Sashe 99
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Yanzu zan kawo miki Momy na mantane wlh" ya faɗa da sauri kuma ya ɗauki muƙullin motarsa ya fita daga ɗakin suka kusa yin karo da Lawan, Autan Hajiya Binta a Maza ya taho hannu biyu riƙe da Tab yana buga game kamar wani yaro ƙarami yayi diri diri shi bai kauce ba be kuma matsa bayaba. Haushi ya ƙume Ahmad, ga sauri yanayi a fusace yace masa
"Ni zan kauce maka ka wuce kenan?"
Lawan ɗin yayi muimui da baki kafin ya raɓe gefe, Ahmad yayi ƙwafa ya wuceshi dan yana da abinyi yanzu amma tabbas se koma ta kansa wannan rainin da yaron ya ɗauko baze zuba Ido ya barshi ya tashi a haka ba kamar sauran Yaran gidan idanba haka fa Zayyad da yake ƙarami a gidan duka shima haka ze taso da Tarbiyyarsu, Matan tasu rashin kunyar da sauƙi da wuya suyiwa Mazan sedai a tsakaninsu amma su waɗannan da suke tashi yanzu shida Mu'allim jin kansu suke daidai dai da uban kowa daman Salim Da Faisal sun rigada sun ƙafura tuntuni.
Ledar Hijaban ya ɗauka, guda goma ne ya bawa Fatima ɗaya ya wuce ciki a tsakar gida suka ci karo da Hajiya idanuwanta akan Ledar hannunsa tamkar zata huda tashiga taga abinda yake ciki haka take kallon Ledar ko gaisuwar da yake mata bataji ba balle ta amsa dan haka yayi gaba shina ya kusa shiga ɗakin Momy ya jiyota tana cewa
"Au Amadu, kana kallona ka wuce ko gaisheni ba zakayi ba"
"Ya fa gaisheki Hajiya kinata kallon Ledar hannunsa" Sarah ta bata amsa aiko ta kai mata duka ta kauce nan ta shiga sababi tana cewa
"Dan uwarki dake nake? Ko kin koma Amadu bansani ba shegiya me shegen shishshigi a abinda ba'a sakata ba kuma da idon ubanki kika ga ina kallon kayan hannunsa?"
Hajiya Rabi na daga cikin falonta inda ta idar da sallah tana lazumi hayagagar Hajiyar ya na neman ya raba mata hankali dan ta jikin window ta take tsaye, rabon ayi yasa ta leƙa kaɗan tacewa Hajiyar tayi haƙuri tayi shiru nan ta juya kanta ta dirar mata cin mutunchi da gorin da bata gajiya dayi mata.
"Itama Rabi banda neman magana waya kaita tanka mata? Yau Allah ya taimakemu tun safe kunnuwanmu shiru rabon dai se an mana na dare" Momy ta faɗa sanda Ahmad ya dire ledar hannunsa a ƙasa ta jata gabanta tana fito da kayan ciki. Hijabai tara ta gani, ta fara ciresu daga ledojinsu tana duba yadin, fuskarta a washe tace
"Kaji laushin yadin nan ga kyau a ido waye zece ba Ɗan Egypt ɗin bane?"
Ahmad ya ja guda yana dubawa yace
"Wai daman ba order kikayo ba?"
"Inafa order? Yadin gidane wlh a gurin Hajiya Hauwa nake ganin ire irensu harta bani guda biyu naji daɗin ɗinkin sosai yanda yake zama a jiki be matse ba kuma baya bin Jikin mutum ga matured style na hannaye nima na ɗauka na wajene tace mun wata Matace takeyinsu sunanta *MARYAM FAROUK amma anfi saninta da UMMU-MAHEER (07061838488) indai Hijabi ake magana daga Normal Hijab me Hannu ko Mara hannu, Jilbab, ko two pieces Gown da V hijab to idan ka sameta an rufe magana, ga yadikan da take amfani dasu ka gansu nan dai ga kyau ko ba'a faɗa ba zasuyi quality sannan ga sauƙi shiyasa nace ta bani number ta kawai na siya na huta da jigilar siyowa daga Egypt ɗin nan kuma babu lallai mutum ya samu yanda yake so".
