← Book details Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 129 OF 137

Sashe 129

Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Wayarta tayi ƙara, yana ganin yanda ta zabura ta duba in beyi ƙarya ba har sautin ajiyar zuciyar da tayi ya jiyo. Suka haɗa ido sanda ta saci kallonsa kafin ta ɗaga wayar. Zuciyarsa ta harba, daga yanayinta da yanda take magana a wayar dukda bajin me take cewa yakeyi ba tsabar yanda tayi ƙasa da murya ya gane da Namiji take maganar. Kansa ya ɗauki zafi, har wani sara masa yakeyi idanuwansa sukayi jajir lokaci ɗaya saboda wutar kishin data tashi ta fara ci balbal a zuciyarsa. Be san ta gama wayar ba seda yaga tana Ƙoƙarin saka cajin wayar ta ajikin cajar motar. Murya a kausashe da irin sautin da bata taɓa jinsa dashi ba ya kira sunanta kafinyace

"Ni ba shashashan Namiji bane da kina zaune tareda ni wani ze kiraki a waya ki ɗauka, this should be the last time da zaki kwatanta wani abu kamar haka. Wlh kika sake sena fasa wayar idan yaso naga da abinda zaki cimun fuska kiyi magana da wani Namiji".

Tsabar yanda maganarsa ta shigeta har karkarwa jikinta ya ɗauka, tunani takeyi daman Ahmad ya iya faɗa irin haka? Yanda ya juye mata lokaci ɗaya ya firgitata ga speed daya ƙarawa motar yanda kasan zasu tashi sama.

"Kayi haƙuri" ta faɗa bakinta na rawa. Har suka isa Kano kuma be sake ce mata komai ba, a bakin layinsu da suka isa ya faka be kulata ba ya fita ya samu yara ya buɗe booth suka kwashe mata kayanta. Be bata fuskar da zata sake masa wata magana ba, a wajen motar ma ya tsaya har seda ta sauka kafin yaja yayi tafiyarsa ya barta da bin bayansa da kallo.
A sanyaye ta isa gida kafin ta shiga dai tayi ƙoƙarin daidaita nutsuwarta saboda gudun tambayar meya sameta. Ta tarar da Anty Sauda da yaranta, ganinsu yasa ta sake sakin ranta musamman kuma da sahibul Ƙalbinta ya kirata ya mata fatan sa'a akan Jarabawar da suka gama yace zasuyi magana idan ta isa gida. Wannan birkicewar ta Ahmad ce ta jirkitata amma tana shiga gida ta manta da babinsa ta shiga sabogogi sedai lokaci lokaci yakan faɗo mata, yanda ya fututtuke se taji kamar Jay yana sababi, daman ance masu haƙuri basu iya fushi ba yau kuwa gashi ta tabbatar.

Ahmad kuwa seda yayi dagaske kafin ya danne abinda ya ringa cin zuciyarsa, yana da kishi matuƙa musamman akan abinda yake so kamar Fatima. Koda yake binta yana lallaɓata dan yasan kawai ra'ayinsa ne batayi bawai wani saurayi ne da ita daban da yasa take ƙinsa saboda shi ba. Yasan bata double dating, shiyasa ya nace yake ta roƙon Allah yana kuma ƙara cusa kansa gurinta amma yanzu ya fahinci ta samu wani saurayin da take ra'ayi shiyasa harta iya ci masa fuska ta ringa waya dashi a gabansa shi ga sakarai wato bazeji komai a ransa ba.

Seda aka kwana biyu da ɗakkota da yayi be sake kiranta ba, dan ya yanke dole ya koyawa zuciyarsa haƙuri da ita tunda har ya fahimci da wani bayan shi yanzu komai yana iya faruwa kenan. Da safe ranar Asabar kwana biyu kenan da dawowar tata yana kwance a ɗakinsa se gashi ta kirashi. Ya ringa kallon wayar kamar wanda yayi loosing memory saboda ya kasa yarda Fatima ce take kiransa da karan kanta yau. Rejecting yayi kafin yabi bayan kiran duk da zuciyarsa nace masa karya amsa ya bar wayar tayi ringing ta gama harta sake kira dan ya tabbatar da gaske shi take kira ba tuntuɓen number tayi ba.

"Ina kwana?" Ta faɗa a sanyaye bayan da yayi mata sallama ta amsa. Ya amsa gaisuwar yana jin tamkar ya taka rawar murna, dahgaske kenan idan mutum yaja aji za'a mutuntashi tunda gashi fushin kwana biyu ya juyo masa da hankalin Fatima.
"Kayi haƙuri akan abinda ya faru ranar nan banyi da wata niyya ba" ta sake faɗa a sanyaye. Daɗi ya sake kamashi, har tasan ta kirashi kenan ta bashi haƙuri ai kuwa akwai haske a cikin tafiyar. Ya wani mula yace
"Babu komai kawai dai na gaya miki idan kika sake sena fasa wayar tunda bazan iya fasa miki baki ba"
"Ai dai nace kayi haƙuri" ta sake nanatawa yace
"Na haƙura na kuma yafe miki Alhakina da kika ɗauka kika sa nayi fushi dake".

"Uhm" kawai tace, suka ɗan taɓa hira kafin sukayi sallama bayan yace mata zeje da yamma tace tana gidan Anty Sauda ya sameta a can dan kwana zatayi.

