Sashe 41
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A bakin gate suka d'an tsaya wurin Baba buzu,
cikin yanayin sun fara sabawa dashi sukace.
"Baba bari muje gidansu Zakariyya."
murmushi yayi tare da cewa.
"Auho kuce wanda yace zai bani kakarshi in aura in inaso ko?."
Cikin shek'iyamci Imran yace.
"Yauwa to ita zumuje dubowa, me zaka kawo mu kai mata?."
goro ya fiddo cikin aljihun rigarshi irin gara ga nakan nan na buzaye,
ya mik'awa Hayatuddeen su tare da cewa.
"To gashi ku kai mata wannan."
aifa dariya suka sa sannan suka amsa suka tafi.
gidansu Isma'il suka biya sannan suka nufi hanyar da zai sadasu da ceceniya kasan cewar ba nisa sosai tsaka ninsu.
Suna isa,
Zakariyya na jin muryarsu ya fito da sauri yana isa inda suke ya basu hannu suka tafa tare yin murmushi suna cikin haka sukaji wata zazzak'ar murya mai dad'in sauraro tana cewa...!
By
*GARKUWAR FULANI*
8/18/20, 7:52 PM - Ummi Tandama: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 12*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
Cikin d'an d'aga murya take cewa.
"Zakariyya! Zakariyya!! Zakariyya!!! wlh bana son raini kazo ka bani wayata."
cikin d'aga murya Zakariyya yace.
"Ank'i a bada d'in uwar masifa k'arfinki ya kwata miki aikin kawai ke ba dama mutun ya tab'a woyarki sai kiyi ta rashin mutunci."
dariya Imran yayi tare da cewa.
"Yaseen yau sai mun zuk'e cajinki."
dai-dai lokacin ta fito daga ganinta yayar Zakariyya ne dan suna d'an kama kekyawace ajin forko tanada cikar sura,
idanu ta zubawa Hayatuddeen da yake kallonta tare da cewa.
"Wannan itama irin Raliya ce ko sai hegen masifa."
Zakariyya ne yayi dariya tare da cewa.
"Haka suke dan sun samu sun fimu da sharu uku zuwa hud'u kacal sai sukeji kamar sune suka haifemu."
da sauri ta iso ta wabce wayarta dake hannun Imran kana tace.
"Hegu kawai masu jajayen fuskoki."
cikin tsiya Zakariyya yace.
"Shima samune kina bak'in cikin jar fatanmu."
tsaki taja tare da cewa.
"Hauka kawai me abin jin haushi duk kunyi kalar zabiya kuma dai baku fini fari ba."
dariya Imran yayi sannan yace.
"Ke dai dama kina bak'in ciki ace Zakariyya ya fiki kyau."
juyawa tayi tana cewa.
"A ina ka tab'a ganin namiji yafi macce kyau."
cikin sauri Hayatuddeen yasha gabanta tare da cewa.
"Yaseen na miji nafin mace kyau kin ganki duk da kyanki Hamma Saifuddeen d'ina ya fiki kyau, in kin ganshi keda kanki zaki shaida hakan."
bata bi ta kansuba ta shiga cikin parlour inda kakarsu ke kwance tanata raki,
bayanta sukabi da saurinsu suna shiga suka gaida Kaka sannan suka zauna gefen ta. Cikin kula tace.
"Imarana ya gida?."
ba tare da ya juyo ya kalletaba yace.
"Lfy lau Alhamdulillahi Mama tace in gaidaki da jiki."
"Ina amsawa." ta bashi amsa tare da juyawa tana kallon Hayatuddeen da yake nunawa Zakariyya abu a wayarshi tace.
"Kai Hayatu hankalin ka duk yana kan waya, Umminka tana lfy ko."
still idanunshi na kan wayar yace.
