Sashe 114
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 6 min read
Hayatuddeen da abokansa kuwa, tuni suke ta murnar bikin, inda suka shirya partyn da zasuyi a bikin nasu na musamman, tuni Hayatuddeen ya watsa hotunan katin auren ashafinsa na Instagram da kuma WhatsApp status ɗinsa, tuni Ameena ta haukace masa da tayi tozali da invitation card ɗin, nan tafara kuka yayinda zuciyarta tacika da kishi haɗi da raɗaɗin auren na Saifuddeen da zaiyi, wasa-wasa fa Ameena harda kwanciya zazzaɓi.
Asma'u ma sosai tayi takaici domin bata da wani buri daya wuce kasancewarta da Saifuddeen, ita kanta batasan soyayyarsa tashigeta sosai ba saida taga katin na aurensa da Zaleeha kuma dai hakan baisa ta sauya k'udirinta ba.
Ɓangaren Zaleeha kuwa tun jiya da ta sa kanta aɗaki ta kulle bata ƙara ko leƙowa ba, gaba ɗaya haka ta wuni cikin ɗaki, zuciyarta cike da ƙunci, haɗi da takaici, tuni tagama shirya duk wani plant ɗinta na yanda zata fitowa da ƴan gidannasu sabon tsarin takunta, na yanda zata rufe idanunta ta shumfuɗa taɓaran ƙin auren Saifuddeen da ake ƙoƙarin laƙaba mata. Hakanan ta-tashi yau da son zuwa gidan yayarta Maryam, don haka tun safe ta kammala shirye shiryenta, wanka tayi inda ta shirya kanta cikin wata haɗaɗɗiyar doguwar riga navy blue colour mai kyaun gaske, sosai rigan tabi shape ɗin jikinta ta ƙafe, yayinda adon stones ɗin rigarta keta shinning yana ɗauke ido, parking dogon gashinta tayi atsakiyar kanta, kana tayi rolling ɗan maidaidaicin vail ɗin rigan akanta, wanda ya sauƙo har zuwa kan ƙirjinta, wani ɗan maidaidaicin hand bag ɗinta shima me kalar navy ta riƙe ahannunta tare da ɗaukan wayoyinta, ƙiran iphone da kuma samsung, wani navy blue toms masu kyau da taushin gaske ta sanya aƙafafunta, wanka tayiwa jikinta da daddaɗan turarenta mai daɗin ƙamshi, sosai tayi kyau duk da kasancewar ƴar rama ta bayyana ajikinta amma tayi kyau sosai, raman ma saiya kasance yaƙara mata kyau da burgewa.
Cikin takunta mai ɗauke da burgewa tafito daga cikin ɗakin nata, bata samu kowa acikin falon ba hakan yasa kai tsaye ta nufi compound ɗin gidan, cikin nutsuwa taƙarasa jikin motarta, buɗe murfin motar tayi tare da shigewa ciki, maigadi ne ya wangale mata gate sannu ahankali tatura hancin motar tata waje, cikin nutsuwa haka take murza steering motar, azahiri idan kaganta bazaka taɓa tunanin cewa wani abu na damunta ba, amma abaɗini tanajin kusan ma tafi kowa yawan damuwa, sosai takejin kamar zuciyarta zata fashe saboda damuwa, batayi wani tafiya sosai ba taƙaraso gaban gidan na Maryam wanda yake madaidaici mai kyaun gaske, maigadi ne ya wangale mata gate ɗin gidan ta cilla hancin motar ciki.
Da mamaki take kallon motar Yaya Ahmad dake fake cikin compound ɗin gidan na Maryam, sam batasan ma da zuwansa cikin garin na Gombe ba, da ɗan sauri ta bude murfin motar tafito, direct ta nufi cikin gidan, ahankali ta murɗa handle ɗin ƙofar tashiga, bakinta ɗauke da sallama, Ya Ahmad, Maryam, sune zaune acikin falon yayinda suka juyo da kallonsu gareta, idanunta ne suka sauƙa acikin na Ya Ahmad, saurin ɗauke idanunta tayi tare da turo bakin nata gaba, lokaci guda hawaye suka cika idanunta, sai kawai ta kawar da kanta gefe, cak kuma ta tsaya batare da ta ƙaraso tsakiyar falon inda suke zaune ba.
