kubra cikakkiyar ƴar kasuwace kuma sana'anta kenan saida kayan mata, hakan yasanya sosai ta darje wajen zaɓo zafafan lesuka, atamfofi, shaddodi, materials,  dakuma tsadaddun yadukan boyels na mata, kaya sosai suka saya masu tsananin tsada don kuwa kaf cikin kayan nasu babu wanda kuɗinsa yayi ƙasa da dubu Hashirin talatin dai arba'in dai kana hamsin, ɓangaren jakakkuna da takalma kuwa ba acewa komai domin kuwa kaya suka saya masu kyau da inganci.
sashin yan kunnaye da awarwaro haɗi da saraƙa kuwa komai na gwal suka saya,   ɓangaren takalma da jaka kuwa ko wani takalmi da mayafinsa, kana kuma da kalan kayansa, materials, lace, atamfa ko boyel,   sashin ƙananan kaya kuwa abun ba'acewa komai, ɓangaren dogin riguna kuwa saida suka cika akwatuna biyu tam da dogin riguna masu kyau da tsada, domin kaf cikin rigunan babu ta ƙasa da 30k, kaya kam dai sun haɗu sosai, musamman ɓangaren kayan meckup sun kashe kuɗi sosai, musamman suka sayi meckup kit har guda uku,   masha Allah kaya ya haɗu sosai inda aka shirya kayan cikin akwatuna, tsab kayan suka ɗauke gaba ɗaya akwatuna 24 dozin biyu kenan sai guda shida da akasa kayan uwa da uba a akwati sauran ukun kuma akasa na dangi shine ya bada akwati 30 da suka saya.   Koda suka dawo gida kowa saida ya yaba kayan domin anyi abu wanda sam babu ƙaranta aciki, ko ƴar Gwomna aka kaiwa ba laifi. ya ware Million uku da rabi ya bawa Salisu, tare da cewa ya kawo mishi dan ƙareriyar mota mai kyau ta mata irin wacce ake yayi.

Shima Salisu nan yayi tasa bajintar, inda ya kawo haɗaɗɗiyar mota har ta million huɗu.

Can cikin gida kuwa tuni su Adda Rahama, Aunty Mina, Aunty Kubra, matar yayan Jabeer, da Goggo Dada, da  Hajia Rabi matar Alhaji kabiru duk suna cike a parlour Ummi, musamman sukazo don kai lefen Saifuddeen.

Hayatuddeen da abokanshi Imran da Sulaiman ne suka shigo da kayayyakin.
Wanda Ahmad yake matuk'ar jin takaici da bak'in cikin yawan kuɗaɗen da aka ɓatar akan yarinyar da ba mutunci ne da itaba.

Gaba ɗaya sun cika da mamakin irin Yanda Saifuddeen ya narka kuɗi wajen ƙawata kayan,
Hajia Rabi ce tace.
Sam baza'a kai kayan nan duka ba dole a rabashi biyu, ai wanna almobazzaranci ne.
Ita dai Ummi shiru tayi tare da danne ainihin abinda ke ranta wanda babu mahaluk'in da zai gane meke cikin ranta.
Aunty Kubra ce tace a a banda dai a raba biyu kam,
dan ita bata son harkan ƙaranta,
ita da tasoma a Dubai zasu haɗo lefen dan dai kawai abin yazo a ƙurarren lokaci ne, ta nace dole saida aka rarrage wasu abubuwan wasu kuma tama hana fir.

A gidan Baba malam kuwa tun jiya da yamma da Dirankadi ya shaida mishi gobe fa za'a kawo komai da komai kama daga gishiri goro da lefe da kayan rufi da sadaki,
duk zasu kawo a tare sai ya gayawa Mamy.
dan Mama yanzu ko Magana bata mishi, shiyasa shi kuma ya shareta dan ya bata iya matsayinta na uwa so yanzu dole ya nuna mata koda ita ko ba ita dole nefa zai aurar da yarsa ga wanda takeso, ya ga kuma ya dace da ita.