"Nace miki ki dena cemin Hayatu, ki cika min sunana Hayatuddeen ko kuma kice min Deen in kuwa Hayatun kike son fad'i to kice Hayat."
dariya budurwannan tayi ganin yadda Tsohuwar taketa buga mishi harara,
Isma'il ma da babu bakin mgna sai murmushi yakeyi
Imran ma dariyar yayi dan da yaji dariyar Budurwar ne yasashi kallon inda take kallo,
d'ago kansu sukayi suma suka kallesu jin dariyar tayi yawa,
Zakariyya ne ya kad'a baki yace.
"Haba dai Inna ai wannan kallo sai ya razanamu, dan Allah ki rage idanunki."
sai ya kuma kalli yayar tashi cikin tsigar tsokana yace.
"Ke ashe ga wacca ta b'ataki da k'uru-k'urun idanu bamu ankara ba."
jin haka ai yasa ta haiyayak'o kanshi wai ya zageta mai k'uru-k'urun idanu,
ita kuwa Inna baki ta tab'e tare da cewa.
"Wannan dokoki na kiran sunanka ai sai 'yan boko ni ba abinda ya shamin kai Hayatu zan kiraka."
dariya yayi sosai jin Imran na ce mata.
"To inna ba sai mu shigar dake makarantarba mu samu ki haddace sunan ba Dukke."
shi kuwa Zakariyya sanin bayanshi Inna takebi yasa ya mik'e yana tarfawa yayar tashi tsiya,
ganin Inna tak'i ta kulashi yasa ta sunkuyo ta zari hand bag nata tare da car key d'inta dake gefen jakar cikin jin haushin tace.
"Yaseen bazan zauna a gidan nan ba,
zan koma gida haka kawai a turoni dan inzo in taimaka miki tunda kin gurd'e kuma kina ganin jikanki ya rainani da yake kin fi sonshi bazaki mishi fad'aba."
cikin sababi irin na tsofaffi masu zafi tace.
"Ki tafi mana kada Allah yasa ki zauna dan ubanki! ai bani na kirakiba ni dama Zahira nace a turo min dan itace mai mutunci,
amman tunda kikace bazaki zaunan ba ni kuwa yanzu zan kira Babanku kina komawa zaki dawo kiyi asaran man motarki kawai."
bata bi ta kan magar tsohuwar ba ta fice abinta,
su kuwa duk bayanta sukabi,
suna fitawa tana figin motarta ta tana shirin barin harabar d'an k'aramin gidan,
Hayatuddeen ne yayi sauri d'aga murya tare da cewa.
"Kadafa ki manta kinada tambarin *L* yaseen ki kula kada kije kiyi ta tambola a titi."
k'ura ta bud'esu dashi kana tayi ficewarta daga gidan.
Su kuwa nan sukayi ta sabgoginsu sai gab da magrib suka fito suka nufi gida duk da akwai 'yar tazara tsakaninsu amman haka suke tattakawa da k'afafunsu har zuwa gida a cewarsu Hayatuddeen yaga garin da kyau,
suna isa gab da gidansu Isma'il ne Imran ya tare machine ya tafi,
shi kuwa Hayatuddeen jan hannun isma'il yayi a kan dole sai suje gidansu a dole ya bishi.
Sannu-sannu su Ummi sun saba da bak'otansu da iyayen abokansu Saifuddeen da Hayatuddeen.
