Sashe 45
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Shi kuwa Saifuddee ganin abinda Dalla yayi mata tun fasa mata glass da yayi ya nufo kansu da gudu so kasancewar akwai 'yar tazara tsakaninsu gashi sai ya ratsa gaban babura da keke napeps da motocin da suka cika titin yasa kafinma ya isa tuni Dalla ya shiga motarshi,
kana babura da napep da motoci duk sun fara shirin wucewa wonda dole suke ratsawa ta gefen motarta. Itako tunda ya mareta zafin marin da gigita yasa ta fad'in gaban motar tata ta kifu samanshi.
Cikin gudu da sassarfa ya isa gareta, yana zuwa yasa hannunshi duka biyu ya kamo kafad'unta, kana ya d'agota ya tsaidata suna fuskantar juna yadda in tayi mgna zai iya ganewa,
idonshi ya rumtse da k'arfi ganin jini na bin hancinta kana tuni fuskarta tayi jazir hatta shatin yatsunshi sun taso a fuskarta,
ga wasu zafafan hawaye dake kwaranya a idanunta sabida rad'ad'in marin da k'unar zuciya kan cimata zarafi da tozartata da akayi a tsakiyar gari.
shi kuwa Saifuddeen tuni fuskarshi ta sauya launi daga fara ta koma jazir kana idanunshi tamkar su amayar da wuta tuni jijiyoyin kanshi suka taso,
yayinda jijiyar kan goshinsa tayi ziwat har kan tsinin karan hancinsa a fili zaka gane zallan b'acin rai, gaba d'aya jikinshi tsuma yakeyi,
ido ya zubawa fuskarta kana itama ido ta zuba mishi cikin rauni da muryar kuka tace.
"Wlh ban saniba bada gaggan na buga mishi motarshi ba hankalina ya tafi wurin kallon wani ne."
lips enshi na k'asa ya taune da k'arfi tamkar zai hudashi,
kana ya kama hannunta tare da yi mata nuni data shiga motarta,
cikin rawan jiki ta nufi gefen direban,
hannunta ya kamo da sauri, juyowa tayi tana kallonshi itama kai ya jujjuya mata alamar a a kana ya nuna mata gefen mai zaman banza,
ba musu ta zagaya ta shiga ta zauna.
Shi kuwa gefen driving sit ya shiga ya zauna,
sit bell yaja ya sank'ala jikinshi,
kana ya juyo ya kalleta tare da yi mata alamu da idonshi tasa nata sit bell d'in.
ba musu ta saka,
sai ta kuma d'ago kanta da sauri jin ya dannawa motar Key kana ya figi motar a guje,
ido ta zazzaro ganin yadda yake tsula gudu tamkar zai tashi sama,
gudu yakeyi da tsanani amman cikin bin k'a'ida da dokar tuk'i cikin abinda bai gaza 5 minutes ba ya cimma motocin su Dalla, yayinda su kuwa tuni sun mik'a hanyar data ratsa bakin kasuwa zata kuma wuce zata bi ta kaisu fantami daga nan su ratsa bayan gidan goje,
binsu yakeyi kib da kib haka yasa suka gane binsu akeyi,
tuni kuma an fara kiraye-kirayen sallan mangrib,
murmushin mugunta Dalla yayi kana ya juya akalar motarshi ya shiga cikin sitadiyon ,
shima binsu yayi a baya kusan a tare sukayi parking.
cikin azama da zafin nama ya bud'e ya fito kana ya zagoyo inda take ya bud'e mata tare da kamo hannunta ya juyo ya nufi inda motar Dalla take,
shima Dalla wurinsu ya nufa,
a tsakiyar sitadiyon d'in sukayi kicibus,
cikin wani yanayi mai wuyar fassarawa Saifuddeen yayiwa Dalla alama da hannu akan ya bata hak'uri.
cikin izaya da tak'ama Dalla ya gyara tsayuwanshi tare da cewa.
"Baka da bakine ko iskanci ne zaka zo kana min mgnar kurame?."
cikin tsuke fuska Saifuddeen ya kuma yimishi alamu daya bata hak'uri, ganin haka Dalla ya kuma motsotsu kana yace.
