Sashe 73
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Bara'atu da taja Hijabi ta rufe fuska dan ta kasa riqe kukan daya zo mata qasa qasa takeyinsa tana share hawaye wato dai ranakun baqin cikinta basu qare a gidan Audu ba, maidota yayi ya qara sauke mata buhun hunan rashin mutunchin da be ida sauke mata a baya ba, da sauri ta dago kai jin abinda Bintan take cewa
"Kin ga ya dage dole mubi tsarin da aka kawo da farko amma tunda kin nemi a canza, idan kin yarda ni a bangarena a maimakon sharar dakina zaki ringa yimun Wankin kayan Yara ke ma seki fadi abinda zan ringayi miki a madadin taki sharar" ta qarasa tana doka murmushi kamar wawiya.
Kasa cewa komai tayi, ta kalli Bintan kafin ta kalli Audu tana jiran taji abinda zece se ji tayi yana cewa
"Babu maganan ta zabi abinda zaki mata, sharar dakinta ita tace ta yafe kar kiyi na dakinki kuma wannan da ba zatayi ba kika musanya mata" ya juya kan Bara'atu da tayi fakare tana sauraronsu yace
"Zaki ringayi mata wankin kayan yaran duk ranar da baki da girki, My decision is final" aka jefo turanci daga nan ya shige daki ya barsu zaune.
"Yanzu wasan ya fara yarinya" Binta ta fito mata a sak ta fada kafin ta miqe tana juya Mazaune tabi bayan Audu tana wata shaidaniyar dariya irin ta wanda ya nisa cikin lamarin duniya.
https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*PAGE 28*
Kwana tayi tana juyi duk motsi abinda ya faru daren jiyan seya fadomata zuciyarta tayi mata nauyi, idanunta banda radadi babu abinda sukeyi dalilin kukan data sha, Ta rasa a wanne matsayi zata ajiye Audu dan bata ta Binta kwata kwata ta gama sallama mata amma shi Audu fa?
Son zuciya ko kuwa qin gaskiya ne yake saka shi aikata abubuwan da yakeyi ko yaya? Me yasa duk hukuncinsa yake kasancewa na son zuciya kuma bisa goyon bayan rashin gaskiya?.
Rashin baccin da batayi ba cikin dare yasa ta makara, dakyar ta iya tashi tayi sallah kanta na bala'in sara mata ta koma ta sake kwanciya tana jin yaran na qu qunin Yunwa dan Zakariyya harya fara kuka gashi bata jiyo motsin Bintan ba alamarbata sakko ba balle ta dora abin kari, Audun m yau be leqa su da Asuba yaga ko sun tashi ba kamar yanda ya saba haka daya dawo wucewarsa daki yayi tunda fushi yake da ita kuma yau din Lahadi ce baya fita da wuri daman se qarfe sha biyun rana shiyasa Bintan ta qara samun damar tsula tsiyarta.
Abdullahi ta kira tace ya share tsakar gida ya wanke saboda hadari ya taso daren jiya ruwa be sauka ba se Iska ta taho da qura ita kuma ta daure ta hada ruwan wanka ta yiwa yaran kafin Hajiyar gidan ta gama qailularta ta basu abin kari. Tana cikin shiryasu ta jiyo hayagagar Binta ta san baze wuce da Abdullahi take ba. Cikin kayan Babannan ta samarwa Zakariyya wanda suka masa tace su zauna nan bari ta kawo musu abin karyawa ta zura Hijabinta tana qoqarinfita ta jiyo sallamar Bintan a qofar dakinta, tayi A'uziyya a zuciyarta domin Binta ta zarce shaidan kaidi, sanin Audu na gida kuma zata yuwu wani bala'in ta sake zuwa ta hada mata dan haka tayi saurin fita kafin ita ta shigo mata cikin dakin.
Faran faran tamkar babu wani mugun abu a ranta ta gaida Bara'atun ita dai daga lafiya ta gagara qara ce mata komai saboda zuciyarta gaba daya ma tsinkewa takeyi, ita dai kaf a karkararsu bata taba ji ko ganin Mace irin Binta ba, to ko daman wannan abin shine wayewar da ake fada? Idan kuwa hakane ta godewa Allah da ta kasance bagidajiya akan ta zamo daga cikin munafukai.