"Gaskiya sunyi kyau sosai nima idan zan siyi Hijabs zaki bani number ta" yayi suɓutar baki, Momyn tayi dariya tace
"Wato kowacece wannan bata kama da sauƙi ba, to Allah ya nuna mana lokaci dama ai ita zan bawa order Hijaban Lefenka da Jafar, ni guda tara ma na gani inaga tayi kuskuren lissafi ne"
Ahmad ya shafa kansa cikin kunya yace
"Aa Momy ni na ɗauka ɗayan"
"To seka turamun kuɗina kuwa, ina zakaje haka naga kasha kwalliya da daren nan ko gurin yar tawa zakaje?" Ta sake faɗa tana kallonsa daga sama zuwa ƙasa ganin harda hula ya kafa, seya juya ya nufi ƙofa yana cewa
"Kai Momy, nidai sena dawo kiyimun addu'a"
"Allah ya tsare ya dawo dakai lafiya"
"Amin Momyna" ya amsa daga nan ya fice da sauri yana jin Hajiya na kwala masa kira yaƙi tsayawa dan ɓata masa lokaci kawai zatayi ya sani.
Daidai inda ya saukesu waccen ranar yayi parking, akwai wutar Nepa ga kuma fitilun Solar a cikin layukan dan haka hankali kwance ya ringa kutsawa harya isa ƙofar gidansu. A kan Dakali dake ƙofar gidan ya zauna ganin gurin fes yake babu datti kamar yanda Dandamalin Ƙofar gidan yake har zuwa cikin soron da shima yake shafe da sumunti da fasassun Tiles ko ina tas. Hangen yaron daze tura yayi masa sallama da ita yakeyi sega wani Saurayi da zasu iyayin Sa'anni koya girme masa da kaɗan ya fito daga gidan yana ganinsa ya fahimci ɗan gidannan kamarsu ɗaya dasu sedai shima be kaita haske ba amma yafi waccen Yayar tasu haske.
Ya miƙawa saurin daya dakata hannu sukayi musabaha.
"Baffa za'ayi maka sallama dashi?" Saurayin ya faɗa dan dukda ya ganshi Matashi be kawo gurin Afeeya yazo ba tunda yasan samarinta a waya suke kiranta da wuya a aiko yaro sallama kuma ya dade a cikin gida harya fito beji tayi waya ko tayi zancen zatayi baƙo ba.
Ahmad kuwa ji yayi kamar ya masa wata tunasarwa daya manta. Tabbas da mahaifinta ya kamata ya fara magana ya nemi izinin nemanta kamar yanda Shari'a ta tanadar dan haka yayi murmushi yace masa Eh.
Saurayin ya juya, a bayan rigar Jessy dake jikinsa yaga an rubuta JAY amma bata Arsenal bace ta club ɗin unguwa ce amma ya tabbatar sunan daya gani baya rasa ace Fan ɗin Jafar ɗinsa ne. Saurayin ya fito ya sanar masa da Baffan yana zuwa daga nan ya wuce inda zashi, babu jimawa Sega wani Dattijon ya fito a ƙalla zeyi shekaru sittin da ɗoriya yana da matsakaicin jiki tamkar dai Ahmad ɗin, babu wata shahararriyar kama tsakaninsa dasu Fatiman seta jini da kuma fatarsa me duhu da Anty Sauda da saurayin da yaji ya ambata da Jafaru suka ɗauka.
"Samari kaine Jafaru yace kanaa sallama dani?" Baffan ya faɗa. Ahmad ya zube a ƙasa kamar ze kwanta ya shiga gaisheshi Baffa se cewa yake ya tashi karya ɓata kayansa amma ya ƙi tashin. Bayan gaisuwar shiru ya biyo baya, Baffa na kallonsa da sauraron jin me yake tafe dashi Ahmad kuma nauyin Dattijon da kunya irin tasa yasa ya kasa magana seda Baffan yace
"Inajinka samari lafiya dai ko? Fuskar taka ta kwantamun gaskiya ko maganar gyaran Mota ce?"
