Sashe 27
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Shi kuwa Saifuddeen a Gombe ganin lokacin sallan isha yayi ne yasa suka fita sukaje masallaci akayi sallan isha rashin samun labarin ganin wata yasa akayi asham d'inma.
Bayan an idar ne sun dawo gida suka shiga parlourn Baban Ishaq zaune suka sameshi yana kallon tv, ganinsu yasa ya maida hankalin shi a kansu,
cikin nitsuwa suka gaida su nan yayi musu bayanin k'ungiyar su ta nakasassu da yake son su shiga wato (Jonapwd), sosai ya musu bayani ya k'ara da ce musu.
"Shi abu na taron jama'a yanada amfani da fa'ida domin hannu d'aya baya d'aga jinka,
shiga k'ungiyar yanada amfani domin tamkar taimakekeniyace a gareku dan saida had'in kanku zai zama maganarku zatayi tasiri wa kunnuwan jama'an gari dama gwamnati,
saida had'in kan k'ungiya da zaku samu damar yak'an barace da k'arfafawa mutanenku guiwa ta yadda zaku fahimtar dasu Nakasa ba kasawa bace."
Cikin gamsuwa suka gyad'a kai dan shi Saifuddeen yana gane abinda Baba yake fad'a da matsin bakinshi shi kuwa Ishaq yana jinshi, ganin sun gamsune yasashi ci gaba da cewa.
"Dama naje nayi mgna da shugaban k'ungiyar na mishi bayaninku, kuma na shaida mishi in anyi salla lfy zan kaiku."
still kansu suka gyad'a cikin alamun amincewa,
daga nan yayi musu nasiha da basu k'arfin guiwa daga bisani Saifuddeen yace zai tafi,
nan ya mishi addu'an komawa lfy,
shi kuwa ishaq ya rakashi parlour Mama ya d'auki kayanshi sannan ya rakashi har woje saida ya hau machine yaja ya tafi sannan ya koma cikin gida.
Shi kuwa Saifuddeen yana isa kasuwa ya had'a kayanshi duka sannan ya dawo bakin kasuwa inda yasan Salisu zaizo ya d'aukeshi,
bai jima da zuwaba kuma Salisu ya iso daga nan suka kama hanyar Dukku.
To a wannan shekaran dai azumi talatin akayi.
Ranar salla duk al'ummar musulmai kowa da ko ina ana cikin farin ciki,
duk inda ka gibta ido cikin garin dukku zakaga kowa cikin cikar sura da haiba.
K'arfe tara dai-dai akayi sallan idi,
ana idarwa Saifuddeen da abokanshi da suke cikin shiga iri d'aya suka kama hanyar gida,
kasan cewar sun canza hanyar komawa ne yasa suka fito gab da k'ofansu Saminu,
dan haka nan suka shiga suka gaida iyayen Saminu daga nan suka shiga parlour Hajja Mama mahaifiyar Saminu,
inda k'anwarshi Sakina tayi ta jero musu abin ci da sha,
nan suka zauna suka d'anci,
suna fitowa gidansu Saminu suka wuce gidansu Warisu.
Dalinshi tana ganinsu tai ta farin ciki tare da sa musu al'barka nan ta kawo musu fura da nono, sunsha nonon sosai daga nan suka fito suka shiga gidansu Mudassir nan suka samu ya Adnan ya dawo jiya da dare,
yana ganinsu yace.
"Iye Umma zo ki ga 'yan samarinku, wlh yarannan sun girma sosai fa kalli duk sun kusa kamoni tsawo fa."
Bud'a kafad'u sukayi tare da had'a baki sukace.
"Kai Ya Adnan mun kamo ka dai kawai zaka ce."
Umma dai sai murmushi takeyi,
shi kuwa Adnan kamo hannun Saifuddeen yayi tare da cewa.
"Duk baku da kunya Saifuddeen ya fiku mutunci, dan ku gani kuke kunma fini."
sai ya kuma kalli Ahmad dake tsare fuska cikin raha yace.