Daga nan ya ƙira ƙanwarshi Goggo Maryama ta kwarar Maryam yayar Zaleeha kenan.
Kana ya sanar da ita Maryam ɗin.
sannan matar abokinshi Malam Adam itama tazo,
sai Maman Ya Aminu matar yayanshi kenan,
ga Lubna matar Ahmad nan fa Lubna da Maryam suka shiga kitchen tunda safe
suka fara shirya abin tarban baƙi, waƴanda za abawa ƴan kawo lefe da kuma abinda za'a basu su tafi dashi gida, kamar yanda al'adar Gombawa take.
Mommy matar malam Adam ƙawar Mamy mace mai sauƙin kai gata ta iya girki da kala-kala kasancewar shuwa arab ce. Tana matuƙar son Zaleeha haka itama Zaleeha duk cikin matan abokan Baba malam  da suke ƙawayen Mamy tafi sonta.

Sosai suka shirya komai cikin manya-manyan food flask masu azabar kyau,
yayinda tuni sun cika fridge da ƙawatattun drinks.

Mama kuwa dama yau tunda sanyin safiya ta tafi Doho gidan yayarta Ruda da takebi wacce itama arniya ce dan duk zuriyar Mama ita kaɗaice ta musulunta sai ƙanwarta mai binta,
wacce ta sauya suna daga Rebeka ta dawo Aisha.
tana nan cikin Gombe da mijinta da yaranta Aisha macece mai nitsuwa da kamala sau da dama tana dakatar da yayar tata daga aikata wasu mugayen ɗabi'u da sukafi dacewa da masu aljihun baya.
Yayinda Ruda kuwa ke ingizata.

Ƙarfe uku da rabi  na yammaci dai-dai,
Salisu yazo da Matarsa Sadiya da zazzafar motarsa,
Kana Ahmad ya d'auki motar Saifuddeen,
sai kuma Aunty Kubra da Jabeer yazo ya amshi tuk'in haɗaɗɗiyar motarta ƙiran babbar vibe,
sai kuma Motar Ishaq da direbanshi. sai Motar ya Adnan. Sai dalleliyar mota kirar kia samfurin bugun 2019, wacce take baƙa mai Shek'i dan har an kawo fara Saifuddeen yace,
ai ita farar macece dan haka baƙa za'a kawo mata, don haka dole aka canzo aka kawo mata kalar da yake so ɗin.
Nan duk suka kwashi kayan suka shirgeshi cikin motar kana aka bawa Muddasir Key ɗinta yaja.

A jere-a Jere suke tafiya yayinda,
Hayatuddeen ke cikin motar Aunty Kubra,
yana gaba gefen Ya Jabeer. Ita kuwa Aunty Kubra ita da Aunty Mina suna baya.
Imran kuwa motar ya Adnan ya shiga yana gaba kusa dashi baya kuma Adda Rahma ce da Goggo Dada.
Sai motar Saifudddeen da Ahmad ne  aciki,Raliyanshi na gefenshi,
tana ta son sama mishi farin ciki dan ta lura sam shi baya wani farin ciki da abun.

Sai Hajia Rabi dage gefenshi wacce itama sam bata farin ciki da abin sabida Hayatuddeen yana gaya mata komai.
sai motar ishaq wacce ba komai a ciki shiyasa shida Saifuddeen suka shiga baya direbanshi yaja,
suka nufi can k'ungiyar tasu.

Shima Ahmad sam baiso zuwaba to ya zaiyi dole yaje.

Su kuwa masu kai lefen.
Suna isa bakin Gate ɗin gidan mai gadi ya wangale musu gate inda suka kutsa cikin gidan cikin nutsuwa,
bayan sun gama yin parking ne.
Ahmad ya fito ya nufi wurin mai gadin,
hannu ya bashi suka gaisa sannan yace mishi ya shiga cikin gida yace bak'in sun iso.
Cikin mutuntawa mai gadin yace to tare da juyawa ya shiga cikin gidan.

Jim kaɗan ya fito yace.
Ance su isa.

Nan duk matan suka shiga su kuma mazan duk suka zauna cikin motocin.

Suna shiga cikin gidan Maryam tayi musu jagora har babban parlour Mama duk da bata nan dole a bata matsayinta na uwa.
Bayan sun zazzauna, an gaisa cikin mutun taka, an kawo musu drinks da snacks, sun ɗan taɓa abin sha.
Hajia Rabi ce ta gyara zama tare da cewa.
"Raliya je kice Imran Suleiman da Hayatudeen su shigo da kayan."
A hankali ta mik'e tare da cewa.
"To."
Chapter 101 · 0% Book details