"Aa Baffa, bamu taɓa haɗuwa bama. Daman wata yarinya na gani kuma akace a nan gidan take, shine nake so nayi tambaya naji ko da maganar wani a ciki" ya tattara ƙarfin guiwa ya faɗa. Baffa yayi murmushi Ahmad ɗin kuma ya burgeshi domin ya nuna shi ɗin mai tarbiyyane kuma yasan shari'a. Gyara tsayuwa Baffa yayi yana kallonsa yace
"Madallah, naji daɗi kwarai da kayi abinda ya kamata kuma ina mai sanar dakai Yarinya tana da manema amma har yanzu dai babu wanda magana me ƙarfi ta ƙullu tsakaninsu dan haka kana da dama ka gwada taka sa'ar idan da rabo se Allah yasa a dace, amma Yaya sunaka? Kuma kai ɗin ɗan garin nan ne ko Ina?"
Daɗi ya kama Ahmad jin amsar Baffa ya sake sunkuyar da kai yana murmushi yace
"Eh, ni ɗan garin nan ne. Mahaifina sunansa Alhaji Audu Bechi sunana Ahmad"
"Alhaji Audu Bechi dai dana ke jin sunansa?" Baffa ya faɗa cikin mamaki, Ahmad ya gyaɗa kai cikin tabbatarwa yace
"Eh shi, ni Ɗansa ne".
"Toh, toh masha Allah, amma yaro ita Mamana ka gani ko kuwa wata ce tazo gurinta kaga ta shiga nan gidan?" Baffa ya sake tambayarsa dason tabbatarwa domin sunan Mahaifinsa daya kira ya sakashi kokonton Anya wanda ya fito daga babban gida kamar wannan ze biyi yar Talaka irinsa yace yana sonta da aure?
"Sunanta dai Fatimaz tareda yayarta Anty Sauda na gansu" Ahmad ya bashi amsa wannan ya tabbatar masa dagaskw ita Fatiman dai ya gani. Numfashi yaja kafin ya fara magana yana cewa
"Tabbas Yatace wacce ka gani, sedai kuma a matsayi da irin gidan daka fito bana tsammanin zaka zo gida kamar nawa kace kaga yarinya kana so ba kuma da aure, dan haka ina roƙonka da kayi haƙuri idan wata sharholiya ce ta kawoka gurinta ka tafi domin nasan maganar Aure ba zata taɓa yuwuwa a tsakaninku ba saboda banbanci matsayi da kuke dashi, a zamanin nan da Masu kuɗi suke kyamatar talakawa bana zatom koda har zuciyarka da gaske kake son Fatima Iyayenka zasu goyi bayan daka Aureta kadai ga gidansu ka kuma ganni nine mahaifinta ni ba kowa bane sana'ar gyaran Mota nakeyi da ita nake cida Iyalina na shayar dasu kar wani kyau ko zubin Halittarta ya ruɗeka, ni bana son tashin hankali da abinda ze janyo Kace nace, a Ƙasar nan babu wanda besan sunan Mahaifinka ba bana tsammatar mutum kamar shi ze yarda ya haɗa zuri'a da Talaka kamata".
Cikin mutuwar jikin da maganganun Malam Hafizu Ahmad ya buɗe baki dakyar yace
"Amma Baffa banji daɗin da kayi mun zaton wani abu na daban ya kawoni gurin Fatima ba aure ba, dukda kaima kana da naka uzurin amma Baffa da Mai kuɗi da talaka duk Allah yayisu babu wanda yafi wani a gurinsa se wanda yafi tsoronsa da kiyaye dokokin Allah. Sannan babu wata Aya ko Hadisi ko shari'a data haramta Aure tsakanin Mai kuɗi da Talaka, kuma Baffa Mahaifina baya daga cikin irin waɗannan mutanen da suke kyamatar wani saboda banbancin matsayin abun duniya ko Mulki, a auratayya bayan Ingancin Asali da Tarbiyyar gidan da aka nemo Auran muddin Ma'aurin yana so bashida damuwa baze hana ba. Nine Ɗa na goma sha ɗaya a jerin Maza, yayyena Tara sunyi aure ɗayane beyi ba a cikinsu kuma harda me mata uku sannan kowa da irin gidan da yayo aure babu kuma wanda Alhajinmu ya taɓa hanawa ya auri Matar da yake so ba na tabbatar kuma ba za'a fara a kaina ba In sha Allahu".