"Kai Ahmad me na had'e fuska haka?."
tab'e baki yayi tare da cewa.
"Au ashe dai baka mance niba ai wlh ya Adnan baka da kirki, kullum Dada sai tayi cekiyarka in taga Mudassir tace wato kai kam tunda Ya Nuruddeen ya rasu ka yanke zumuncin dake tsakani."
da sauri ya juyo ya kalli Ummanshi dake cewa.
Ai wlh shi Adnan sam baida k'afa dama Nuru shike sashi ziyara,
kullum in yazo sai nayi ta binshi yaje amman sai ya zama ko fitan baya so."
da sauri ya katsesu tare da cewa.
"Kinga ko Umma wlh yanzuma niyata shabewa zan tafi dan wlh nima kaina nayi kewan goggo Dada tun rasuwar Abba ban kuma ganintaba."
shi dai Saifuddeen baibi ta kansuba,
shiko Ya Adnan bayan sun shiga d'akin Umma ne shi kuma ya fita.
Kai tsaye gidansu Saifuddeen ya nufa,
yana shiga ya samu Ummi a tsakar gida cikin shiga ta salla,
tana ganinshi ta fad'ad'a fara'arta cikin jin dad'i tace.
"Lale marhabin da Ya Adnan yaushe a gari mutanen Zaria."
cikin sakin fuska ya zauna bisa taburmar data shimfid'a mishi cikin sakin fuska yace.
"Jiya da dare ne Ummi shiyasa ban shigoba."
gyara zama tayi tare da cewa.
"Ayyah sannu da hanya."
"Yauwa sannu Ummi ya gida yasu Saifuddeen ina auta Hayatuddeen."
juyawa ta d'anyi ta kalli k'ofar d'akin Rahma cikin d'an d'aga murya tace.
"Auta ga Ya Adnan d'inku."
jin haka yasa Hayatuddeen fitowa da sauri,
ita kuwa Ummi juyawa tayi ta kalli Adnan tare da cewa.
"Yanzu ya dawo idi shida Faruq to wai zai tafi shabewa wurin Goggo Dada da yake Adam da Raliya suna can shiyasa suketa d'okin zasu tafi can."
shi kuwa Hayatuddeen yana zuwa ya ruggumi Adnan yayinda Faruq ke bayanshi da sauri ya iso ganin Adnan na mik'o mishi hannu ruggumesu yayi baki d'aya yana jin tausayin yaran da k'aunarsu yana tuno irin so da k'aunar da Nuruddeen ke musu.
ita kuwa Ummi cikin sanyin sautin da ganin Adnan ya tuna mata d'anta ta kalli Rahma da yanzu ta fito ganin Adnan ne yasa ta koma cikin d'aki da sauri,
jin muryar Ummi na cewa.
"Rahma fito mana kizo ki kawo mishi abinci."
cikin sanyin murya tace.
"To Ummi bari insa hijabi."
daga nan sukaci gaba da hira,
cikin kula Ummi tace.
"Ya karatu yanzu kam ka kusa gamawa ko?."
gyara zama yayi tare da cewa.
"Alhamdulillahi Ummi ai nama gama."
cikin jin dad'i tace.
"Alhamdulillahi nayi farin ciki Allah ya taimaka ya baka aiki cikin sauk'i."
ido ya lumshe ganin Rahma data rutsuna gabanshi,
sai ya kuma kauda kai daga gareta tare da sauk'e numfashi kana ya kalli Ummi tare da cewa.
"Amin Amin Ummi aiki kam ya samu ma da yake karatun likitanci ne samun aikin ba wuya,
next week zan koma gombe dan na samu gurbin aiki a medical senta gombe harma sun bani gidan zama a can a jerin gida jen ma'aikatan su."
Sosai Ummi tayi farin cikin wannan labarin,
daga bisani ta tashi taja hannun Hayatuddeen da Faruq da tace.
"To muje in had'a muku kayanku,
kai Auta baka ganin girmanka sai kayi ta zama jikin mutane."
murmushi yayi tare da zaro kud'in 'yan ishirin-ishirin ya bawa Hayatudden guda goma hakama Faruq aifa nan sukayi ta tsalle suna murna, cikin had'a fuska Rahma tace.
