Sashe 19
Nakasa Ba Kasawa Bace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bayan an idar duk an fiffito ne sai Bappa Ali yacewa Saifuddeen zasufa tafi masallacin fada yanzu zasu fara tafsir d'in dan takwas ta kusa.
Mudassir ne ya kalllesu kana yace,
"Bari inje in cewa Ummi tafa ajiye mana jolof d'innan in mun taso tabsir zamuci dan ni in nazo konciya sai naci abinci."
dariya sukayi mishi kana Warisu dake bayansu yace.
"Anya ko kai bafullatanine Mudassir dan gaskiya fulani basu da yawanci."
Ahmad ne da shima yanzu ya iso yace.
"Yoh ai shi iyamburi ne bakaga yadda yayi k'atoba."
shiko Mudassir shafa cikinsa yayi tare da cewa.
"Me yafi raina."
dariya suka kumayi sai Saifuddeen da yaketa murmushi sai kuma Warisu ya kalli Saifuddeen kana ya kallesu tare da cewa.
"Ni ai ko dan kar inyi k'aton ciki zan yiwa kaina k'aidar ci abinci,
wlh da nasan yadda zanyi in koma kamar Saifuddeen da nayi na koma,
kalleshi komai na jikinshi dai-dai da shekarunsa,
shiyasa yake tafiya da kenshi da k'uruciyarshi,
wlh koda namiji d'an uwanshi in ya ganshi sai ya kuma kallonshi in ka ganshi kamar balarabe ko ba indiye."
cikin kauda kai Saifuddeen ya d'an shafa suman kanshi tare da mishi alamar.
"Kai Warisu in naga wani kyau."
daga nan suka shiga cikin gida bisa taburmar da Ummi ke zaune suka zauna bayan sun gaisane ta kallesu cikin kula tace.
"Ya kamata ace iwar haka kuna wurin tafsir, ku rage yawon dare kun san wannan wata ta musammance ga musulmai."
mik'ewa sukayi da sauri sai kuma Mudassir yace.
"Yauwa Ummi a ajiye mana taliyar nanfa in mun taso zamuci."
cikin jin dad'in had'in kan yaran tace.
"Ba matsala sai kun dawo."
daga nan suka juya har sunje bakin k'ofa tace.
"Ahmad kwana zamuyi ko."
cikin tsiya wasu Salisu yace.
"No Ummi ba kwana zanyiba ai inada yan rakiya."
yana fad'in haka sukayi ca a kanshi wai bazasu rakashi ba.
ita kam Ummi da murmushi ta rakasu.
Bayan sunje suka samu anata taruwa manya da yara da dottab'ai duk an cika can ta wojen gidan sarki kuma wani rumfane da mata ke taruwa a ciki.
Suna shiga duk sukayi gefen da aka ajiye mazaunin malam,
wuri d'aya suka zauna yayinda tuni,
Saifuddeen kuma ya zagaya bayan Bappa Ali da alarammanshi Abdurahman gyara tsayuwarshi yayi gefen d'an agajin dake bayansu Bappa Alin.
shi kuwa Bappa Ali da alarammanshi gyara abin sautin mgnar dake gabansu sukayi tare da d'an sunkuyawa kan Qur'anen dake bud'e a gansu inda bana zasuyi tabsir d'in ```suratul Maedah.```
shi kuwa Saifuddeen ta cikin glass d'in table d'in gabansu yake ganin fuskar Bappa Ali ras har yadda zai gane motsin bakinshi da abinda yake fad'in.
dan haka ya maida hankalinshi bisa bakin bappan nashi.
Bayan anyi addu'a an bud'e taro kana ya kuma jero addu'o'i. gyara zamanshi yayi kana cikin sakekken sauti yace.
"Alhamdulillahi Allah ya kawomu watan Ramadan tun kafin mu shiga cikin tafsirin namu zan d'anyi tsokaci ga yan kasuwanmu."
sai ya kuma d'ago kanshi ya d'an kalli taron jama'ar dake cike da masallacin ido ya d'an zuba musu tare da ci gaba da cewa.