"OK kyautarta ka kawo min kenan?, baka san waye Dalla bako? shiyasa ka biyoni da mace kana nufin in bata hak'uri ne ko?."
cikin sauri da jin dad'in Dalla ya fahimci abinda yake nufi ya tsare fuska kana ya gyad'a mishi kai alamar eh ka bata hak'uri.
wani fatsik'in murmushi Dalla yayi tare da lashe manyan lip's enshi yace.
"Hmmm aini Dalla bana bada hak'uri sai dai in bata ciki tunda ka biyoni da ita, gata kuma zata iya kashe kishin dake addabata wunin yau gaba d'aya ban hutaba kaga yanzu na samu wurin hutawa gashi tanada lafiyayyun kayan marmari a jikinta, yanzu zan mata inkiyata Dalla-dalla da budurcinta zan rab'i jikinta."
Ya k'arishe mgnar tare da kai hannunshi kan k'irjinta.
Wani irin wawan ihu da kururuwa Dalla ya kurma jin wani irin damk'a da Saifuddeen yayiwa hannunshi ba tare da ya samu ya isar da hannun nashi kan k'irjintan ba,
ihu Dalla ya kuma kurmawa jin Saifuddeen ya kuma murd'a mishi hannunshi har saida ya bada sautin b'as alamun ya k'arya mishi hannun, ihun daya sane yasa tarin zugan matasan dake cikin sauran motoci hud'un nan duk suka fito,
wando gaba d'ayansu 'yan kalarene domin duk kansu da makamai a hannunsu wasu da sanduna wasu da kataki wasuma da wuk'ak'e.
A guje suka nufin inda suke, shi kuwa Saifuddeen ko kad'an bai karaya da ganinsu ba,
asalima zagewa yayi ya fara dukan Dalla tamkar Allah ne ya aikoshi,
kunsan fad'an kurma babu sauk'i shiyasa basa tsokana basa tada husuma sabida sun san zuk'atansu basa iya jurar suga ana raini ko zalumci bare fajirci.
sam Dalla ya gaza bawa kanshi kariya,
shiko Saifuddeen dukan ƙaton gargadi yakewa Dalla tare da dandatseshi ta yadda bazai sake sha'awar wata d'iya maceba a duniyar nan har gaban abadan, ita kuwa Zaleeha ganin yadda suka nufo kansu haik'an k'adaran ne yasata sakin ihu tare da bubuga tsalle tanayi tana yarfa hannu tana cewa.
"Zomu gudu zasuyi maka illa zasu kasheka fa,
kazoo mugudu karsu isomu zasu illata ka."
ganin sam bai sararawa Dallanba yasa tayi sauri ta shiga tsakanin su kana ta rik'o hannayenshi tare da kallon fuskarshi tace.
"Mu gudu zafa su kashemu."
ido ya d'ago ya kalleta yadda jikinta ke rawa tamkar mazari tsoro da firgici k'arara a idanunta da ka ganta kasan cikekkiyar matsoraciya mai lasisi ce, haka yasa ya kamo hannunta kana ya juya da ita inda motarta take,
su kuwa zugan 'yan kalaren nan kansu suka nufo a guje ganin hakane yasa,
yajata da k'arfi sannan ya bud'emata motartata wurin zaman direba ya ajiyeta kana ya meda marfin ya rufe sannan ya sunkuyo kanta tare da kad'a mata yatsunshi biyu kana yayi mata alama dataja motar ta gudu, gane abinda yake nufine yasa ta jujjuya kai tare da zubda hawaye cikin haki tace.
"Mutafi zasu kasheka fa 'yan kalarene fa yaranshi ne."
ganin zata b'ata lokaci har suzo su sameta suyi mata illane yasashi buga marfin motar da k'arfi tare dayi mata gurnani irin nasu na kurame wanda in bawai ka saniba sai kayi zaton tsawa ya buga mata hakance ta kasance ga Zaleeha dan jin sautinshi tayi a sama haka yasa ta figi motarta a guje, tana jan motar suna isowa inda yake, yayinda shi kuwa yake kallonta so yake yaga fitanta a wurin, su kuwa suna isa inda yake ba tare da ya juyoba don shi dai kurmane bazaiji sautin takun k'afafunsu ba,
suna isa d'aya daga cikinsu ya narka mishi k'aton katakon dake hannunshi a tsakiyar gadon bayanshi kafin, yayi wani yunk'urinma
d'aya daga cikinsune ya dab'a mishi wuk'a a tsakiyar bayanshi kana ya zaro wuk'ar wanda tuni sun farka mishi rigarshi
wani irin razanennen ihu Zaleeha tasaka tare da zubawa bayanshi ido sabida tana ganinshi ras dan hasken motoci dake haska wurin da hasken fitulun dake zagaye da farfajiyar wurin
cikin tsananin tsoro da firgici taja motarta ta bar sitadiyon d'in,
tana fita kai tsaye gombe division ta nufa.