"Baku iya godiya bako?."
da sauri suka juyo tare da cewa.
"Ya Adnan mun gode Allah ya saka ya k'ara bud'i."
Amin Amin yace,
tuni su kuma sunbi bayan Ummi,
shi kuwa Adnan idonshi ya d'an lumshe tare da sa yatsunshi biyu ya d'an ja jelan kitson Rahma dake har bisa kafad'unta,
da sauri ta d'an juyo tare da cewa.
"Wash Allah na ya Adnan zafi."
girarshi d'aya ya d'aga mata tare da cewa.
"Raguwa kawai."
ido ta lumshe da sauri jin yana cewa.
"Kinji na gama karatu har na sama mana aiki,
bakice komaiba."
idon ta ta d'an bud'e tare da cewa.
"Nayi mana addu'a ai ya Adnan."
gyara zamanshi yayi ya kalli gefe ganin Ummi ta fito zata shiga d'akinta cikin yin k'asa da murya yace.
"Kinga sauran burinmu na gaba,
yanzu dai na kusa in baiyana kaina gaban bappa Ali ya aura min ke in rik'e 'yar k'anwata in sata farin ciki."
da sauri ta kuma rufe ido,
shi kuma sai ya d'an d'aga murya tare da cewa.
"Yunwa fa nakeyi bani abinci inci."
hararanshi ta d'anyi sannan ta zuba mishi abincin ganin zai fara cine yasa ta yunk'ura zata tashi,
sai kuma ta koma ta zauna jin ya kamo hijabinta,
dole ta zauna suna d'an hira yana cin abinci.
har saida ya k'oshi sannan yace.
"Nafa yi amarya."
ido ta d'an zaro alamun tambaya,
murmushi yayi tare da cewa.
"Bafa amaryar da za'ake konciya da ita a gadoba machine ne kasia na saya mana."
cikin jin kunya tace.
"Masha Allah, nayi farin ciki."
juyawa yayi ya shiga d'akin Ummi kud'i ya zaro yan d'ari-d'ari rafan dubu uku ya mik'awa Ummi,
amsa tayi tare da sa mishi al'barka ta kuma yi godiya,
daga nan ya fito tare da cewa su Hayatuddeen su fito ya kaisu gidan goggo Dada aifa da murnarsu suka fito,
suna fitowa Raihana kuma dake k'ofan bappa Ali tana taya Aunty Nina kirba fura itama ta fito nan tace zata bisu,
nan take ta shirya suka fita suka nufi shabewa.
Su Saifuddeen kuwa ranan sun zazzagaya gidan yan uwa da abokan arzik'i,
sai bayan sallan magrib suka dawo gidan Ummi inda dama sukace tayi musu miyar kuka da tuwon semo wai sun gaji da cin kayan maik'o,
aifa sukaci sukayi hanik'an,
har sha d'aya na dare Ahmad yace shifa zai koma aiko sukace yasin bazasu rakashi ba,
dole Salisu ne ya maidashi.
Ishaq kuwa ranan wuni yayi yana zura idon ganin Saifuddeen,
yayi ta gwada kiranshi kuma woyar tashi bata shiga,
haka ya hak'ura ya kwanta da niyar gobe da sassafe zai tafi dukku.
Washe gari kuwa Saifuddeen yayi kolliya na gani na fad'a dan zaije gidan Abokan Abbanshi Baba Hamisu kakansu Faruq kenan da kuma Malam Ashiru,
yana gama kimtsawa ya d'auki turare ya feshe jikinshi dashi kayan sunyi matuk'ar mishi kyau shida Hayatuddeen da Ahmad ne wanda Ahmad d'inne ya d'inka musu shi,
yad'in voyel ne mai ruwan madara yadin mai gidan dara-dara, sai surfani bak'i da akayi aikin d'inkin,
sai kuma takalmi bak'i mai ratsin fari da hula zanna bukar bak'i da ratsin farin,
sosai kayan sukayi d'as da jikinshi yayi wani irin mashahurin kyau da korjini.