"Ni zan kauce maka ka wuce kenan?"
Lawan ɗin yayi muimui da baki kafin ya raɓe gefe, Ahmad yayi ƙwafa ya wuceshi dan yana da abinyi yanzu amma tabbas se koma ta kansa wannan rainin da yaron ya ɗauko baze zuba Ido ya barshi ya tashi a haka ba kamar sauran Yaran gidan idanba haka fa Zayyad da yake ƙarami a gidan duka shima haka ze taso da Tarbiyyarsu, Matan tasu rashin kunyar da sauƙi da wuya suyiwa Mazan sedai a tsakaninsu amma su waɗannan da suke tashi yanzu shida Mu'allim jin kansu suke daidai dai da uban kowa daman Salim Da Faisal sun rigada sun ƙafura tuntuni.
Ledar Hijaban ya ɗauka, guda goma ne ya bawa Fatima ɗaya ya wuce ciki a tsakar gida suka ci karo da Hajiya idanuwanta akan Ledar hannunsa tamkar zata huda tashiga taga abinda yake ciki haka take kallon Ledar ko gaisuwar da yake mata bataji ba balle ta amsa dan haka yayi gaba shina ya kusa shiga ɗakin Momy ya jiyota tana cewa
"Au Amadu, kana kallona ka wuce ko gaisheni ba zakayi ba"
"Ya fa gaisheki Hajiya kinata kallon Ledar hannunsa" Sarah ta bata amsa aiko ta kai mata duka ta kauce nan ta shiga sababi tana cewa
"Dan uwarki dake nake? Ko kin koma Amadu bansani ba shegiya me shegen shishshigi a abinda ba'a sakata ba kuma da idon ubanki kika ga ina kallon kayan hannunsa?"
Hajiya Rabi na daga cikin falonta inda ta idar da sallah tana lazumi hayagagar Hajiyar ya na neman ya raba mata hankali dan ta jikin window ta take tsaye, rabon ayi yasa ta leƙa kaɗan tacewa Hajiyar tayi haƙuri tayi shiru nan ta juya kanta ta dirar mata cin mutunchi da gorin da bata gajiya dayi mata.
"Itama Rabi banda neman magana waya kaita tanka mata? Yau Allah ya taimakemu tun safe kunnuwanmu shiru rabon dai se an mana na dare" Momy ta faɗa sanda Ahmad ya dire ledar hannunsa a ƙasa ta jata gabanta tana fito da kayan ciki. Hijabai tara ta gani, ta fara ciresu daga ledojinsu tana duba yadin, fuskarta a washe tace
"Kaji laushin yadin nan ga kyau a ido waye zece ba Ɗan Egypt ɗin bane?"
Ahmad ya ja guda yana dubawa yace
"Wai daman ba order kikayo ba?"
"Inafa order? Yadin gidane wlh a gurin Hajiya Hauwa nake ganin ire irensu harta bani guda biyu naji daɗin ɗinkin sosai yanda yake zama a jiki be matse ba kuma baya bin Jikin mutum ga matured style na hannaye nima na ɗauka na wajene tace mun wata Matace takeyinsu sunanta *MARYAM FAROUK amma anfi saninta da UMMU-MAHEER (07061838488) indai Hijabi ake magana daga Normal Hijab me Hannu ko Mara hannu, Jilbab, ko two pieces Gown da V hijab to idan ka sameta an rufe magana, ga yadikan da take amfani dasu ka gansu nan dai ga kyau ko ba'a faɗa ba zasuyi quality sannan ga sauƙi shiyasa nace ta bani number ta kawai na siya na huta da jigilar siyowa daga Egypt ɗin nan kuma babu lallai mutum ya samu yanda yake so".
