← Book details Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 60 OF 116

Sashe 60

Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Zaleeha da Ya Ahmad d'inta da Mamy da Mama dasu Habu wanda yayan Zaleeha ne kana sai maryam yayar Zaleeha wacce tazo da mijinta Aminu wanda d'an bappansu ne yayan Baba malam, duk sun nitsu sunyi shiru,
shi kuwa Baba malam cikin cikar haiba da dottaku da nitsuwa da kamala irinta manyan mutane wadanda suka wadatu da ilimin addini, ya fara yi musu addu'a kana yayi musu nasiha mai ratsa jiki sannan ya d'aura da cewa.
"Alhamdulillahi duk kunsan sanadin zamannan namu tunda kukaga mun zauna zaman jiran Zaleeha."
gyad'a kai sukayi baki d'aya sai Aminu wanda da ka ganshi kasan irin mutanen nanne masu zafi da tsauri fuskarnan tashi tana had'e sai harara yake cillawa Zaleeha k'anwarshi d'iyar Bappanshi k'anin mahaifinshi wanda suke uwa d'aya uba d'aya, kana k'anwar salihar matarshi Maryam.
Ya Ahmad kuwa tonk'oshe kafafu yayi cikin tsanin girmamawa yace.
"Na'am". Alamun suna jiran umarni ko shawara daga mahaufin nasu.
Shi kuwa Baba Malam, Malam Bashir Sulaiman Dukku kenan,
gyara zama yayi tare da cewa.
"Dama ta k'arshe zan baiwa Zaleeha wanda zan ninka mata da damar dana bata, wata shida baya, nace ta fito da gwoninta, na bata dama tayi zab'inta duk da shariya ta bani dama in zab'a mata mijin danaga ya dace a matsayinta na budurwa ni kuwa mahaifinta,
to amman na bata dama zan kuma k'ara bata dama na k'arshe kada ita da mahaifiyarta suyi zaton bani basu hak'k'insu,."
sai kuma ya tsagaita kana ya kalli Mamansu Zaleeha wacce fuskarta ke had'e kauda kai yayi tare da cewa.
"Halima ki shawarci d'iyarki data fidda goninta cikin masu sonta,
nanda tsawon shekara guda,
na bata wannan damarne sabida ina sane da k'orafin da kikayi tayi a auren Maryam cewa nayiwa yarki auren dole kika rink'a zugata data bijirewa zabin da ni nayi mata,
sai nayi dacen Maryam salihace muminace mai biyeyya a gareni, tabi zabina ta watsar da mummunar shawarar da kike bata ta ruggume aurenta tayi biyeyya ga mijinta d'an uwanta."
sai ya kuma kalli Maryam wacce yasan duk yayanshi daga Ahmad sai ita basa son duk wani abu da zai bata mishi rai bare ya zubda mutuncinsa.
Cikin taushin lafazi yace.
"Allah ya miki Al'barka Maryama ubangiji ya sa yaranki su miki biyayya fiye da yadda kikayi min, Allah ya saka miki da jannatul firdausi."
"Amin Amin ya rabbil izzati ngd Baba Malam Allah ya kara nisan kwana".
Cewar Maryam kana duk parlour suka amsa da Amin,
Ita kuwa Mama sai k'ara had'e fuska tayi,
itako Zaleeha sai k'ara sunkuyar da kanta ta kumayi,
gyaran murya Baba malam ya kumayi sannan yaci gaba da cewa.
"Zaleeha ki fito da zab'inki cikin watanni goma sha biyun nan, ki fara lissafi tun daga yau d'in nan yanzun nan kuma,
kinga dai a baya na baki wata shida, shiru baki fidda mijiba,
to ki sani muddin kika cika wa'adin da na baki baki fidda mijiba,
toh zab'i ya dawo gareni, duk wanda naga dama shi zan aura miki, domin nasan,
baki rasa ma nemaba, amman kinyi burus da zancen,
kinasa ana nunani in na wuce ana cewa shine babanta, ai yar malami ne,
wasu na tuhumar to meyasa ban aurar dake ba,
na barki kinata gallafiri a gari sai kije gidan radio kiyi ta zuba kid'e-kid'e kina waƙe-waƙe kamar zabiya,
to na baki shekara guda."
cikin jin dad'i Zaleeha ta gyada kai dan ita a ganinta ai bata da matsala shekara guda aka bata so sai takega ai lokacin da tsawo lokacin ya isheta ta nemo inda yake tasan halin da yake ciki ta bashi tukuicin aurenta bisa kareta da yayi ya zame mata Garkuwa ya saida ranshi a kanta, to me take dashi da zata bashi a duniya in banda kanta ta hanyar haure tayi mishi biyayya ta faranta mushi ta haskaka mishi dararen rayuwarsu.
Aminu kuwa tsawa ya daka mata tare da cewa.
"Baki da bakin amsawa ne sai mgna da kai?."
cikin tsoronshi tace.
"Na amsa fa Ya Aminu."
tsaki ya d'anja kana yace. "Wallahi Allah kenan, kada kiyi kuka da kowa kiyi kuka da kanki in har kika bari akaje matakin da Baba Malam zai miki zabi, kin sani muddin yace eh to eh d'ince har gaban abadan in kuma yace a a to a ance, dana gaba ake gane zurfin ruwa kin daiga Maryam gata a gidane tana kuma da yara har biyu dan haka kada kiyi wasa da damarki ki fito da zabinki in kin tsaida goni dai babu mai miki dole."
cikin sanyi tace.
"To ngd Ya Aminu."
sai ta kuma kalli Mahaifin nasu cikin sanyi da tsantsar biyayya tace.
"Ngd Baba Malam Allah ya k'ara girma, ya jik'a magabata."
"Amin Amin Allah ya muku al'barka ya tsareku da sharrin shaid'an da fitinar zamani."
ya fad'i yana gyara zamanshi, domin yana jin dad'in addu'ar da yaranshi kewa iyayenshi haka yana nuna mishin koda bayan ranshi zasu kasance mishi al'waladul saliha.
Ita kuwa Zaleeha
sai ta kuma kalli Ya Habu tare da cewa.
"Ya Habu ga car Key inka."
amsa yayi yana hararanta kana yace.
"Ni naso ace wata biyu za'a bata ai."
hannu Baban nasu ya d'aga mishi kana yace.
"Aminu yi mana addu'a."
Addu'a yayi musu kana suka tashi daga taron.