Bayan an idar ne sun dawo gida suka shiga parlourn Baban Ishaq zaune suka sameshi yana kallon tv, ganinsu yasa ya maida hankalin shi a kansu,
cikin nitsuwa suka gaida su nan yayi musu bayanin k'ungiyar su ta nakasassu da yake son su shiga wato (Jonapwd), sosai ya musu bayani ya k'ara da ce musu.
"Shi abu na taron jama'a yanada amfani da fa'ida domin hannu d'aya baya d'aga jinka,
shiga k'ungiyar yanada amfani domin tamkar taimakekeniyace a gareku dan saida had'in kanku zai zama maganarku zatayi tasiri wa kunnuwan jama'an gari dama gwamnati,
saida had'in kan k'ungiya da zaku samu damar yak'an barace da k'arfafawa mutanenku guiwa ta yadda zaku fahimtar dasu Nakasa ba kasawa bace."
Cikin gamsuwa suka gyad'a kai dan shi Saifuddeen yana gane abinda Baba yake fad'a da matsin bakinshi shi kuwa Ishaq yana jinshi, ganin sun gamsune yasashi ci gaba da cewa.
"Dama naje nayi mgna da shugaban k'ungiyar na mishi bayaninku, kuma na shaida mishi in anyi salla lfy zan kaiku."
still kansu suka gyad'a cikin alamun amincewa,
daga nan yayi musu nasiha da basu k'arfin guiwa daga bisani Saifuddeen yace zai tafi,
nan ya mishi addu'an komawa lfy,
shi kuwa ishaq ya rakashi parlour Mama ya d'auki kayanshi sannan ya rakashi har woje saida ya hau machine yaja ya tafi sannan ya koma cikin gida.
Shi kuwa Saifuddeen yana isa kasuwa ya had'a kayanshi duka sannan ya dawo bakin kasuwa inda yasan Salisu zaizo ya d'aukeshi,
bai jima da zuwaba kuma Salisu ya iso daga nan suka kama hanyar Dukku.
To a wannan shekaran dai azumi talatin akayi.
Ranar salla duk al'ummar musulmai kowa da ko ina ana cikin farin ciki,
duk inda ka gibta ido cikin garin dukku zakaga kowa cikin cikar sura da haiba.
K'arfe tara dai-dai akayi sallan idi,
ana idarwa Saifuddeen da abokanshi da suke cikin shiga iri d'aya suka kama hanyar gida,
kasan cewar sun canza hanyar komawa ne yasa suka fito gab da k'ofansu Saminu,
dan haka nan suka shiga suka gaida iyayen Saminu daga nan suka shiga parlour Hajja Mama mahaifiyar Saminu,
inda k'anwarshi Sakina tayi ta jero musu abin ci da sha,
nan suka zauna suka d'anci,
suna fitowa gidansu Saminu suka wuce gidansu Warisu.
Dalinshi tana ganinsu tai ta farin ciki tare da sa musu al'barka nan ta kawo musu fura da nono, sunsha nonon sosai daga nan suka fito suka shiga gidansu Mudassir nan suka samu ya Adnan ya dawo jiya da dare,
yana ganinsu yace.
"Iye Umma zo ki ga 'yan samarinku, wlh yarannan sun girma sosai fa kalli duk sun kusa kamoni tsawo fa."
Bud'a kafad'u sukayi tare da had'a baki sukace.
"Kai Ya Adnan mun kamo ka dai kawai zaka ce."
Umma dai sai murmushi takeyi,
shi kuwa Adnan kamo hannun Saifuddeen yayi tare da cewa.
"Duk baku da kunya Saifuddeen ya fiku mutunci, dan ku gani kuke kunma fini."
sai ya kuma kalli Ahmad dake tsare fuska cikin raha yace.
"Kai Ahmad me na had'e fuska haka?."
tab'e baki yayi tare da cewa.