Shi kuwa Saifuddin tuni sun mishi illa sun daddatsa mishi kataki a tsakiyan bayanshi.
yayinda duk da haka bai bar kare kanshiba sai dai ance sarkin yawa yafi sarkin k'arfi gashi sun zomishi ta bayanshi kuma sunzo tare da makamai yayinda shi kuwa babu ko allura a jikinshi,
haka yasa sukayi mishi illah mafi muni a jikin d'an adam, haka suka rink'a hankad'ashi kan k'arafun wurin suna buga bayanshi a kai
saida sukaga yabar motsi kana suka dauki uban gidansu da Saifuddeen ya daddaga mishi jelershi sukaja motocinsu suka tafi,
yayinda tuni mazauna wurin kuwa sun watse don kowa yasan rashin mutuncin Dalla.
Shiru cikin sitadiyon d'in ba ko tsuntsu sai Saifuddin dake yashe tamkar mamaci,.
Ita kuwa Zaleeha bayan ta sanarwa hukuma, ganin ita macece kuma sananniya kana yar babban Malamin da akeji dashi a fad'in jihar dama k'asar bak'i d'aya yasa aka had'ata da police officer d'aya ya rakata gidansu dake New G.R.A...
A haka police officers na station d'in gombe division suka iso,
yayinda aka had'a da sosojin Anty kalare,
kana
suna isowa ganin halin da yake ciki ne yasa suka d'aukeshi,
kai tsaye general hospital Gombe suka nufa dashi, kai tsaye aka wuce dashi o,p,d. suna isa ma aikatan wannan sashin suka turo irin yan wannan gadaje na d'aukar marasa lfy,
tare dasa hannun hukuma aka karb'eshi bayan an duddubashi ganin aikin babbane ya kuma ji rauni sosai ne sai aka basu takarda wacce zata sadasu da babban likitan dake Medical Center.
kana babura da napep da motoci duk sun fara shirin wucewa wonda dole suke ratsawa ta gefen motarta. Itako tunda ya mareta zafin marin da gigita yasa ta fad'in gaban motar tata ta kifu samanshi.
Cikin gudu da sassarfa ya isa gareta, yana zuwa yasa hannunshi duka biyu ya kamo kafad'unta, kana ya d'agota ya tsaidata suna fuskantar juna yadda in tayi mgna zai iya ganewa,
idonshi ya rumtse da k'arfi ganin jini na bin hancinta kana tuni fuskarta tayi jazir hatta shatin yatsunshi sun taso a fuskarta,
ga wasu zafafan hawaye dake kwaranya a idanunta sabida rad'ad'in marin da k'unar zuciya kan cimata zarafi da tozartata da akayi a tsakiyar gari.
shi kuwa Saifuddeen tuni fuskarshi ta sauya launi daga fara ta koma jazir kana idanunshi tamkar su amayar da wuta tuni jijiyoyin kanshi suka taso,
yayinda jijiyar kan goshinsa tayi ziwat har kan tsinin karan hancinsa a fili zaka gane zallan b'acin rai, gaba d'aya jikinshi tsuma yakeyi,
ido ya zubawa fuskarta kana itama ido ta zuba mishi cikin rauni da muryar kuka tace.
"Wlh ban saniba bada gaggan na buga mishi motarshi ba hankalina ya tafi wurin kallon wani ne."
lips enshi na k'asa ya taune da k'arfi tamkar zai hudashi,
kana ya kama hannunta tare da yi mata nuni data shiga motarta,
cikin rawan jiki ta nufi gefen direban,
hannunta ya kamo da sauri, juyowa tayi tana kallonshi itama kai ya jujjuya mata alamar a a kana ya nuna mata gefen mai zaman banza,
ba musu ta zagaya ta shiga ta zauna.