ita da Mamanta suka wuce side din Maman,
Maryam kuma tabi bayan Mamy,
kana Aminu da Ahmad kuwa, suna zaune gaban Baba Malam suna tattauna kan lamarin Zaleehan,
ganin mangrib ta gabato yasa sukayi al'wala suka nufi masallacin dake cikin gidan nasu.
A falo suka samu d'an wani matashi wanda bazai wuce sa'an Hayatuddeen ba,
yana ganin Zaleeha yazo gabanta tare da cewa.
"Dan Allah Zaleeha sammin motarki mana."
hararanshi tayi tare da cewa,
"Lallai kam Zakariyya ni zan baka motata wacce nima ko hawanta banba kai ko key d'intama Ya Ahmad bai banba nima yau da ta Ya Habu naje wurin aiki, yanzune dana dawo ne naga motar a parking lot."
harara ya watsa mata cikin tsama irinta sak'o da sak'o yace.
"Kada Allah yasa ki bada, kawai dan na tambayeki sai kita min ihu a kai."
cikin huce haushinta a kanshi tace.
"Ni zaka cewa ina maka ihu a kai ni mahaukaciyace da zan maka ihu."
Gwalo ya mata tare da cewa..
"To da banne? Ba gashiba daga mgna kin fara zubda ƙolla."
juyawa tayi ta kalli Mamansu data zuba musu ido tana dariya dan yanzu in ta shiga zasu nuna mata itace bare inda sabo kowa yasan Zaleeha da Zakariyya, shida hatta abo kanshi sun medata abokiyar wasansu.
ganin Maman tana murmushi yasa tace.
"Mama kina jinshi yana cemin mahaukaciya, kuma kina dariya."
cikin muryar rashin fara'a tace.
"Kunfi kusa."
shi kuwa Zakariyya dariya yayi tare da cewa.
"Ni barima in koma."
zama tayi bisa stull din dake tsakiyar falon kana tace.
"Da yafi maka kam, d'an ci rani kawai, gwara ka koma can wurin tsohuwar nan data sakaltaka kuyu fama da wannan tsukekken anguwar taku dake saman dutse."
zama yayi kusa da ita tare da cewa.
"Tab kaji yarinya nida gidanmu harda cemin d'an cin rani, toma na fasa tafiya."
murmushi tayi tare da share hawayenta dake zuba duk sanda ta tunoshi kai ta sunkuyar kana tace,
"Rainon kaka kawai".
Oho dai na fiki shanawa Baba malam yana ji dani tunda na girma gaban tsohuwarshi bakiji har cewa yake nine zan samu irin tarbiyarshi."
cewar Zakariyya,
ita kuwa Zaleeha wayarta ta duba tare da cewa.
"Rainon sakalci ba, naga hatta abo kanka sakalallune."
dariya yayi kana yace.
"Oho dai na yarda ni goyon kakane, inje ƙasar da nakeso da ƴar tsohuwata."
baki ta tabe kana tace.
"Yaro kai ke jiran wani ya biya maka ni in naga dama al'bashi na zai kaini ."
murmushi tayi tare da cewa.
"Daga baya Keenan."
Gefenta ya zauna kana yace.
"Yauwa Adda Zaleeha kin tuna wannan abokin nawa Hayatuddeen wanda kwanaki kuka had'u a gidan kaka yaje wurina?."
jim ta d'anyi kana tace.
"Yes na tunashi wani kekyawan yaro shima sakali irinka."
da sauri yace .
"Eh shi dai."
aje wayarta tayi tare da cewa.
"Har yace min shine d'an auta a gidansu shiyasa akeji dashi."
Cikin sauri Zakariyya yace. "Yesss kin gane."
sai ya kuma yayi kalar tausayi tare da cewa.
"Ayyah to shine nakeso inje gidansu.
Yayanshi ba lfy, suna Abuja yace ba mmki ma su wuce India,
to shine zanje in gaida wata yayarshi Raliyya irinki."
cikin sanyi tace.
"Ayyah Allah ya bashi lfy, kaje wurin.
Ya Ahmad ka amshi Key din."
tsalle yayi tare da manna mata kiss a goshinta tare da cewa.
"Yesss my lovely Aunty faratu."
ajiyan zuciya tai kana tace.
"Yayi kyau dan na bakane zaka cemin faratu ko?."
bazan sakeba yace yana mai fita,
da sauri tabi bayanshi kana tace.
"Yauwa Zakariyya ga kud'i in kana dawowa dan Allah ka saya min feesh roll."
ba musu ya amshi kudin kana yaje ya amshi key din sannan ya tafi.