"Au ashe dai baka mance niba ai wlh ya Adnan baka da kirki, kullum Dada sai tayi cekiyarka in taga Mudassir tace wato kai kam tunda Ya Nuruddeen ya rasu ka yanke zumuncin dake tsakani."
da sauri ya juyo ya kalli Ummanshi dake cewa.
Ai wlh shi Adnan sam baida k'afa dama Nuru shike sashi ziyara,
kullum in yazo sai nayi ta binshi yaje amman sai ya zama ko fitan baya so."
da sauri ya katsesu tare da cewa.
"Kinga ko Umma wlh yanzuma niyata shabewa zan tafi dan wlh nima kaina nayi kewan goggo Dada tun rasuwar Abba ban kuma ganintaba."
shi dai Saifuddeen baibi ta kansuba,
shiko Ya Adnan bayan sun shiga d'akin Umma ne shi kuma ya fita.
Kai tsaye gidansu Saifuddeen ya nufa,
yana shiga ya samu Ummi a tsakar gida cikin shiga ta salla,
tana ganinshi ta fad'ad'a fara'arta cikin jin dad'i tace.
"Lale marhabin da Ya Adnan yaushe a gari mutanen Zaria."
cikin sakin fuska ya zauna bisa taburmar data shimfid'a mishi cikin sakin fuska yace.
"Jiya da dare ne Ummi shiyasa ban shigoba."
gyara zama tayi tare da cewa.
"Ayyah sannu da hanya."
"Yauwa sannu Ummi ya gida yasu Saifuddeen ina auta Hayatuddeen."
juyawa ta d'anyi ta kalli k'ofar d'akin Rahma cikin d'an d'aga murya tace.
"Auta ga Ya Adnan d'inku."
jin haka yasa Hayatuddeen fitowa da sauri,
ita kuwa Ummi juyawa tayi ta kalli Adnan tare da cewa.
"Yanzu ya dawo idi shida Faruq to wai zai tafi shabewa wurin Goggo Dada da yake Adam da Raliya suna can shiyasa suketa d'okin zasu tafi can."
shi kuwa Hayatuddeen yana zuwa ya ruggumi Adnan yayinda Faruq ke bayanshi da sauri ya iso ganin Adnan na mik'o mishi hannu ruggumesu yayi baki d'aya yana jin tausayin yaran da k'aunarsu yana tuno irin so da k'aunar da Nuruddeen ke musu.
ita kuwa Ummi cikin sanyin sautin da ganin Adnan ya tuna mata d'anta ta kalli Rahma da yanzu ta fito ganin Adnan ne yasa ta koma cikin d'aki da sauri,
jin muryar Ummi na cewa.
"Rahma fito mana kizo ki kawo mishi abinci."
cikin sanyin murya tace.
"To Ummi bari insa hijabi."
daga nan sukaci gaba da hira,
cikin kula Ummi tace.
"Ya karatu yanzu kam ka kusa gamawa ko?."
gyara zama yayi tare da cewa.
"Alhamdulillahi Ummi ai nama gama."
cikin jin dad'i tace.
"Alhamdulillahi nayi farin ciki Allah ya taimaka ya baka aiki cikin sauk'i."
ido ya lumshe ganin Rahma data rutsuna gabanshi,
sai ya kuma kauda kai daga gareta tare da sauk'e numfashi kana ya kalli Ummi tare da cewa.
"Amin Amin Ummi aiki kam ya samu ma da yake karatun likitanci ne samun aikin ba wuya,
next week zan koma gombe dan na samu gurbin aiki a medical senta gombe harma sun bani gidan zama a can a jerin gida jen ma'aikatan su."
Sosai Ummi tayi farin cikin wannan labarin,
daga bisani ta tashi taja hannun Hayatuddeen da Faruq da tace.
"To muje in had'a muku kayanku,
kai Auta baka ganin girmanka sai kayi ta zama jikin mutane."
murmushi yayi tare da zaro kud'in 'yan ishirin-ishirin ya bawa Hayatudden guda goma hakama Faruq aifa nan sukayi ta tsalle suna murna, cikin had'a fuska Rahma tace.