"Zaleeha!." Maryam taƙira sunanta murya asanyaye, domin tuni ta hango ƙyallin hawaye acikin idanun Zaleehan.
Ɗan juyowa Zaleeha tayi ta kalli yayarta ta, sai kuma ga hawaye zirrr sun ziraro daga cikin idanunta, rumtse idanu Ya Ahmad yayi tare da ɗan cije laɓɓansa, sam baya ƙaunar ganin hawaye a idon ƙannensa, musamman ma ita Zaleeha dayakejinta matsayin shalelensa, cikin son sama mata nutsuwa yace.
"Bansan ƴan matan Yaya Ahmad da saurin kuka haka ba, nasan dai tana da juriya sosai, calm down my lovely sister, zo kigayamin menene damuwar da har tasanyaki hawaye!".
Ae tuni kafun ma yaƙare maganar tasa ta rugu da gudu zuwa cikin falon, faɗawa jikinsa tayi tare da sakin wani irin kuka mai taɓa zuciya, ƙwarai tajima bata samu wanda zata shiga jikinsa tayi kuka haka ba sai yau, hakan yasa ta ƙara riƙe Ya Ahmad ɗin nata tana kuka sosai, shiru Yaya Ahmad da Maryam sukayi, sam sun kasa hanata kukan, domin sunyi imani cewa kuka ma rahamane, sannan wani lokaci yana gusar da damuwa, kana kuma duk cikinsu babu wanda baisan kukan me Zaleehan keyi ba, domin dama ansan tatsuniyar gizo bata wuce ta ƙoƙi, tayi kuka sosai, aƙalla ta share sama da mintuna 15 tana kuka, sannu ahankali kukannata ya tsagaita, ajiyar zuciya kawai take sauƙewa akai-akai, ɗagota daga jikinsa Ya Ahmad yayi tare da kai dubansa gareta, hannu yasa ya goge hawayen da gaba ɗaya suka dame fuskarta, cikin tausasa murya yace.
"Akullum tun kina ƙarama nakasance ina me horanki da ki-kasance mai haƙuri, Domin shi haƙuri yana maganin abubuwa da yawa Zaleeha, sannan Addu'a tafi kuka don itace babban jigo akan komai, ke ƴar uwata ce kuma jinina, bazan taɓa son ganinki cikin damuwa ba, amma yazamuyi Zaleeha? yarda da ƙaddara mai kyau ko akasinta alamace dake nuna ƙarfin imanin mutum, sannan kada ki manta kowani bawa a duniya da irin jarabawar da Allah yake ɗaura masa, wani mai kyau wani akasinta, shin meyasa bazaki sa aranki cewa aurenki da ake ƙoƙarin yi da Saifuddeen haɗi ne na Allah Ba? babu fa wani bawa aduniya daya isa sauyawa kansa Ƙaddararsa!."
ɗan tsagaitawa da maganan yayi kana ya sanya hannunsa ya shafi kanta, cikin son kwantar mata da hankali yace.
"Kaf cikin ƙannena nafi ƙaunarki Zaleeha, inason duk wani abu da kikeso, banason ɓacin ranki ko kaɗan, dan Allah Zaleeha, kada ki watsawa mahaifinmu ƙasa a ido, kizama mai biyayya agaresa koda yaushe, ita al'barkan iyaye tana da tasiri akan ƴaƴa, har abada Baba Malam bazai taɓayin danasanin zamantowarki ƴa agaresa ba matuƙar kikayi masa biyayya, zai tabbata yana me alfahari dake, ki yi dubi ga ƴar uwarki".
Ya nuna Maryma wanda take zaune itama idanunta sunyi rau rau, kana sun cika da ƙwalla.