"Kuyi haquri na barku da yunwa ko? Bacci ne ya kwace mun yau, Bari in maza ko ruwan shayi ne a tafasa se a soya wainar qwai tunda muna da burodi" Binta ta fada tana murmushi. Cikin sanyi Bara'atu tace
"Babu komai ai" ta bata amsa a sanyaye daga nan Bintan ta juya tana murmushin da Allah kadai yasan ma'anarsa.
Kusan Minti goma tsakani Binta ta sake dawowa da qaton Fulas din ruwan zafi tun wanda Dada ta bata ne lokacin Amarcin da ake zuba musu ruwan zafi a ciki. Yana da girma ga riqe zafi shiyasa take jin dadinsa sosai.
"Sannu da aiki" ta fada sanda ta kabi Fulas din, Binta tayi murmushi ta koma kitchen ta sake kawo mata Farantin data Zubo faya fayen wainar qwai.
A babban Jug din da take hada musu shayi gaba daya ta zuba Madara da Milo da Sukari kadan kafinta tsiyaya Ruwan zafinta motsa, ta zubanata a kofi ta zubawa Abdullahi se ta qara ruwan sanyi akan sauran ta dan qara musu Madara da Milo sannan ta zubawa sauran Yaran.
Yanda suka rarumi Kofunan duk sunbata tausayi musamman Zakariyya da yake qaraminsu a ranta tace
"Wato muguntar harda dan cikinta takeyiwa" tana kallo ya kafa kai yana kurbar shayin a yunwace Babannan yace
"Umma Burodi da kwai"
"Yanzu zan baka ai uban gajen haquri" ta fada tana tura masa farantin data saka masa Burodinsa da kwan akai sauran ma duk ta miqa musu nasu. Abdullahi yakai kofi bakinsa ya kurbi shayi ba zato Bara'atu taji ya fesoshi da qarfi harya batata, a zafafe ta buga masa tsawa tana cewa
"Wane irin wulaqanci ne haka ai kasan shayin da zafi zaka kurba ya qonaka ji yanda ka batani duk ka tsalla mana yawu acikin abinci"
Abdullahim dake karkada harshe yawu na dilala dakyar yace mata
"Umma ba zafi bane, gishirine a ciki kamar ze tsinke mun harshe"
"Gishiri?" Ta fada cikin mamaki, Babangida daya matse fuska yace
"Nima da akwai a cikin nawa Umma".
Robar da sukari yake ciki ta janyo dan ta tantance ko kuskure tayi gurin daukowa sedau sukari ne a ciki, se kuma ta saka cokali ta dibi shayin gabanta dan kadan ta kai baki ai da sauri itama ta fesoshi jin wani azababben gishiri tamkar an jiqe kwano gida ciki ruwan fulas din to meya kawo gishiri ciki?
Kofunan hannun Babannan da Zakariyya wanda qiris ya rage ya shanye nasa ta kwace da alama shi be gane banbancin dandanon gishirin bama. Ta hade su a Jug kafinta miqe a sanyaye ta shige kitchen dinta na cikin daki. A Butar tafasa ruwa ta saka nan da nan yayi zafi bata ko Jira ya tafasa ba ta juyo ta sake hada musu wani zuciyarta ta aminta da cewar da gangan Binta ta zuba musu gishiri a ruwan shayi wai me wannan matar take nema da ita fisabillahi.
Bayan sun gama ta tattaro kwanuka ta fito dasu danta wanke sedata hado ma cikin kitchen ta zauna ta fara wanke wanke, Shayin dayaqi shayuwa ta tsiyayar a rariya Ta bude Fulas din zata zubar da sauran na ciki kenan ta ji muryar Binta a kanta tana cewa
"Aa, Maman Baba meya faru naga kin sheqar da shayi a rariya?"
"Shayi kuma?" Audu sa suka fito tareya tambaya yana kallon rariyar da shayin be gama wucewa ba,
"Gashi nan kuwa ka gani hadin kauri kuwa wlh, qila sun hada ya musu yawa ne maimakon ki barshi an jima ki dumamawa yara susha kuma se ki zubar ai Almubazzaranci ne wannan" Bintan ta sake fada. Bara'atu bata iya dagowa ba balle tace wani abu dan wannan Bom din kam tilas ya tashi da ita dan tafi kowa sanin Audu baya son wulaqanta abinci tun zamanin tana ita kadai a Bechi kafin su dawo Kano ko abu ya siyo ze gaya mata idanba zata iya amfani dashi duka ba ta fitar ta bayar kar abarshi ya lalace balle yanzu akan Idonsa ta zubar da shayi a rariya tasan ko Binta bata saka baki ba se yayi fada.