"Baku iya godiya bako?."
da sauri suka juyo tare da cewa.
"Ya Adnan mun gode Allah ya saka ya k'ara bud'i."
Amin Amin yace,
tuni su kuma sunbi bayan Ummi,
shi kuwa Adnan idonshi ya d'an lumshe tare da sa yatsunshi biyu ya d'an ja jelan kitson Rahma dake har bisa kafad'unta,
da sauri ta d'an juyo tare da cewa.
"Wash Allah na ya Adnan zafi."
girarshi d'aya ya d'aga mata tare da cewa.
"Raguwa kawai."
ido ta lumshe da sauri jin yana cewa.
"Kinji na gama karatu har na sama mana aiki,
bakice komaiba."
idon ta ta d'an bud'e tare da cewa.
"Nayi mana addu'a ai ya Adnan."
gyara zamanshi yayi ya kalli gefe ganin Ummi ta fito zata shiga d'akinta cikin yin k'asa da murya yace.
"Kinga sauran burinmu na gaba,
yanzu dai na kusa in baiyana kaina gaban bappa Ali ya aura min ke in rik'e 'yar k'anwata in sata farin ciki."
da sauri ta kuma rufe ido,
shi kuma sai ya d'an d'aga murya tare da cewa.
"Yunwa fa nakeyi bani abinci inci."
hararanshi ta d'anyi sannan ta zuba mishi abincin ganin zai fara cine yasa ta yunk'ura zata tashi,
sai kuma ta koma ta zauna jin ya kamo hijabinta,
dole ta zauna suna d'an hira yana cin abinci.
har saida ya k'oshi sannan yace.
"Nafa yi amarya."
ido ta d'an zaro alamun tambaya,
murmushi yayi tare da cewa.
"Bafa amaryar da za'ake konciya da ita a gadoba machine ne kasia na saya mana."
cikin jin kunya tace.
"Masha Allah, nayi farin ciki."
juyawa yayi ya shiga d'akin Ummi kud'i ya zaro yan d'ari-d'ari rafan dubu uku ya mik'awa Ummi,
amsa tayi tare da sa mishi al'barka ta kuma yi godiya,
daga nan ya fito tare da cewa su Hayatuddeen su fito ya kaisu gidan goggo Dada aifa da murnarsu suka fito,
suna fitowa Raihana kuma dake k'ofan bappa Ali tana taya Aunty Nina kirba fura itama ta fito nan tace zata bisu,
nan take ta shirya suka fita suka nufi shabewa.
Su Saifuddeen kuwa ranan sun zazzagaya gidan yan uwa da abokan arzik'i,
sai bayan sallan magrib suka dawo gidan Ummi inda dama sukace tayi musu miyar kuka da tuwon semo wai sun gaji da cin kayan maik'o,
aifa sukaci sukayi hanik'an,
har sha d'aya na dare Ahmad yace shifa zai koma aiko sukace yasin bazasu rakashi ba,
dole Salisu ne ya maidashi.
Ishaq kuwa ranan wuni yayi yana zura idon ganin Saifuddeen,
yayi ta gwada kiranshi kuma woyar tashi bata shiga,
haka ya hak'ura ya kwanta da niyar gobe da sassafe zai tafi dukku.
Washe gari kuwa Saifuddeen yayi kolliya na gani na fad'a dan zaije gidan Abokan Abbanshi Baba Hamisu kakansu Faruq kenan da kuma Malam Ashiru,
yana gama kimtsawa ya d'auki turare ya feshe jikinshi dashi kayan sunyi matuk'ar mishi kyau shida Hayatuddeen da Ahmad ne wanda Ahmad d'inne ya d'inka musu shi,
yad'in voyel ne mai ruwan madara yadin mai gidan dara-dara, sai surfani bak'i da akayi aikin d'inkin,
sai kuma takalmi bak'i mai ratsin fari da hula zanna bukar bak'i da ratsin farin,
sosai kayan sukayi d'as da jikinshi yayi wani irin mashahurin kyau da korjini.