Shi kuwa gefen driving sit ya shiga ya zauna,
sit bell yaja ya sank'ala jikinshi,
kana ya juyo ya kalleta tare da yi mata alamu da idonshi tasa nata sit bell d'in.
ba musu ta saka,
sai ta kuma d'ago kanta da sauri jin ya dannawa motar Key kana ya figi motar a guje,
ido ta zazzaro ganin yadda yake tsula gudu tamkar zai tashi sama,
gudu yakeyi da tsanani amman cikin bin k'a'ida da dokar tuk'i cikin abinda bai gaza 5 minutes ba ya cimma motocin su Dalla, yayinda su kuwa tuni sun mik'a hanyar data ratsa bakin kasuwa zata kuma wuce zata bi ta kaisu fantami daga nan su ratsa bayan gidan goje,
binsu yakeyi kib da kib haka yasa suka gane binsu akeyi,
tuni kuma an fara kiraye-kirayen sallan mangrib,
murmushin mugunta Dalla yayi kana ya juya akalar motarshi ya shiga cikin sitadiyon ,
shima binsu yayi a baya kusan a tare sukayi parking.
cikin azama da zafin nama ya bud'e ya fito kana ya zagoyo inda take ya bud'e mata tare da kamo hannunta ya juyo ya nufi inda motar Dalla take,
shima Dalla wurinsu ya nufa,
a tsakiyar sitadiyon d'in sukayi kicibus,
cikin wani yanayi mai wuyar fassarawa Saifuddeen yayiwa Dalla alama da hannu akan ya bata hak'uri.
cikin izaya da tak'ama Dalla ya gyara tsayuwanshi tare da cewa.
"Baka da bakine ko iskanci ne zaka zo kana min mgnar kurame?."
cikin tsuke fuska Saifuddeen ya kuma yimishi alamu daya bata hak'uri, ganin haka Dalla ya kuma motsotsu kana yace.
"OK kyautarta ka kawo min kenan?, baka san waye Dalla bako? shiyasa ka biyoni da mace kana nufin in bata hak'uri ne ko?."
cikin sauri da jin dad'in Dalla ya fahimci abinda yake nufi ya tsare fuska kana ya gyad'a mishi kai alamar eh ka bata hak'uri.
wani fatsik'in murmushi Dalla yayi tare da lashe manyan lip's enshi yace.
"Hmmm aini Dalla bana bada hak'uri sai dai in bata ciki tunda ka biyoni da ita, gata kuma zata iya kashe kishin dake addabata wunin yau gaba d'aya ban hutaba kaga yanzu na samu wurin hutawa gashi tanada lafiyayyun kayan marmari a jikinta, yanzu zan mata inkiyata Dalla-dalla da budurcinta zan rab'i jikinta."
Ya k'arishe mgnar tare da kai hannunshi kan k'irjinta.
Wani irin wawan ihu da kururuwa Dalla ya kurma jin wani irin damk'a da Saifuddeen yayiwa hannunshi ba tare da ya samu ya isar da hannun nashi kan k'irjintan ba,
ihu Dalla ya kuma kurmawa jin Saifuddeen ya kuma murd'a mishi hannunshi har saida ya bada sautin b'as alamun ya k'arya mishi hannun, ihun daya sane yasa tarin zugan matasan dake cikin sauran motoci hud'un nan duk suka fito,
wando gaba d'ayansu 'yan kalarene domin duk kansu da makamai a hannunsu wasu da sanduna wasu da kataki wasuma da wuk'ak'e.
A guje suka nufin inda suke, shi kuwa Saifuddeen ko kad'an bai karaya da ganinsu ba,
asalima zagewa yayi ya fara dukan Dalla tamkar Allah ne ya aikoshi,
kunsan fad'an kurma babu sauk'i shiyasa basa tsokana basa tada husuma sabida sun san zuk'atansu basa iya jurar suga ana raini ko zalumci bare fajirci.
sam Dalla ya gaza bawa kanshi kariya,
shiko Saifuddeen dukan ƙaton gargadi yakewa Dalla tare da dandatseshi ta yadda bazai sake sha'awar wata d'iya maceba a duniyar nan har gaban abadan, ita kuwa Zaleeha ganin yadda suka nufo kansu haik'an k'adaran ne yasata sakin ihu tare da bubuga tsalle tanayi tana yarfa hannu tana cewa.