Yau jumma'a shiyasa Saifuddeen bai fita da wuriba,
sai h'ar k'arfe tara ya tashi daga baccin daya koma bayan sallan asuba,
a hankali ya mik'e mik'a yayi tare da yin salati a zuciyarshi,
bathroom ya nufa,
wonka yayi mai rai da lfy kana yayi al'wala sannan ya fito d'aure da towel a k'ugunshi sai d'an k'aramin dake hannunshi bisa bakin gado ya zauna ya fara tsane ruwan jikinshi,
mik'ewa ya kumayi bisa kujerar dressing mirror ya zauna mai ya fara shafawa sannan ya gyara suman kanshi,
mik'ewa yayi zuwa gaban durowar bud'ewa yayi ya zaro wani tattausan yadi mai taushi yadin bak'i ne mai shek'i yanada zanen gidan dara-dara,
sai kuma ya zaro boxer and vest farare k'al-k'al,
a bakin gado ya ajiyesu,
sannan ya kuma dawowa gefen durowar inda takalmanshi ke jere bisa wani kekyawan abin aje takalma wasu fararen takalma ya zaro,
sai ya kuma bud'e d'aya sashin na durowar inda hulunanshi ke jere,
hula zanna bukar ya zaro fara mai ratsin bak'i-bak'i,
kimtsawa yayi cikin kayan da ya fidda d'in,
bayan ya gama sawane ya dawo gaban mirror yana dai'daita zaman hularshi a kanshi,
murmushi yayi wanda har saida dimples nashi suka lotsa shida kanshi yasan yana kama da Abbansu,
ya kuma san Abbansu kekyawane na nunawa sa'a sosai bak'in kayan ya k'ara fito da farin fatarshi ras,
in ka ganshi tamkar balarabe suman kanshi a konce lib-lib a k'eyanshi da gefen sajenshi,
turare ya d'auka ya feshe jikinshi dashi lungu da sak'o,
ido ya lumshe a hankali tare da shak'an numfashi dan jin sassanyan k'amshin turaren dake ratsa mishi jiki da zuciya.
Towel d'in daya ciren ne ya d'auka ya shiga bathroom ya
shanyashi sannan ya fito,
ya nufi parlour.
Ummi kuwa da yaranta duk suna parlour suna tab'a hira,
Ummi na bisa 3 str Hayatuddeen kuma na konce kusa da ita yayi !!! kan tv,
da sauri Ummi ta d'ago kanta ido ta zubawa steps d'in sauk'owa k'asan dan jin takun d'an nata,
murmushi tayi tare lumshe ido kana tana godewa Allah daya azurtata da wannan kekyawa halitta a matsayin d'anta cikin sanyin sauti tace.
"Masha Allah, babana yayi kyau matuk'a gaya."
murmushi yayi shima dan idanunshi na kanta a hankali yaci gaba da tako steps d'in cikin takunshi mai d'arka hankali har ya sauk'o,
gabab da ita yazo ya zauna cikin kurma-kurma ya gaidata.
"Lfy lau Babana ka tashi lfy ko?."
hannunta ya kamo ya manna a habarshi alamun lfy lau Alhamdulillahi.
cikin girmamawa Raliya ta kalleshi tare da cewa.
"Ina kwana Hamma Saifuddeen."
kai ya jinjina mata ta lamun lfy lau,
sai ya kuma kallin Hayatuddeen dake kallonshi yana mirmushi cikin k'aunar d'an uwan nashi, murya a sake yace.
"Barka da jumma'a Hamma." bai jira amsarshi ba yaci gaba da cewa.
"Kayi kyau sosai Hamma na."
murmushi yayi kana ya shafa fuskar k'anin nashi.
Ummi kuwa mik'ewa tayi ta nufi dinning table tare da yafitoshi tai mishi alamar yazo yayi breakfast."
mik'ewa yayi yabi bayanta,
Zama yayi a kujerar dake dab da ita yana kallon yadda taken had'a mishi tea,
tana gamawa ta mik'a mishi sannan ta zubo mishi soyayyan dankali da kwai sai kuma ta jawo wani filet d'in da alamun wani abun zata kuma zuba mishi,
da sauri ya jujjuya mata kai,
tare da mata alamun sauri yakeyi tea d'in kawai zaisha da d'ankalin,
sanin halinshi da halittarshi ta rashin cin abinci da yawane yasata meda filet d'in sannan ta zauna gefenshi yana d'anci suna kuma d'an tab'a hira sauri-sauri ya gama ya sallameta ya fita ya tafi.
Ita kuwa Ummi ta haura sama kai tsaye bedroom nashi ta nufa ita da kanta ta gyara mishi d'akinshi da bathroom da parlour nashi duka ta sassake mishi labuye sannan ta feffesa turaren d'aki mai suna touch me sannan ta rege mishi gudun AC kana ta fito.
cikin yanayin sun fara sabawa dashi sukace.