"Shi watan Ramadan wotan rahama ne da jink'ai da kuma tausayin juna. Amman abin takaici abin haushi tun gabanin zuwan watan zakaga wasu musulman suna k'arawa kayayyakin sana'arsu kud'i domin suyi tsada, maimakon su rage musu k'ud'in domin tausayawa juna da tallafawa tallakawa."
sai ya kuma tsagaita. shi kuwa Saifuddeen tuni yake fassara abinda yake fad'in da body language yadda masu matsalar ji zasu iya gane komai a sau k'ak'e.
cikin nitsuwa Bappa Ali yaci gaba da sharan fage akan bayanin Ramadan inda yake cewa.
"Yana daga cikin fa'idojin azumi,
Azumi na sanya bawa godewa ni'imomin Allah mad'aukaki.
Azumi na taimaka wa bawa gurin barin abinda Allah ya haramta.
A cikin azumi akwai tsanani ga shaid'an da raunatashi.
Sannan Azumi na karya k'arfin sha'awa mu samman ga matasanmu.
Azumi na gadar da samin rahamar Allah da jin k'ansa.
Azumi na koyarwa bawa tsoron Allah, da tausayin na k'asa dashi.
Azumi na tafe da wasu falaloli na musamman,
da yawa sai a azumi suke samun dama da k'arfin guiwar shiga itikafi.
Itikafi shine keb'ewa ko zama cikin masallaci domin ibada.
Mafi falalan itikafi lokacin goman k'arshe, yin itikafi sunnace mai k'arfi
yin itikafi a masallacin jumma'a idan kwanakin da za'ayi sun had'a da jumma.
Idan zaka shiga itikafi zaka shiga kafin fad'uwar rana a daren da kake son fara itikafin.
Mustahabbi ne ga maiyin itikafi ya keb'ance da ibadu yawan salloli, zhikiri, addu'a, karatun Qur'an, tuba, istik'afari, salatin annabi, da dai sauransu domin nemar kusanci da yardar Allah.
Mai itikafi idan ya gama kwanakin da yayi niya zai fitane bayan fad'uwan rana.
Baya halatta ga mai yin itikafi ya fita zuwa duba mara lfy da kusantar iyali.
Amman mai itikafi zai iya fita domin abinda ya zama dole kamar buk'atu irin na d'an adam,
kamarsu zagayawa bayan gida da neman abinda zaici.
Idan rashin lfy ko jinin haila suka zowa mai itikafi,
zasu fita idan ya samu sauk'i ko ta samu tsarki sai a dawo."
gaba d'aya wurin anyi tsit ana sauraron bayanin malam Alin.
daga nan ya d'anyi k'arin bayani game da azumin kanshi inda yake cewa.
"Abubuwan k'i ga mai azumi,
Kaiwa matuk'a gurin kurkuran baki da shak'a ruwa.
Sumbatar iyali da makamancin haka ga wanda baya iya mallakar kanshi.
D'andanon abinci badon buk'ata ba.
B'ata lokaci kawai wasannin banza da surutai marasa amfani.
Zarcewa da azumi kwana biyu zuwa sama."
A k'arshe yace a tak'aice abinda ya kamata ga mai azumi ya kiyaye harshensa daga dukkan maganganun banza zagi annamimanci giba isgilanci da sauransu kodako a social media ne.
Daga nan suka shiga cikin tafsir d'in nasu gadan-gadan,
mutane sun nitsu wurin jin fad'in allahu subahanahu wata ala.
K'arfe tara dai-dai aka tashi, Saifuddeen ne ya karb'i d'an jakar Quran d'in bappan nashi kana suka wuce gida da abo kanshi,
suna shiga su suka wuce d'akinshi shi kuwa ya bi bayan bappa Ali da jakarshi saida suka shiga ya bashi sannan ya juyo ya nufi side insu,
murmushi yayi ganin suna fito daga d'akinshi suna zuwa tsakar gida Ummi kuwa taburma ta shimfid'a musu kana ta zuba musu zazzafan colof d'inan a tire tare da basu forks Mudassir ne ya amshi cokulan ya raba musu kana suka fara ci,
Raliyya kuwa babban kofi ta d'auka ta d'ebo musu ruwan randar d'akinshi ta kawo musu,
shi kam bai kula abincinba suma basubi ta kanshiba dan sun sanshi sam baida cin abinci,
Warisu ma kad'an yaci ya ajiye spoon d'in sabida baison yayi teb'a
suna gamawa suka sha ruwa kana suka fita suka raka Ahmad har shabewa sannan suka dawo,
tuni sha d'aya tayi shiyasa kowa ya nufi gida.