"Yanzu saboda wulaqanci abinci zaki wulaqanta haka? Da yayi muku yawa me yasa bazaki bawa Abdullahi ya fita ya bawa Almajiri ba?" Audun ya fada cikin fushi. Murya a sanyaye tace
"Kayi haquri ba yawa ya mana ba, kuskure aka samu gishiri ne a cikin ruwan da aka dafa se bayan dana hada mana sannan muka ankare kaga baze shawu ba shiyasa ma zubar"
"Gishiri a cikin shayin?" Ya tambayeta cikin sigar rainin wayo irin be kama abinda ta fada ba. Fulas din gabanta ta tura masa tana cewa
"Dama ba zaka yarda ba amma ga sauran ruwannan ka dandana kaji"
"Ikon Allah a garin yaya gishiri ya shiga ruwan shayi? bari muji" Binta ta fada tana dauke fulas din cikin mugunta datayi kama da kuskure ta sakeshi daga tsayen da take ji kake tush ya tarwashe a qasa ruwan ya watse duk ya tsallar musu a qafa harda Audun.
"Innalillahi na qone" Bintan daya fi zubar mata ta fada tana daqe qafafu, Audu ya zabga tsaki yana cewa
"Wane irin sakarci ne zaki yada fulas se kace bakya gani? Se ki dakko tsintsiya ki tattare gurin ai kafin yara su fito wani ya taka kwalba" yana fadar haka ya baza Babbar rigar da ta zame masa Kayan sawa yanzu ya fice daga gidan.
"Ke kin dauka zaki kwanta ki miqe qafa in daga miki abinci? To ba Gishiri ba idan bakiyi sannu ba wata ran shinkafar bera zan zuba miki" ta wuce ciki tana tsaki.
Sanadin zaman Bara'atu boyi boyi kenan a gidan, da ranar girkinta da ba nata ba muddin tana so yaranta suci abinci kan lokaci sedai ta tashi tayi, an koma makaranta Abdullahi ya koma makarantar kwana dan haka ita zatayi shara ta hada abin kari ta shirya yan makaranta su tafi sannan tayi wanke wanke ta hado wankin kayan Yaranta dana Bintan da wani sa'ilin harda nata kayan take tulo mata kuma bata isa taqiyi ko tayi magana ba ranar Audu ya ringa surfa mata bala'i akan ta fiya fitina bata qaunar a zauna lafiya.
"Kin ga ya dage dole mubi tsarin da aka kawo da farko amma tunda kin nemi a canza, idan kin yarda ni a bangarena a maimakon sharar dakina zaki ringa yimun Wankin kayan Yara ke ma seki fadi abinda zan ringayi miki a madadin taki sharar" ta qarasa tana doka murmushi kamar wawiya.
Kasa cewa komai tayi, ta kalli Bintan kafin ta kalli Audu tana jiran taji abinda zece se ji tayi yana cewa
"Babu maganan ta zabi abinda zaki mata, sharar dakinta ita tace ta yafe kar kiyi na dakinki kuma wannan da ba zatayi ba kika musanya mata" ya juya kan Bara'atu da tayi fakare tana sauraronsu yace
"Zaki ringayi mata wankin kayan yaran duk ranar da baki da girki, My decision is final" aka jefo turanci daga nan ya shige daki ya barsu zaune.
"Yanzu wasan ya fara yarinya" Binta ta fito mata a sak ta fada kafin ta miqe tana juya Mazaune tabi bayan Audu tana wata shaidaniyar dariya irin ta wanda ya nisa cikin lamarin duniya.
https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*PAGE 28*
Kwana tayi tana juyi duk motsi abinda ya faru daren jiyan seya fadomata zuciyarta tayi mata nauyi, idanunta banda radadi babu abinda sukeyi dalilin kukan data sha, Ta rasa a wanne matsayi zata ajiye Audu dan bata ta Binta kwata kwata ta gama sallama mata amma shi Audu fa?
Son zuciya ko kuwa qin gaskiya ne yake saka shi aikata abubuwan da yakeyi ko yaya? Me yasa duk hukuncinsa yake kasancewa na son zuciya kuma bisa goyon bayan rashin gaskiya?.