"Baba bari muje gidansu Zakariyya."
murmushi yayi tare da cewa.
"Auho kuce wanda yace zai bani kakarshi in aura in inaso ko?."
Cikin shek'iyamci Imran yace.
"Yauwa to ita zumuje dubowa, me zaka kawo mu kai mata?."
goro ya fiddo cikin aljihun rigarshi irin gara ga nakan nan na buzaye,
ya mik'awa Hayatuddeen su tare da cewa.
"To gashi ku kai mata wannan."
aifa dariya suka sa sannan suka amsa suka tafi.
gidansu Isma'il suka biya sannan suka nufi hanyar da zai sadasu da ceceniya kasan cewar ba nisa sosai tsaka ninsu.
Suna isa,
Zakariyya na jin muryarsu ya fito da sauri yana isa inda suke ya basu hannu suka tafa tare yin murmushi suna cikin haka sukaji wata zazzak'ar murya mai dad'in sauraro tana cewa...!
By
*GARKUWAR FULANI*
8/18/20, 7:52 PM - Ummi Tandama: 📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
*NAKASA BA KASAWA BACE*
*PAGE 12*
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
Cikin d'an d'aga murya take cewa.
"Zakariyya! Zakariyya!! Zakariyya!!! wlh bana son raini kazo ka bani wayata."
cikin d'aga murya Zakariyya yace.
"Ank'i a bada d'in uwar masifa k'arfinki ya kwata miki aikin kawai ke ba dama mutun ya tab'a woyarki sai kiyi ta rashin mutunci."
dariya Imran yayi tare da cewa.
"Yaseen yau sai mun zuk'e cajinki."
dai-dai lokacin ta fito daga ganinta yayar Zakariyya ne dan suna d'an kama kekyawace ajin forko tanada cikar sura,
idanu ta zubawa Hayatuddeen da yake kallonta tare da cewa.
"Wannan itama irin Raliya ce ko sai hegen masifa."
Zakariyya ne yayi dariya tare da cewa.
"Haka suke dan sun samu sun fimu da sharu uku zuwa hud'u kacal sai sukeji kamar sune suka haifemu."
da sauri ta iso ta wabce wayarta dake hannun Imran kana tace.
"Hegu kawai masu jajayen fuskoki."
cikin tsiya Zakariyya yace.
"Shima samune kina bak'in cikin jar fatanmu."
tsaki taja tare da cewa.
"Hauka kawai me abin jin haushi duk kunyi kalar zabiya kuma dai baku fini fari ba."
dariya Imran yayi sannan yace.
"Ke dai dama kina bak'in ciki ace Zakariyya ya fiki kyau."
juyawa tayi tana cewa.
"A ina ka tab'a ganin namiji yafi macce kyau."
cikin sauri Hayatuddeen yasha gabanta tare da cewa.
"Yaseen na miji nafin mace kyau kin ganki duk da kyanki Hamma Saifuddeen d'ina ya fiki kyau, in kin ganshi keda kanki zaki shaida hakan."
bata bi ta kansuba ta shiga cikin parlour inda kakarsu ke kwance tanata raki,
bayanta sukabi da saurinsu suna shiga suka gaida Kaka sannan suka zauna gefen ta. Cikin kula tace.
"Imarana ya gida?."
ba tare da ya juyo ya kalletaba yace.
"Lfy lau Alhamdulillahi Mama tace in gaidaki da jiki."
"Ina amsawa." ta bashi amsa tare da juyawa tana kallon Hayatuddeen da yake nunawa Zakariyya abu a wayarshi tace.
"Kai Hayatu hankalin ka duk yana kan waya, Umminka tana lfy ko."
still idanunshi na kan wayar yace.