Yauma da dare kamar jiya haka Ummi ta tashi yaranta,
sai k'arfe uku Rahma ta tuk'a musu tuwon shinkafa dama kuma Raihana tayi musu miyar zogale tun da dare.
to yau Saifuddeen ya d'anci mai d'an yawa kana yasha tea,
suna gama sahur din ya shiga wonka kafin ya fito anyi assalatu,
so alwala yayi tasa Hayatudden a a gaba suka tafi,
su Ummi kuma sukayi nasu a gida.
Ana idar da salla ya fara azkar nashi sai da ya gama sannan ya shiga suka gaisa da Ummi kana ya bata 5k d'innan yace ta sama musu asusu na daban ta rink'a sasu,
ita kam Ummi tayi mmkin yawan kudin to ganin yana sauri Salisu na jiranshi yasa ta barshi ya tafi sai ya dawo suyi mgna.
Suna isa Salisu ya sauk'eshi a bakin masallacin bakin kasuwan,
shi kuma ya wuce kabo-kabonshi.
shi kuwa Saifuddeen cikin masallacin ya shiga kamar jiya yayi baccin awa d'aya da rabi kana yana farkawa yayi Al'wala yayi walaha raka'a biyu sannan yayi addu'o'inshi kafin ya fito ya nufi cikin kad'uwa.
Yana shiga kai tsaye dilansu na leda ya shiga inda ya samu mutun biyu a gabanshi dole yabi layi,
bayan an basu shima aka bashi na 60k Lamar na jiya kenan k'arfe 10:00 Am dai-dai suka bashi nashin,
with full confidence ya fara bin layi-layi shago-shago lungu da sak'o yana raba musu suna bashi kud'in na jiya, 1:35 pm ya gama rabawa da yake kusan fiye da rabin kasuwar duk a wurin baba bello suke sayan ledan to shiyasa yake dad'ewa yana yawata kasuwan da k'afa tunda shi bashi da keke kamar baba bello,
yana gamawa yazo ya had'a lissafin kud'in ya samu dubu settin da bakwai da dari biyu, cikin aminci ya basu 60k d'insu sannan ya adana ribarshi a jikinshi godiya yayi musu bayan an rubuta ya dawo da kud'in na jiya,
tafiya yake yana nazari shifa gani yakeyi kamar kyauta suke bashi kud'in duk da ko azabar nauyin kwalin da yake azawa a k'afad'anshi na dama aikine mai matuk'ar wuya ga yawo cikin rana har ji yake k'afafunshi suna yum-yum dan azaban rana da nauyin kayan da yake azawa a kafad'anshi.
Ganin azahar ta kawo kai yasa ya zauna ya d'an huta dan yana jin kafad'arshi na mishi ciwo ga zafin ranan da yabi sai yake jin wani irin azabebben k'ishi ,
ganin an kira salla yasa ya mik'e yaje yayi al'wala kana ya shiga sahu,
bayan an idar ne ya mik'e a gajiye yana tafiya a hankali yaje ya karb'i omo dasu sabulu,
sai kuma ya zage da talla dan yanada burin ya maida Raihana da Raliyya makaranta in kes dai ace sun gama koda d'an Secondary school,
yana kuma fatan ya ink'anta karatun Hayatuddeen da Faruq da Adam kuma yana fatan Allah ya hanasu sake tsammatan abinda zasuci daga wurin wani.
Da wannan tunanin ya zage yaketa yawa tawa cikin ikon Allah ranar ribar 1,200 ya samu.
Ganin ya fara ganin jirine ya sashi neman inuwa ya zauna saida ya huta sannan ya maida sauran omon.
ganin hud'u da rabi tayi sai yaje shagon ba mishkila gero ya auna mudu shida sai wake mudu shida sai sugar mudu d'aya da rabi,
daga nan yaje ya sayi mai k'aramin galam sai ya saya musu lemu da ayaba da kankana,
A tak'aice dai ya kashe dubu uku d'ari biyun nan sai dubu biyar ya bari su kuma na sawa a asusune.