Rashin baccin da batayi ba cikin dare yasa ta makara, dakyar ta iya tashi tayi sallah kanta na bala'in sara mata ta koma ta sake kwanciya tana jin yaran na qu qunin Yunwa dan Zakariyya harya fara kuka gashi bata jiyo motsin Bintan ba alamarbata sakko ba balle ta dora abin kari, Audun m yau be leqa su da Asuba yaga ko sun tashi ba kamar yanda ya saba haka daya dawo wucewarsa daki yayi tunda fushi yake da ita kuma yau din Lahadi ce baya fita da wuri daman se qarfe sha biyun rana shiyasa Bintan ta qara samun damar tsula tsiyarta.
Abdullahi ta kira tace ya share tsakar gida ya wanke saboda hadari ya taso daren jiya ruwa be sauka ba se Iska ta taho da qura ita kuma ta daure ta hada ruwan wanka ta yiwa yaran kafin Hajiyar gidan ta gama qailularta ta basu abin kari. Tana cikin shiryasu ta jiyo hayagagar Binta ta san baze wuce da Abdullahi take ba. Cikin kayan Babannan ta samarwa Zakariyya wanda suka masa tace su zauna nan bari ta kawo musu abin karyawa ta zura Hijabinta tana qoqarinfita ta jiyo sallamar Bintan a qofar dakinta, tayi A'uziyya a zuciyarta domin Binta ta zarce shaidan kaidi, sanin Audu na gida kuma zata yuwu wani bala'in ta sake zuwa ta hada mata dan haka tayi saurin fita kafin ita ta shigo mata cikin dakin.
Faran faran tamkar babu wani mugun abu a ranta ta gaida Bara'atun ita dai daga lafiya ta gagara qara ce mata komai saboda zuciyarta gaba daya ma tsinkewa takeyi, ita dai kaf a karkararsu bata taba ji ko ganin Mace irin Binta ba, to ko daman wannan abin shine wayewar da ake fada? Idan kuwa hakane ta godewa Allah da ta kasance bagidajiya akan ta zamo daga cikin munafukai.
"Kuyi haquri na barku da yunwa ko? Bacci ne ya kwace mun yau, Bari in maza ko ruwan shayi ne a tafasa se a soya wainar qwai tunda muna da burodi" Binta ta fada tana murmushi. Cikin sanyi Bara'atu tace
"Babu komai ai" ta bata amsa a sanyaye daga nan Bintan ta juya tana murmushin da Allah kadai yasan ma'anarsa.
Kusan Minti goma tsakani Binta ta sake dawowa da qaton Fulas din ruwan zafi tun wanda Dada ta bata ne lokacin Amarcin da ake zuba musu ruwan zafi a ciki. Yana da girma ga riqe zafi shiyasa take jin dadinsa sosai.
"Sannu da aiki" ta fada sanda ta kabi Fulas din, Binta tayi murmushi ta koma kitchen ta sake kawo mata Farantin data Zubo faya fayen wainar qwai.
A babban Jug din da take hada musu shayi gaba daya ta zuba Madara da Milo da Sukari kadan kafinta tsiyaya Ruwan zafinta motsa, ta zubanata a kofi ta zubawa Abdullahi se ta qara ruwan sanyi akan sauran ta dan qara musu Madara da Milo sannan ta zubawa sauran Yaran.
Yanda suka rarumi Kofunan duk sunbata tausayi musamman Zakariyya da yake qaraminsu a ranta tace
"Wato muguntar harda dan cikinta takeyiwa" tana kallo ya kafa kai yana kurbar shayin a yunwace Babannan yace
"Umma Burodi da kwai"
"Yanzu zan baka ai uban gajen haquri" ta fada tana tura masa farantin data saka masa Burodinsa da kwan akai sauran ma duk ta miqa musu nasu. Abdullahi yakai kofi bakinsa ya kurbi shayi ba zato Bara'atu taji ya fesoshi da qarfi harya batata, a zafafe ta buga masa tsawa tana cewa
"Wane irin wulaqanci ne haka ai kasan shayin da zafi zaka kurba ya qonaka ji yanda ka batani duk ka tsalla mana yawu acikin abinci"
Abdullahim dake karkada harshe yawu na dilala dakyar yace mata
"Umma ba zafi bane, gishirine a ciki kamar ze tsinke mun harshe"
"Gishiri?" Ta fada cikin mamaki, Babangida daya matse fuska yace
"Nima da akwai a cikin nawa Umma".
Robar da sukari yake ciki ta janyo dan ta tantance ko kuskure tayi gurin daukowa sedau sukari ne a ciki, se kuma ta saka cokali ta dibi shayin gabanta dan kadan ta kai baki ai da sauri itama ta fesoshi jin wani azababben gishiri tamkar an jiqe kwano gida ciki ruwan fulas din to meya kawo gishiri ciki?