"Maryam takasance abun al'faharin Baba Malam, tayi masa biyayya, bata bijiremasa ba, tayarda da zaɓinsa duk da cewa bata so, amma ayanzu ki dubeta, tana zaune cikin jin daɗi, farin ciki, annushuwa haɗi da salama, hakan yafarune kuma duk saboda biyayyan da tayi ga mahaifinmu, sam bata bijire masa ba duk da kuwa bataso, haka yasa muke tsananin sonta kema ki daure ki masa wannan biyayyar."
Hannayen Zaleeha ya kamo cike da kula yace.
"Dan Allah Zaleeha kimin al'ƙawarin zaki yiwa Baban mu biyayya, Insha Allah aurenki da Saifuddeen al'khairi ne, sannan Baba Malam bazai taɓa kaiki inda za'a cutar dake ba!."
Sabon kuka Zaleeha tasanya wiwi kamar wanda aka faɗawa ranar muruwarta, sam kalaman Ya Ahmad basu shigeta ba, inama dazai gane cewa ayanzu idanunta sun rufe, bataji bata gani, inama dabai ɓata lokacin sa ya faɗi waƴannan maganganun ba, zuciyarta tajima dayin nisa wajen tsanan Saifuddeen, bata sonsa, ba kuma ta son aurensa. Haka Zaleeha ta dinga yi musu kuka wiwi, Ya Ahmad da Maryam kuwa sai nasiha sukeyi mata tare da ban baki, saidai kuma ko ɗaya bata ɗaukar nasiharsu, aduk ma sanda sukace da ita tayi haƙuri ta ɗauki Ƙaddara, takuma yiwa mahaifinsu biyayya, saitaji kamar wuƙa suke caka mata agadon bayanta, idan kuwa suka yaba Saifuddeen, suka kuma ce ta rungumi aurensa hannu bibbiyu sai taji kamar narkakken dalma suke watsa mata cikin kunnuwanta.
Haka dai tasha kukanta ta ƙoshi har saida idanunta suka kumbura, daga ƙarshe dai Ya Ahmad ne dayaji yanda jikinta ya ɗau zafi yasakata amotarsa suka dawo gida, yayinda tabar motar ta agidan Maryam ɗin.
Tunda ta dawo daga gidan Maryam tasa kanta aɗaki ta kulle, wani zazzafan zazzaɓi kuwa take yakawo mata ziyara, domin irin kukan da tayi yauɗin nadabanne.
Asma'u ma sosai tayi takaici domin bata da wani buri daya wuce kasancewarta da Saifuddeen, ita kanta batasan soyayyarsa tashigeta sosai ba saida taga katin na aurensa da Zaleeha kuma dai hakan baisa ta sauya k'udirinta ba.
Ɓangaren Zaleeha kuwa tun jiya da ta sa kanta aɗaki ta kulle bata ƙara ko leƙowa ba, gaba ɗaya haka ta wuni cikin ɗaki, zuciyarta cike da ƙunci, haɗi da takaici, tuni tagama shirya duk wani plant ɗinta na yanda zata fitowa da ƴan gidannasu sabon tsarin takunta, na yanda zata rufe idanunta ta shumfuɗa taɓaran ƙin auren Saifuddeen da ake ƙoƙarin laƙaba mata. Hakanan ta-tashi yau da son zuwa gidan yayarta Maryam, don haka tun safe ta kammala shirye shiryenta, wanka tayi inda ta shirya kanta cikin wata haɗaɗɗiyar doguwar riga navy blue colour mai kyaun gaske, sosai rigan tabi shape ɗin jikinta ta ƙafe, yayinda adon stones ɗin rigarta keta shinning yana ɗauke ido, parking dogon gashinta tayi atsakiyar kanta, kana tayi rolling ɗan maidaidaicin vail ɗin rigan akanta, wanda ya sauƙo har zuwa kan ƙirjinta, wani ɗan maidaidaicin hand bag ɗinta shima me kalar navy ta riƙe ahannunta tare da ɗaukan wayoyinta, ƙiran iphone da kuma samsung, wani navy blue toms masu kyau da taushin gaske ta sanya aƙafafunta, wanka tayiwa jikinta da daddaɗan turarenta mai daɗin ƙamshi, sosai tayi kyau duk da kasancewar ƴar rama ta bayyana ajikinta amma tayi kyau sosai, raman ma saiya kasance yaƙara mata kyau da burgewa.