"Nace miki ki dena cemin Hayatu, ki cika min sunana Hayatuddeen ko kuma kice min Deen in kuwa Hayatun kike son fad'i to kice Hayat."
dariya budurwannan tayi ganin yadda Tsohuwar taketa buga mishi harara,
Isma'il ma da babu bakin mgna sai murmushi yakeyi
Imran ma dariyar yayi dan da yaji dariyar Budurwar ne yasashi kallon inda take kallo,
d'ago kansu sukayi suma suka kallesu jin dariyar tayi yawa,
Zakariyya ne ya kad'a baki yace.
"Haba dai Inna ai wannan kallo sai ya razanamu, dan Allah ki rage idanunki."
sai ya kuma kalli yayar tashi cikin tsigar tsokana yace.
"Ke ashe ga wacca ta b'ataki da k'uru-k'urun idanu bamu ankara ba."
jin haka ai yasa ta haiyayak'o kanshi wai ya zageta mai k'uru-k'urun idanu,
ita kuwa Inna baki ta tab'e tare da cewa.
"Wannan dokoki na kiran sunanka ai sai 'yan boko ni ba abinda ya shamin kai Hayatu zan kiraka."
dariya yayi sosai jin Imran na ce mata.
"To inna ba sai mu shigar dake makarantarba mu samu ki haddace sunan ba Dukke."
shi kuwa Zakariyya sanin bayanshi Inna takebi yasa ya mik'e yana tarfawa yayar tashi tsiya,
ganin Inna tak'i ta kulashi yasa ta sunkuyo ta zari hand bag nata tare da car key d'inta dake gefen jakar cikin jin haushin tace.
"Yaseen bazan zauna a gidan nan ba,
zan koma gida haka kawai a turoni dan inzo in taimaka miki tunda kin gurd'e kuma kina ganin jikanki ya rainani da yake kin fi sonshi bazaki mishi fad'aba."
cikin sababi irin na tsofaffi masu zafi tace.
"Ki tafi mana kada Allah yasa ki zauna dan ubanki! ai bani na kirakiba ni dama Zahira nace a turo min dan itace mai mutunci,
amman tunda kikace bazaki zaunan ba ni kuwa yanzu zan kira Babanku kina komawa zaki dawo kiyi asaran man motarki kawai."
bata bi ta kan magar tsohuwar ba ta fice abinta,
su kuwa duk bayanta sukabi,
suna fitawa tana figin motarta ta tana shirin barin harabar d'an k'aramin gidan,
Hayatuddeen ne yayi sauri d'aga murya tare da cewa.
"Kadafa ki manta kinada tambarin *L* yaseen ki kula kada kije kiyi ta tambola a titi."
k'ura ta bud'esu dashi kana tayi ficewarta daga gidan.
Su kuwa nan sukayi ta sabgoginsu sai gab da magrib suka fito suka nufi gida duk da akwai 'yar tazara tsakaninsu amman haka suke tattakawa da k'afafunsu har zuwa gida a cewarsu Hayatuddeen yaga garin da kyau,
suna isa gab da gidansu Isma'il ne Imran ya tare machine ya tafi,
shi kuwa Hayatuddeen jan hannun isma'il yayi a kan dole sai suje gidansu a dole ya bishi.
Sannu-sannu su Ummi sun saba da bak'otansu da iyayen abokansu Saifuddeen da Hayatuddeen.