Kofunan hannun Babannan da Zakariyya wanda qiris ya rage ya shanye nasa ta kwace da alama shi be gane banbancin dandanon gishirin bama. Ta hade su a Jug kafinta miqe a sanyaye ta shige kitchen dinta na cikin daki. A Butar tafasa ruwa ta saka nan da nan yayi zafi bata ko Jira ya tafasa ba ta juyo ta sake hada musu wani zuciyarta ta aminta da cewar da gangan Binta ta zuba musu gishiri a ruwan shayi wai me wannan matar take nema da ita fisabillahi.
Bayan sun gama ta tattaro kwanuka ta fito dasu danta wanke sedata hado ma cikin kitchen ta zauna ta fara wanke wanke, Shayin dayaqi shayuwa ta tsiyayar a rariya Ta bude Fulas din zata zubar da sauran na ciki kenan ta ji muryar Binta a kanta tana cewa
"Aa, Maman Baba meya faru naga kin sheqar da shayi a rariya?"
"Shayi kuma?" Audu sa suka fito tareya tambaya yana kallon rariyar da shayin be gama wucewa ba,
"Gashi nan kuwa ka gani hadin kauri kuwa wlh, qila sun hada ya musu yawa ne maimakon ki barshi an jima ki dumamawa yara susha kuma se ki zubar ai Almubazzaranci ne wannan" Bintan ta sake fada. Bara'atu bata iya dagowa ba balle tace wani abu dan wannan Bom din kam tilas ya tashi da ita dan tafi kowa sanin Audu baya son wulaqanta abinci tun zamanin tana ita kadai a Bechi kafin su dawo Kano ko abu ya siyo ze gaya mata idanba zata iya amfani dashi duka ba ta fitar ta bayar kar abarshi ya lalace balle yanzu akan Idonsa ta zubar da shayi a rariya tasan ko Binta bata saka baki ba se yayi fada.
"Yanzu saboda wulaqanci abinci zaki wulaqanta haka? Da yayi muku yawa me yasa bazaki bawa Abdullahi ya fita ya bawa Almajiri ba?" Audun ya fada cikin fushi. Murya a sanyaye tace
"Kayi haquri ba yawa ya mana ba, kuskure aka samu gishiri ne a cikin ruwan da aka dafa se bayan dana hada mana sannan muka ankare kaga baze shawu ba shiyasa ma zubar"
"Gishiri a cikin shayin?" Ya tambayeta cikin sigar rainin wayo irin be kama abinda ta fada ba. Fulas din gabanta ta tura masa tana cewa
"Dama ba zaka yarda ba amma ga sauran ruwannan ka dandana kaji"
"Ikon Allah a garin yaya gishiri ya shiga ruwan shayi? bari muji" Binta ta fada tana dauke fulas din cikin mugunta datayi kama da kuskure ta sakeshi daga tsayen da take ji kake tush ya tarwashe a qasa ruwan ya watse duk ya tsallar musu a qafa harda Audun.
"Innalillahi na qone" Bintan daya fi zubar mata ta fada tana daqe qafafu, Audu ya zabga tsaki yana cewa
"Wane irin sakarci ne zaki yada fulas se kace bakya gani? Se ki dakko tsintsiya ki tattare gurin ai kafin yara su fito wani ya taka kwalba" yana fadar haka ya baza Babbar rigar da ta zame masa Kayan sawa yanzu ya fice daga gidan.
"Ke kin dauka zaki kwanta ki miqe qafa in daga miki abinci? To ba Gishiri ba idan bakiyi sannu ba wata ran shinkafar bera zan zuba miki" ta wuce ciki tana tsaki.
Sanadin zaman Bara'atu boyi boyi kenan a gidan, da ranar girkinta da ba nata ba muddin tana so yaranta suci abinci kan lokaci sedai ta tashi tayi, an koma makaranta Abdullahi ya koma makarantar kwana dan haka ita zatayi shara ta hada abin kari ta shirya yan makaranta su tafi sannan tayi wanke wanke ta hado wankin kayan Yaranta dana Bintan da wani sa'ilin harda nata kayan take tulo mata kuma bata isa taqiyi ko tayi magana ba ranar Audu ya ringa surfa mata bala'i akan ta fiya fitina bata qaunar a zauna lafiya.