"Toh ko kefa? Nifa harga Allah zancen wani Ɗan Ball be kwantamun a rai ba. Haka kawai zaki kwasarwa kanki abinda ze saka miki ciwon rai idan ya aureki ɗin ma kenan. A matsayinki nawa Afeeyah zakice zaki auri world class Celebrity? Ai ɗagen yayi yawa, irin waɗannan ai ba kowacce mace ba, kuma duk ma ba wannan ba na tabbatar wlh fuskarki ce kawai ta ruɗeshi, babu tabbacin idan yasan wacece ke ya yarda ya aureki a haka gara miki Ahmad ɗin. Mutumin nan ga Hankali, nutsuwa, mutunchi, karamchi uwa uba yana matuƙar sonki kuma ya sanki ciki da bai yasan Mahaifanki a hakan kuma yace yaji ya gani yana sonki ze aureki na rasa wace masifa ce tasa bakya son Bawan Allahn nan Afeeyah wlh in guje miki kiyi nadanar da ba zata amfana miki komai ba a gaba" Anty Sauda wadda ita ta tursasata kiran Ahmad bayan data shaida mata abinda ya faru tsakaninsu ta faɗa.

Afeeyah ta zumɓura baki, kafin tayi magana wayarta ta shiga ƙara, ringing tune data sakawa Jay ne dan haka ta miƙe da sauri da wayar a hannunta ta shige ɗaki Anty Sauda ta rakata da ido tana cewa
"Idan kina da rabo Allah ya ganar dake amma wlh nasan wannan Jay yake kowa yaudararki yakeyi ba auranki zeyi ba gara tun kina da sauran dama kiyi amfani da ita amma ba takanki zanbi ba, Baffa zan samu tun wuri asan abinyi baze yuwu shekara biyu ki gama yaudare bawan Allah kizo kice ba zaki aure shi ba" taja wayarta ta shiga kiran Baffansu sedai wayarsa a kashe. Tayi ƙwafa a fili ta sake cewa
"Har gidan zanje, gara ko auran dole ne miki tunda baki da hankali" ita dai Afeeyah na kan gado tana malele kuwa Jay na kasheta da kalaman Love, tunda suka shirya ta manta komai. Hatta maganar dake ta azalzalar zuciyarta ta mahaifiyarsa bata tayar ba tama manta da batun ta sake zama daram akan Alƙawarurrukan madarar ƙaunar da yace ze shayar da ita idan sukayi aure. Ya mata Alƙawari nan da watanni shida zezo Nigeria musamman saboda ita, ya kuma ce mata zuwan da zeyi zeje ya gaida Mahaifinta daga nan iyayensa suzo dan ya rigada ma harya gayawa Yayansa maganarta shima shirin Aure yakeyi tare za'a haɗa da nashi dan haka ta fara duk wani shirinta da idan yazo tana iya yuwuwa daga tambaya taji an ɗaura musu aure kawai sedai taji ana fito kibi Mijinki.

Ranar tayi dariyar maganarsa yace tasaka wasa zata gani da gaske yakeyi, Alhajinsu bashida wasa ko yau yace masa zeyi aure muddin ya yarda da inda ya nemo auran magana ta ƙare tambaya kawai za'aje ayo. Wannan tasa ta yanke shawarar sanar da maganarsa a gida tunda wuri ba wai se rana tsaka ba, ta fara takan Anty Sauda domin itace tsanin da ze kaita gasu Baffa. Muddin tayi na'am da abin tasan komai ze zo da sauƙi sedai daga yanda ta karɓi maganar tasan ko zata yarda se an yi ƙwaibai da ita dan tamkar Badar itama Ahmad ya lashe mata zuciya sonsa suke nasa son abinda ze taɓa shi. Daga ce mata sunyi faɗa tace seta kirashi ta bashi haƙuri idan ba haka ba ta gayawa Baffa ta samu wani saurayi yana hure mata kunne harta kori Ahmad ta masa wulaƙanci shiyasa ta kirashi.

****************
Hajiya Binta zaune kan carpet tana zubawa Alhaji Audu faten Accar da tayi masa saboda tana da buƙatu yau da kanta ta tsaya ta masa girki me kyau ta kashe gayu da wata kamfalarta shadda ta saka daham, lallen bikin da aka mata tun yau litinin yayi raɗau a hannayenta da Ƙafa dukda na Salatif ne me yankan Siga amma da yake fatar da sauran Armashinta ya mata kyau. Humrar da akayiwa Amarya Hafsatu ta bulbula abinta ƙamshin har hawa kai yakeyi dan seda Alhajinya kunna fanka bayan Ac dake falon saboda Atishawar da turaren nata ya saka ya fara jerawa.

Hira take masa wadda duk labarin irin tsaruwar gidan Hajiya ƙaramar take zayyana masa. Jiya su Turai suka dawo daga jere, dakyar da roƙon Allah ma ta yarda ta zauna dan cewa tayi da da ita za'aje.
"Wannan wane irin abune babu kunya kawai Binta ki bimu se a ganki tsalam ace ga uwar Amarya a ina kima taɓa ganin anyi haka? Ita Aisha data aurar da Yaya biyu gata uku wanne kika gani a ciki tajewa jere baku ne kuke zuwa ba se kece zakice se kinje salon ki zubarwa da yarinya ƙima tun bata kai ga shiga cikinsu ba? Abujar ce baki taɓa zuwa ba ko kuwa ance za'a rufe shigarta ne idan bakije yanzu ba?" Turai ta ringa zazzaga mata bala'i dan lamarin Ƙawar tata ya fara kaita bango.
Chapter 129 · 0% Book details