Mudassir ne ya kalllesu kana yace,
"Bari inje in cewa Ummi tafa ajiye mana jolof d'innan in mun taso tabsir zamuci dan ni in nazo konciya sai naci abinci."
dariya sukayi mishi kana Warisu dake bayansu yace.
"Anya ko kai bafullatanine Mudassir dan gaskiya fulani basu da yawanci."
Ahmad ne da shima yanzu ya iso yace.
"Yoh ai shi iyamburi ne bakaga yadda yayi k'atoba."
shiko Mudassir shafa cikinsa yayi tare da cewa.
"Me yafi raina."
dariya suka kumayi sai Saifuddeen da yaketa murmushi sai kuma Warisu ya kalli Saifuddeen kana ya kallesu tare da cewa.
"Ni ai ko dan kar inyi k'aton ciki zan yiwa kaina k'aidar ci abinci,
wlh da nasan yadda zanyi in koma kamar Saifuddeen da nayi na koma,
kalleshi komai na jikinshi dai-dai da shekarunsa,
shiyasa yake tafiya da kenshi da k'uruciyarshi,
wlh koda namiji d'an uwanshi in ya ganshi sai ya kuma kallonshi in ka ganshi kamar balarabe ko ba indiye."
cikin kauda kai Saifuddeen ya d'an shafa suman kanshi tare da mishi alamar.
"Kai Warisu in naga wani kyau."
daga nan suka shiga cikin gida bisa taburmar da Ummi ke zaune suka zauna bayan sun gaisane ta kallesu cikin kula tace.
"Ya kamata ace iwar haka kuna wurin tafsir, ku rage yawon dare kun san wannan wata ta musammance ga musulmai."
mik'ewa sukayi da sauri sai kuma Mudassir yace.
"Yauwa Ummi a ajiye mana taliyar nanfa in mun taso zamuci."
cikin jin dad'in had'in kan yaran tace.
"Ba matsala sai kun dawo."
daga nan suka juya har sunje bakin k'ofa tace.
"Ahmad kwana zamuyi ko."
cikin tsiya wasu Salisu yace.
"No Ummi ba kwana zanyiba ai inada yan rakiya."
yana fad'in haka sukayi ca a kanshi wai bazasu rakashi ba.
ita kam Ummi da murmushi ta rakasu.
Bayan sunje suka samu anata taruwa manya da yara da dottab'ai duk an cika can ta wojen gidan sarki kuma wani rumfane da mata ke taruwa a ciki.
Suna shiga duk sukayi gefen da aka ajiye mazaunin malam,
wuri d'aya suka zauna yayinda tuni,
Saifuddeen kuma ya zagaya bayan Bappa Ali da alarammanshi Abdurahman gyara tsayuwarshi yayi gefen d'an agajin dake bayansu Bappa Alin.
shi kuwa Bappa Ali da alarammanshi gyara abin sautin mgnar dake gabansu sukayi tare da d'an sunkuyawa kan Qur'anen dake bud'e a gansu inda bana zasuyi tabsir d'in ```suratul Maedah.```
shi kuwa Saifuddeen ta cikin glass d'in table d'in gabansu yake ganin fuskar Bappa Ali ras har yadda zai gane motsin bakinshi da abinda yake fad'in.
dan haka ya maida hankalinshi bisa bakin bappan nashi.
Bayan anyi addu'a an bud'e taro kana ya kuma jero addu'o'i. gyara zamanshi yayi kana cikin sakekken sauti yace.
"Alhamdulillahi Allah ya kawomu watan Ramadan tun kafin mu shiga cikin tafsirin namu zan d'anyi tsokaci ga yan kasuwanmu."
sai ya kuma d'ago kanshi ya d'an kalli taron jama'ar dake cike da masallacin ido ya d'an zuba musu tare da ci gaba da cewa.