Yau jumma'a shiyasa Saifuddeen bai fita da wuriba,
sai h'ar k'arfe tara ya tashi daga baccin daya koma bayan sallan asuba,
a hankali ya mik'e mik'a yayi tare da yin salati a zuciyarshi,
bathroom ya nufa,
wonka yayi mai rai da lfy kana yayi al'wala sannan ya fito d'aure da towel a k'ugunshi sai d'an k'aramin dake hannunshi bisa bakin gado ya zauna ya fara tsane ruwan jikinshi,
mik'ewa ya kumayi bisa kujerar dressing mirror ya zauna mai ya fara shafawa sannan ya gyara suman kanshi,
mik'ewa yayi zuwa gaban durowar bud'ewa yayi ya zaro wani tattausan yadi mai taushi yadin bak'i ne mai shek'i yanada zanen gidan dara-dara,
sai kuma ya zaro boxer and vest farare k'al-k'al,
a bakin gado ya ajiyesu,
sannan ya kuma dawowa gefen durowar inda takalmanshi ke jere bisa wani kekyawan abin aje takalma wasu fararen takalma ya zaro,
sai ya kuma bud'e d'aya sashin na durowar inda hulunanshi ke jere,
hula zanna bukar ya zaro fara mai ratsin bak'i-bak'i,
kimtsawa yayi cikin kayan da ya fidda d'in,
bayan ya gama sawane ya dawo gaban mirror yana dai'daita zaman hularshi a kanshi,
murmushi yayi wanda har saida dimples nashi suka lotsa shida kanshi yasan yana kama da Abbansu,
ya kuma san Abbansu kekyawane na nunawa sa'a sosai bak'in kayan ya k'ara fito da farin fatarshi ras,
in ka ganshi tamkar balarabe suman kanshi a konce lib-lib a k'eyanshi da gefen sajenshi,
turare ya d'auka ya feshe jikinshi dashi lungu da sak'o,
ido ya lumshe a hankali tare da shak'an numfashi dan jin sassanyan k'amshin turaren dake ratsa mishi jiki da zuciya.
Towel d'in daya ciren ne ya d'auka ya shiga bathroom ya
shanyashi sannan ya fito,
ya nufi parlour.
Ummi kuwa da yaranta duk suna parlour suna tab'a hira,
Ummi na bisa 3 str Hayatuddeen kuma na konce kusa da ita yayi !!! kan tv,
da sauri Ummi ta d'ago kanta ido ta zubawa steps d'in sauk'owa k'asan dan jin takun d'an nata,
murmushi tayi tare lumshe ido kana tana godewa Allah daya azurtata da wannan kekyawa halitta a matsayin d'anta cikin sanyin sauti tace.
"Masha Allah, babana yayi kyau matuk'a gaya."
murmushi yayi shima dan idanunshi na kanta a hankali yaci gaba da tako steps d'in cikin takunshi mai d'arka hankali har ya sauk'o,
gabab da ita yazo ya zauna cikin kurma-kurma ya gaidata.
"Lfy lau Babana ka tashi lfy ko?."
hannunta ya kamo ya manna a habarshi alamun lfy lau Alhamdulillahi.
cikin girmamawa Raliya ta kalleshi tare da cewa.
"Ina kwana Hamma Saifuddeen."
kai ya jinjina mata ta lamun lfy lau,
sai ya kuma kallin Hayatuddeen dake kallonshi yana mirmushi cikin k'aunar d'an uwan nashi, murya a sake yace.
"Barka da jumma'a Hamma." bai jira amsarshi ba yaci gaba da cewa.
"Kayi kyau sosai Hamma na."
murmushi yayi kana ya shafa fuskar k'anin nashi.
Ummi kuwa mik'ewa tayi ta nufi dinning table tare da yafitoshi tai mishi alamar yazo yayi breakfast."
mik'ewa yayi yabi bayanta,
Zama yayi a kujerar dake dab da ita yana kallon yadda taken had'a mishi tea,
tana gamawa ta mik'a mishi sannan ta zubo mishi soyayyan dankali da kwai sai kuma ta jawo wani filet d'in da alamun wani abun zata kuma zuba mishi,
da sauri ya jujjuya mata kai,
tare da mata alamun sauri yakeyi tea d'in kawai zaisha da d'ankalin,
sanin halinshi da halittarshi ta rashin cin abinci da yawane yasata meda filet d'in sannan ta zauna gefenshi yana d'anci suna kuma d'an tab'a hira sauri-sauri ya gama ya sallameta ya fita ya tafi.
Ita kuwa Ummi ta haura sama kai tsaye bedroom nashi ta nufa ita da kanta ta gyara mishi d'akinshi da bathroom da parlour nashi duka ta sassake mishi labuye sannan ta feffesa turaren d'aki mai suna touch me sannan ta rege mishi gudun AC kana ta fito.