Cikin takunta mai ɗauke da burgewa tafito daga cikin ɗakin nata, bata samu kowa acikin falon ba hakan yasa kai tsaye ta nufi compound ɗin gidan, cikin nutsuwa taƙarasa jikin motarta, buɗe murfin motar tayi tare da shigewa ciki, maigadi ne ya wangale mata gate sannu ahankali tatura hancin motar tata waje, cikin nutsuwa haka take murza steering motar, azahiri idan kaganta bazaka taɓa tunanin cewa wani abu na damunta ba, amma abaɗini tanajin kusan ma tafi kowa yawan damuwa, sosai takejin kamar zuciyarta zata fashe saboda damuwa, batayi wani tafiya sosai ba taƙaraso gaban gidan na Maryam wanda yake madaidaici mai kyaun gaske, maigadi ne ya wangale mata gate ɗin gidan ta cilla hancin motar ciki.
Da mamaki take kallon motar Yaya Ahmad dake fake cikin compound ɗin gidan na Maryam, sam batasan ma da zuwansa cikin garin na Gombe ba, da ɗan sauri ta bude murfin motar tafito, direct ta nufi cikin gidan, ahankali ta murɗa handle ɗin ƙofar tashiga, bakinta ɗauke da sallama, Ya Ahmad, Maryam, sune zaune acikin falon yayinda suka juyo da kallonsu gareta, idanunta ne suka sauƙa acikin na Ya Ahmad, saurin ɗauke idanunta tayi tare da turo bakin nata gaba, lokaci guda hawaye suka cika idanunta, sai kawai ta kawar da kanta gefe, cak kuma ta tsaya batare da ta ƙaraso tsakiyar falon inda suke zaune ba.
"Zaleeha!." Maryam taƙira sunanta murya asanyaye, domin tuni ta hango ƙyallin hawaye acikin idanun Zaleehan.
Ɗan juyowa Zaleeha tayi ta kalli yayarta ta, sai kuma ga hawaye zirrr sun ziraro daga cikin idanunta, rumtse idanu Ya Ahmad yayi tare da ɗan cije laɓɓansa, sam baya ƙaunar ganin hawaye a idon ƙannensa, musamman ma ita Zaleeha dayakejinta matsayin shalelensa, cikin son sama mata nutsuwa yace.
"Bansan ƴan matan Yaya Ahmad da saurin kuka haka ba, nasan dai tana da juriya sosai, calm down my lovely sister, zo kigayamin menene damuwar da har tasanyaki hawaye!".
Ae tuni kafun ma yaƙare maganar tasa ta rugu da gudu zuwa cikin falon, faɗawa jikinsa tayi tare da sakin wani irin kuka mai taɓa zuciya, ƙwarai tajima bata samu wanda zata shiga jikinsa tayi kuka haka ba sai yau, hakan yasa ta ƙara riƙe Ya Ahmad ɗin nata tana kuka sosai, shiru Yaya Ahmad da Maryam sukayi, sam sun kasa hanata kukan, domin sunyi imani cewa kuka ma rahamane, sannan wani lokaci yana gusar da damuwa, kana kuma duk cikinsu babu wanda baisan kukan me Zaleehan keyi ba, domin dama ansan tatsuniyar gizo bata wuce ta ƙoƙi, tayi kuka sosai, aƙalla ta share sama da mintuna 15 tana kuka, sannu ahankali kukannata ya tsagaita, ajiyar zuciya kawai take sauƙewa akai-akai, ɗagota daga jikinsa Ya Ahmad yayi tare da kai dubansa gareta, hannu yasa ya goge hawayen da gaba ɗaya suka dame fuskarta, cikin tausasa murya yace.