"Shi watan Ramadan wotan rahama ne da jink'ai da kuma tausayin juna. Amman abin takaici abin haushi tun gabanin zuwan watan zakaga wasu musulman suna k'arawa kayayyakin sana'arsu kud'i domin suyi tsada, maimakon su rage musu k'ud'in domin tausayawa juna da tallafawa tallakawa."
sai ya kuma tsagaita. shi kuwa Saifuddeen tuni yake fassara abinda yake fad'in da body language yadda masu matsalar ji zasu iya gane komai a sau k'ak'e.
cikin nitsuwa Bappa Ali yaci gaba da sharan fage akan bayanin Ramadan inda yake cewa.
"Yana daga cikin fa'idojin azumi,
Azumi na sanya bawa godewa ni'imomin Allah mad'aukaki.
Azumi na taimaka wa bawa gurin barin abinda Allah ya haramta.
A cikin azumi akwai tsanani ga shaid'an da raunatashi.
Sannan Azumi na karya k'arfin sha'awa mu samman ga matasanmu.
Azumi na gadar da samin rahamar Allah da jin k'ansa.
Azumi na koyarwa bawa tsoron Allah, da tausayin na k'asa dashi.
Azumi na tafe da wasu falaloli na musamman,
da yawa sai a azumi suke samun dama da k'arfin guiwar shiga itikafi.
Itikafi shine keb'ewa ko zama cikin masallaci domin ibada.
Mafi falalan itikafi lokacin goman k'arshe, yin itikafi sunnace mai k'arfi
yin itikafi a masallacin jumma'a idan kwanakin da za'ayi sun had'a da jumma.
Idan zaka shiga itikafi zaka shiga kafin fad'uwar rana a daren da kake son fara itikafin.
Mustahabbi ne ga maiyin itikafi ya keb'ance da ibadu yawan salloli, zhikiri, addu'a, karatun Qur'an, tuba, istik'afari, salatin annabi, da dai sauransu domin nemar kusanci da yardar Allah.
Mai itikafi idan ya gama kwanakin da yayi niya zai fitane bayan fad'uwan rana.
Baya halatta ga mai yin itikafi ya fita zuwa duba mara lfy da kusantar iyali.
Amman mai itikafi zai iya fita domin abinda ya zama dole kamar buk'atu irin na d'an adam,
kamarsu zagayawa bayan gida da neman abinda zaici.
Idan rashin lfy ko jinin haila suka zowa mai itikafi,
zasu fita idan ya samu sauk'i ko ta samu tsarki sai a dawo."
gaba d'aya wurin anyi tsit ana sauraron bayanin malam Alin.
daga nan ya d'anyi k'arin bayani game da azumin kanshi inda yake cewa.
"Abubuwan k'i ga mai azumi,
Kaiwa matuk'a gurin kurkuran baki da shak'a ruwa.
Sumbatar iyali da makamancin haka ga wanda baya iya mallakar kanshi.
D'andanon abinci badon buk'ata ba.
B'ata lokaci kawai wasannin banza da surutai marasa amfani.
Zarcewa da azumi kwana biyu zuwa sama."
A k'arshe yace a tak'aice abinda ya kamata ga mai azumi ya kiyaye harshensa daga dukkan maganganun banza zagi annamimanci giba isgilanci da sauransu kodako a social media ne.
Daga nan suka shiga cikin tafsir d'in nasu gadan-gadan,
mutane sun nitsu wurin jin fad'in allahu subahanahu wata ala.
K'arfe tara dai-dai aka tashi, Saifuddeen ne ya karb'i d'an jakar Quran d'in bappan nashi kana suka wuce gida da abo kanshi,
suna shiga su suka wuce d'akinshi shi kuwa ya bi bayan bappa Ali da jakarshi saida suka shiga ya bashi sannan ya juyo ya nufi side insu,
murmushi yayi ganin suna fito daga d'akinshi suna zuwa tsakar gida Ummi kuwa taburma ta shimfid'a musu kana ta zuba musu zazzafan colof d'inan a tire tare da basu forks Mudassir ne ya amshi cokulan ya raba musu kana suka fara ci,
Raliyya kuwa babban kofi ta d'auka ta d'ebo musu ruwan randar d'akinshi ta kawo musu,
shi kam bai kula abincinba suma basubi ta kanshiba dan sun sanshi sam baida cin abinci,
Warisu ma kad'an yaci ya ajiye spoon d'in sabida baison yayi teb'a
suna gamawa suka sha ruwa kana suka fita suka raka Ahmad har shabewa sannan suka dawo,
tuni sha d'aya tayi shiyasa kowa ya nufi gida.