"Gaskiya sunyi kyau sosai nima idan zan siyi Hijabs zaki bani number ta" yayi suɓutar baki, Momyn tayi dariya tace
"Wato kowacece wannan bata kama da sauƙi ba, to Allah ya nuna mana lokaci dama ai ita zan bawa order Hijaban Lefenka da Jafar, ni guda tara ma na gani inaga tayi kuskuren lissafi ne"
Ahmad ya shafa kansa cikin kunya yace
"Aa Momy ni na ɗauka ɗayan"
"To seka turamun kuɗina kuwa, ina zakaje haka naga kasha kwalliya da daren nan ko gurin yar tawa zakaje?" Ta sake faɗa tana kallonsa daga sama zuwa ƙasa ganin harda hula ya kafa, seya juya ya nufi ƙofa yana cewa
"Kai Momy, nidai sena dawo kiyimun addu'a"
"Allah ya tsare ya dawo dakai lafiya"
"Amin Momyna" ya amsa daga nan ya fice da sauri yana jin Hajiya na kwala masa kira yaƙi tsayawa dan ɓata masa lokaci kawai zatayi ya sani.
Daidai inda ya saukesu waccen ranar yayi parking, akwai wutar Nepa ga kuma fitilun Solar a cikin layukan dan haka hankali kwance ya ringa kutsawa harya isa ƙofar gidansu. A kan Dakali dake ƙofar gidan ya zauna ganin gurin fes yake babu datti kamar yanda Dandamalin Ƙofar gidan yake har zuwa cikin soron da shima yake shafe da sumunti da fasassun Tiles ko ina tas. Hangen yaron daze tura yayi masa sallama da ita yakeyi sega wani Saurayi da zasu iyayin Sa'anni koya girme masa da kaɗan ya fito daga gidan yana ganinsa ya fahimci ɗan gidannan kamarsu ɗaya dasu sedai shima be kaita haske ba amma yafi waccen Yayar tasu haske.
Ya miƙawa saurin daya dakata hannu sukayi musabaha.
"Baffa za'ayi maka sallama dashi?" Saurayin ya faɗa dan dukda ya ganshi Matashi be kawo gurin Afeeya yazo ba tunda yasan samarinta a waya suke kiranta da wuya a aiko yaro sallama kuma ya dade a cikin gida harya fito beji tayi waya ko tayi zancen zatayi baƙo ba.
Ahmad kuwa ji yayi kamar ya masa wata tunasarwa daya manta. Tabbas da mahaifinta ya kamata ya fara magana ya nemi izinin nemanta kamar yanda Shari'a ta tanadar dan haka yayi murmushi yace masa Eh.
Saurayin ya juya, a bayan rigar Jessy dake jikinsa yaga an rubuta JAY amma bata Arsenal bace ta club ɗin unguwa ce amma ya tabbatar sunan daya gani baya rasa ace Fan ɗin Jafar ɗinsa ne. Saurayin ya fito ya sanar masa da Baffan yana zuwa daga nan ya wuce inda zashi, babu jimawa Sega wani Dattijon ya fito a ƙalla zeyi shekaru sittin da ɗoriya yana da matsakaicin jiki tamkar dai Ahmad ɗin, babu wata shahararriyar kama tsakaninsa dasu Fatiman seta jini da kuma fatarsa me duhu da Anty Sauda da saurayin da yaji ya ambata da Jafaru suka ɗauka.
"Samari kaine Jafaru yace kanaa sallama dani?" Baffan ya faɗa. Ahmad ya zube a ƙasa kamar ze kwanta ya shiga gaisheshi Baffa se cewa yake ya tashi karya ɓata kayansa amma ya ƙi tashin. Bayan gaisuwar shiru ya biyo baya, Baffa na kallonsa da sauraron jin me yake tafe dashi Ahmad kuma nauyin Dattijon da kunya irin tasa yasa ya kasa magana seda Baffan yace
"Inajinka samari lafiya dai ko? Fuskar taka ta kwantamun gaskiya ko maganar gyaran Mota ce?"