Ita kuwa saida ta wasa ruwa sannan ta nufi side d'in Mamy inda ta samu Ya Ahmad da Maryam suna cin abinci.
Gefen Maryam ta zauna tare da cewa.
"Ya tafi ko?." Ahmad ne ya d'an kalleta tare da cewa.
"Waye d'in?."
jujjuya kai ta d'anyi tare da lek'a hanyar shiga sannan tace.
"Wannan masifeffen mijin nata mana. Shi komai in ansa dashi sai ya zak'e ya rink'a rabka over acting."
tab'e baki Maryam tayi kana tace.
"Kamar a kunnenshi kika fad'i yaseen zan fad'a mishi."
ido ta zazzaro tare da cewa.
"Dan Allah rufa min asiri, wannan saggamin yanzu zaice zai gwada gwanjinshi a kaina."
dariya sukayi sannan daga bisani Ahmad da Maryam sukayi ta bata shawarar kadafa ta bari ta k'ure Baba malam,
suna nan sunata hira Zakariyya ya dawo nan akaci gaba da hira tare dashi, sai dai sam Zaleeha bata tare dasu har Ahmad ya fahimci hakan , so sai ya danganta abin da ko mgnar auren da akayi matane,
sai daga baya Maryam ta mik'e ta tafi side d'in mamansu nan suka d'an tab'a hira kana, suka fito dan tafiya gidan ganin Ahmad ya fito zai maida Zakariyya gidan kakar tasu da yake shi tun yaye yake hannunta,
ganin dare ya d'anyi ne yasa Aminu cewa, Ahmad ya bari zasu biya su sauk'i Zakariyyan.

***
Asalin ahlin Zaleeha.
Chapter 60 · 0% Book details