Yauma da dare kamar jiya haka Ummi ta tashi yaranta,
sai k'arfe uku Rahma ta tuk'a musu tuwon shinkafa dama kuma Raihana tayi musu miyar zogale tun da dare.
to yau Saifuddeen ya d'anci mai d'an yawa kana yasha tea,
suna gama sahur din ya shiga wonka kafin ya fito anyi assalatu,
so alwala yayi tasa Hayatudden a a gaba suka tafi,
su Ummi kuma sukayi nasu a gida.
Ana idar da salla ya fara azkar nashi sai da ya gama sannan ya shiga suka gaisa da Ummi kana ya bata 5k d'innan yace ta sama musu asusu na daban ta rink'a sasu,
ita kam Ummi tayi mmkin yawan kudin to ganin yana sauri Salisu na jiranshi yasa ta barshi ya tafi sai ya dawo suyi mgna.
Suna isa Salisu ya sauk'eshi a bakin masallacin bakin kasuwan,
shi kuma ya wuce kabo-kabonshi.
shi kuwa Saifuddeen cikin masallacin ya shiga kamar jiya yayi baccin awa d'aya da rabi kana yana farkawa yayi Al'wala yayi walaha raka'a biyu sannan yayi addu'o'inshi kafin ya fito ya nufi cikin kad'uwa.
Yana shiga kai tsaye dilansu na leda ya shiga inda ya samu mutun biyu a gabanshi dole yabi layi,
bayan an basu shima aka bashi na 60k Lamar na jiya kenan k'arfe 10:00 Am dai-dai suka bashi nashin,
with full confidence ya fara bin layi-layi shago-shago lungu da sak'o yana raba musu suna bashi kud'in na jiya, 1:35 pm ya gama rabawa da yake kusan fiye da rabin kasuwar duk a wurin baba bello suke sayan ledan to shiyasa yake dad'ewa yana yawata kasuwan da k'afa tunda shi bashi da keke kamar baba bello,
yana gamawa yazo ya had'a lissafin kud'in ya samu dubu settin da bakwai da dari biyu, cikin aminci ya basu 60k d'insu sannan ya adana ribarshi a jikinshi godiya yayi musu bayan an rubuta ya dawo da kud'in na jiya,
tafiya yake yana nazari shifa gani yakeyi kamar kyauta suke bashi kud'in duk da ko azabar nauyin kwalin da yake azawa a k'afad'anshi na dama aikine mai matuk'ar wuya ga yawo cikin rana har ji yake k'afafunshi suna yum-yum dan azaban rana da nauyin kayan da yake azawa a kafad'anshi.
Ganin azahar ta kawo kai yasa ya zauna ya d'an huta dan yana jin kafad'arshi na mishi ciwo ga zafin ranan da yabi sai yake jin wani irin azabebben k'ishi ,
ganin an kira salla yasa ya mik'e yaje yayi al'wala kana ya shiga sahu,
bayan an idar ne ya mik'e a gajiye yana tafiya a hankali yaje ya karb'i omo dasu sabulu,
sai kuma ya zage da talla dan yanada burin ya maida Raihana da Raliyya makaranta in kes dai ace sun gama koda d'an Secondary school,
yana kuma fatan ya ink'anta karatun Hayatuddeen da Faruq da Adam kuma yana fatan Allah ya hanasu sake tsammatan abinda zasuci daga wurin wani.
Da wannan tunanin ya zage yaketa yawa tawa cikin ikon Allah ranar ribar 1,200 ya samu.
Ganin ya fara ganin jirine ya sashi neman inuwa ya zauna saida ya huta sannan ya maida sauran omon.
ganin hud'u da rabi tayi sai yaje shagon ba mishkila gero ya auna mudu shida sai wake mudu shida sai sugar mudu d'aya da rabi,
daga nan yaje ya sayi mai k'aramin galam sai ya saya musu lemu da ayaba da kankana,
A tak'aice dai ya kashe dubu uku d'ari biyun nan sai dubu biyar ya bari su kuma na sawa a asusune.