"Aa Baffa, bamu taɓa haɗuwa bama. Daman wata yarinya na gani kuma akace a nan gidan take, shine nake so nayi tambaya naji ko da maganar wani a ciki" ya tattara ƙarfin guiwa ya faɗa. Baffa yayi murmushi Ahmad ɗin kuma ya burgeshi domin ya nuna shi ɗin mai tarbiyyane kuma yasan shari'a. Gyara tsayuwa Baffa yayi yana kallonsa yace
"Madallah, naji daɗi kwarai da kayi abinda ya kamata kuma ina mai sanar dakai Yarinya tana da manema amma har yanzu dai babu wanda magana me ƙarfi ta ƙullu tsakaninsu dan haka kana da dama ka gwada taka sa'ar idan da rabo se Allah yasa a dace, amma Yaya sunaka? Kuma kai ɗin ɗan garin nan ne ko Ina?"
Daɗi ya kama Ahmad jin amsar Baffa ya sake sunkuyar da kai yana murmushi yace
"Eh, ni ɗan garin nan ne. Mahaifina sunansa Alhaji Audu Bechi sunana Ahmad"
"Alhaji Audu Bechi dai dana ke jin sunansa?" Baffa ya faɗa cikin mamaki, Ahmad ya gyaɗa kai cikin tabbatarwa yace
"Eh shi, ni Ɗansa ne".
"Toh, toh masha Allah, amma yaro ita Mamana ka gani ko kuwa wata ce tazo gurinta kaga ta shiga nan gidan?" Baffa ya sake tambayarsa dason tabbatarwa domin sunan Mahaifinsa daya kira ya sakashi kokonton Anya wanda ya fito daga babban gida kamar wannan ze biyi yar Talaka irinsa yace yana sonta da aure?
"Sunanta dai Fatimaz tareda yayarta Anty Sauda na gansu" Ahmad ya bashi amsa wannan ya tabbatar masa dagaskw ita Fatiman dai ya gani. Numfashi yaja kafin ya fara magana yana cewa
"Tabbas Yatace wacce ka gani, sedai kuma a matsayi da irin gidan daka fito bana tsammanin zaka zo gida kamar nawa kace kaga yarinya kana so ba kuma da aure, dan haka ina roƙonka da kayi haƙuri idan wata sharholiya ce ta kawoka gurinta ka tafi domin nasan maganar Aure ba zata taɓa yuwuwa a tsakaninku ba saboda banbanci matsayi da kuke dashi, a zamanin nan da Masu kuɗi suke kyamatar talakawa bana zatom koda har zuciyarka da gaske kake son Fatima Iyayenka zasu goyi bayan daka Aureta kadai ga gidansu ka kuma ganni nine mahaifinta ni ba kowa bane sana'ar gyaran Mota nakeyi da ita nake cida Iyalina na shayar dasu kar wani kyau ko zubin Halittarta ya ruɗeka, ni bana son tashin hankali da abinda ze janyo Kace nace, a Ƙasar nan babu wanda besan sunan Mahaifinka ba bana tsammatar mutum kamar shi ze yarda ya haɗa zuri'a da Talaka kamata".
Cikin mutuwar jikin da maganganun Malam Hafizu Ahmad ya buɗe baki dakyar yace
"Amma Baffa banji daɗin da kayi mun zaton wani abu na daban ya kawoni gurin Fatima ba aure ba, dukda kaima kana da naka uzurin amma Baffa da Mai kuɗi da talaka duk Allah yayisu babu wanda yafi wani a gurinsa se wanda yafi tsoronsa da kiyaye dokokin Allah. Sannan babu wata Aya ko Hadisi ko shari'a data haramta Aure tsakanin Mai kuɗi da Talaka, kuma Baffa Mahaifina baya daga cikin irin waɗannan mutanen da suke kyamatar wani saboda banbancin matsayin abun duniya ko Mulki, a auratayya bayan Ingancin Asali da Tarbiyyar gidan da aka nemo Auran muddin Ma'aurin yana so bashida damuwa baze hana ba. Nine Ɗa na goma sha ɗaya a jerin Maza, yayyena Tara sunyi aure ɗayane beyi ba a cikinsu kuma harda me mata uku sannan kowa da irin gidan da yayo aure babu kuma wanda Alhajinmu ya taɓa hanawa ya auri Matar da yake so ba na tabbatar kuma ba za'a fara a kaina ba In sha Allahu".