"Zomu gudu zasuyi maka illa zasu kasheka fa,
kazoo mugudu karsu isomu zasu illata ka."
ganin sam bai sararawa Dallanba yasa tayi sauri ta shiga tsakanin su kana ta rik'o hannayenshi tare da kallon fuskarshi tace.
"Mu gudu zafa su kashemu."
ido ya d'ago ya kalleta yadda jikinta ke rawa tamkar mazari tsoro da firgici k'arara a idanunta da ka ganta kasan cikekkiyar matsoraciya mai lasisi ce, haka yasa ya kamo hannunta kana ya juya da ita inda motarta take,
su kuwa zugan 'yan kalaren nan kansu suka nufo a guje ganin hakane yasa,
yajata da k'arfi sannan ya bud'emata motartata wurin zaman direba ya ajiyeta kana ya meda marfin ya rufe sannan ya sunkuyo kanta tare da kad'a mata yatsunshi biyu kana yayi mata alama dataja motar ta gudu, gane abinda yake nufine yasa ta jujjuya kai tare da zubda hawaye cikin haki tace.
"Mutafi zasu kasheka fa 'yan kalarene fa yaranshi ne."
ganin zata b'ata lokaci har suzo su sameta suyi mata illane yasashi buga marfin motar da k'arfi tare dayi mata gurnani irin nasu na kurame wanda in bawai ka saniba sai kayi zaton tsawa ya buga mata hakance ta kasance ga Zaleeha dan jin sautinshi tayi a sama haka yasa ta figi motarta a guje, tana jan motar suna isowa inda yake, yayinda shi kuwa yake kallonta so yake yaga fitanta a wurin, su kuwa suna isa inda yake ba tare da ya juyoba don shi dai kurmane bazaiji sautin takun k'afafunsu ba,
suna isa d'aya daga cikinsu ya narka mishi k'aton katakon dake hannunshi a tsakiyar gadon bayanshi kafin, yayi wani yunk'urinma
d'aya daga cikinsune ya dab'a mishi wuk'a a tsakiyar bayanshi kana ya zaro wuk'ar wanda tuni sun farka mishi rigarshi
wani irin razanennen ihu Zaleeha tasaka tare da zubawa bayanshi ido sabida tana ganinshi ras dan hasken motoci dake haska wurin da hasken fitulun dake zagaye da farfajiyar wurin
cikin tsananin tsoro da firgici taja motarta ta bar sitadiyon d'in,
tana fita kai tsaye gombe division ta nufa.
Shi kuwa Saifuddin tuni sun mishi illa sun daddatsa mishi kataki a tsakiyan bayanshi.
yayinda duk da haka bai bar kare kanshiba sai dai ance sarkin yawa yafi sarkin k'arfi gashi sun zomishi ta bayanshi kuma sunzo tare da makamai yayinda shi kuwa babu ko allura a jikinshi,
haka yasa sukayi mishi illah mafi muni a jikin d'an adam, haka suka rink'a hankad'ashi kan k'arafun wurin suna buga bayanshi a kai
saida sukaga yabar motsi kana suka dauki uban gidansu da Saifuddeen ya daddaga mishi jelershi sukaja motocinsu suka tafi,
yayinda tuni mazauna wurin kuwa sun watse don kowa yasan rashin mutuncin Dalla.
Shiru cikin sitadiyon d'in ba ko tsuntsu sai Saifuddin dake yashe tamkar mamaci,.
Ita kuwa Zaleeha bayan ta sanarwa hukuma, ganin ita macece kuma sananniya kana yar babban Malamin da akeji dashi a fad'in jihar dama k'asar bak'i d'aya yasa aka had'ata da police officer d'aya ya rakata gidansu dake New G.R.A...
A haka police officers na station d'in gombe division suka iso,
yayinda aka had'a da sosojin Anty kalare,
kana
suna isowa ganin halin da yake ciki ne yasa suka d'aukeshi,
kai tsaye general hospital Gombe suka nufa dashi, kai tsaye aka wuce dashi o,p,d. suna isa ma aikatan wannan sashin suka turo irin yan wannan gadaje na d'aukar marasa lfy,
tare dasa hannun hukuma aka karb'eshi bayan an duddubashi ganin aikin babbane ya kuma ji rauni sosai ne sai aka basu takarda wacce zata sadasu da babban likitan dake Medical Center.