"Akullum tun kina ƙarama nakasance ina me horanki da ki-kasance mai haƙuri, Domin shi haƙuri yana maganin abubuwa da yawa Zaleeha, sannan Addu'a tafi kuka don itace babban jigo akan komai, ke ƴar uwata ce kuma jinina, bazan taɓa son ganinki cikin damuwa ba, amma yazamuyi Zaleeha? yarda da ƙaddara mai kyau ko akasinta alamace dake nuna ƙarfin imanin mutum, sannan kada ki manta kowani bawa a duniya da irin jarabawar da Allah yake ɗaura masa, wani mai kyau wani akasinta, shin meyasa bazaki sa aranki cewa aurenki da ake ƙoƙarin yi da Saifuddeen haɗi ne na Allah Ba? babu fa wani bawa aduniya daya isa sauyawa kansa Ƙaddararsa!."
ɗan tsagaitawa da maganan yayi kana ya sanya hannunsa ya shafi kanta, cikin son kwantar mata da hankali yace.
"Kaf cikin ƙannena nafi ƙaunarki Zaleeha, inason duk wani abu da kikeso, banason ɓacin ranki ko kaɗan, dan Allah Zaleeha, kada ki watsawa mahaifinmu ƙasa a ido, kizama mai biyayya agaresa koda yaushe, ita al'barkan iyaye tana da tasiri akan ƴaƴa, har abada Baba Malam bazai taɓayin danasanin zamantowarki ƴa agaresa ba matuƙar kikayi masa biyayya, zai tabbata yana me alfahari dake, ki yi dubi ga ƴar uwarki".
Ya nuna Maryma wanda take zaune itama idanunta sunyi rau rau, kana sun cika da ƙwalla.
"Maryam takasance abun al'faharin Baba Malam, tayi masa biyayya, bata bijiremasa ba, tayarda da zaɓinsa duk da cewa bata so, amma ayanzu ki dubeta, tana zaune cikin jin daɗi, farin ciki, annushuwa haɗi da salama, hakan yafarune kuma duk saboda biyayyan da tayi ga mahaifinmu, sam bata bijire masa ba duk da kuwa bataso, haka yasa muke tsananin sonta kema ki daure ki masa wannan biyayyar."
Hannayen Zaleeha ya kamo cike da kula yace.
"Dan Allah Zaleeha kimin al'ƙawarin zaki yiwa Baban mu biyayya, Insha Allah aurenki da Saifuddeen al'khairi ne, sannan Baba Malam bazai taɓa kaiki inda za'a cutar dake ba!."
Sabon kuka Zaleeha tasanya wiwi kamar wanda aka faɗawa ranar muruwarta, sam kalaman Ya Ahmad basu shigeta ba, inama dazai gane cewa ayanzu idanunta sun rufe, bataji bata gani, inama dabai ɓata lokacin sa ya faɗi waƴannan maganganun ba, zuciyarta tajima dayin nisa wajen tsanan Saifuddeen, bata sonsa, ba kuma ta son aurensa. Haka Zaleeha ta dinga yi musu kuka wiwi, Ya Ahmad da Maryam kuwa sai nasiha sukeyi mata tare da ban baki, saidai kuma ko ɗaya bata ɗaukar nasiharsu, aduk ma sanda sukace da ita tayi haƙuri ta ɗauki Ƙaddara, takuma yiwa mahaifinsu biyayya, saitaji kamar wuƙa suke caka mata agadon bayanta, idan kuwa suka yaba Saifuddeen, suka kuma ce ta rungumi aurensa hannu bibbiyu sai taji kamar narkakken dalma suke watsa mata cikin kunnuwanta.
Haka dai tasha kukanta ta ƙoshi har saida idanunta suka kumbura, daga ƙarshe dai Ya Ahmad ne dayaji yanda jikinta ya ɗau zafi yasakata amotarsa suka dawo gida, yayinda tabar motar ta agidan Maryam ɗin.
Tunda ta dawo daga gidan Maryam tasa kanta aɗaki ta kulle, wani zazzafan zazzaɓi kuwa take yakawo mata ziyara, domin irin kukan da tayi yauɗin nadabanne.