← Book details Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 48 OF 137

Sashe 48

Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Wai se ga Binta na bi gida gida daki daki na yan uwan Audu da sunan taje su gaisa abin dariya ita ce har gidansu Bara'atu. Duk gidan data shiga bata fitowa seta kwance Amaryar Audu ta fada musu tsohuwar kilaki ya auro, Bilki da tun sakin Bara'atu ta fita a sabgar Audu da gidansa farko cin mutunchin Binta taso tayi da ta je mata gida amma zancen data kai mata ya tayar mata da hankali. Me yake damun Audu? Wace hau ce ta haushi da ze auri Karuwa? Hankali tashe ta tafi gida ta samu su Yaya Babba duk sun tattaru dan kowanne na komawa gidansa da yamma ya samu saqon da Binta ta bari shiyasa suna idar da sallar Isha suka tattaro suka taho gidan gaba daya ita ko Binta tana masaukin su da aka qara gyareshi, rabon su duka ya siye banda na Yakubu dan nan yake sauka idan yaje se ya qara fadada nasan yayi dakuna manya da bandaki a ciki.

"Nifa tun ranar da mukaje neman auran kun tuna sanda na fita zagayawa a lokacin naji wasu suna qus qus din wai anya wadannan sun san labarin Yarinyar suka zo nema dansu aure? Basu dai fadi komai ba amma wannan magana tasu ta jefani a wasi wasi sedai tunda shi ma'auri wakilci kawai ya nadamu shi yasa nayi shiru bance komai ba" Yaya Baba ya fada, Aminu yace

"Haba Yaya, menene amfanin girman idan ba zaka ga abin da ba daidai ba ka gyara mana? Yanzi da kaji wannan magana ai ko a tsakanin mu seka gaya mana idan yaso mu basu kudin Aure mu tafi ba zamu yarda a daura ba har se an bincika munji dar din maganar halin nata, na tabbatar shima be sani ba yanzu ya za'ayi?"

"Amma ku kuna ganin gaskiya wannan yarinyar ta fada, kun manta sharrin ta kenan?" Hashimu da be manta kitimurmurar Binta ba ya fada. Bilki tace
"Bana jin qarya ne, tunda ga Yaya Baba ma yace yaji wata magana, yanzun dai mu jirayi Yaya Yakubu ya iso gobe idan Allah ya kaimu in yaso se mu san abinyi kafin Audun ya qaraso shima" inji Bilki, haka taron ya tashi, washe gari ko da Rana Yakubu da Iyalansa suka sauka Bechi. Binta batayi qasa a guiwa ba ta shige ko gajiya bata barshi ya ware ba yana aje haqarqarinsa a kujera ta zube a gabansa ko kallon inda take Bakaraba batayi ba taja yaranta suka shige daki.

Bilki tayi turus da kayan abinci a hannunta tana kallon Binta dake rusa kuka a gaban Yakubu tana masa bayani se ta fara jin anya maganar nan da gaske ce kuwa kodai wasan kwaikwayonta data saba ne ta hadashi?

"Yanzu saboda Allah ba zaki barshi ya ko huta ba zaki tasashi a gaba da wannan maganar?" Bilki ta fada taba harararta.
"Zauna Bilki" ya bata umarni kafin yaci gaba da cewa
"Menene gaskiyar abinda ta fada?"

"Yaya muma ita tazo mana da maganar, amma Yaya Baba yace..." Ta fada masa abinda Yaya Baba yaji sanda sukaje neman aure.

"Shikenan tashi kije, zamuji ta bakinsa idan ya qaraso"
"Dan girman Allah kar kuce masa ni na gaya muku"
"Dama ba zamu fada ba tashi kije abinki" da haka ta fita rai fes dan koda Yakubu beyi wata magana ba daga fuskarsa ta fahimci ya kadu da maganar.

Tana fita Balaraba ta fito daga daki tace
"Yanzu kun yarda da maganar wannan annamimiyar matar? Matar data laqawa wata sharrin kisan kai sena Bariki ne ba zata dorawa wata ba? Koda yake Allah ya kawoshi gara yaji abinda ta hada ko idonsa ze washe ya gane da wadda yake zaune ai".

Yamma Lis Audu ya isa Bechi, seda sukayi sallar Isha kafin Yakubu ya tareshi a wajen dan baya so sauran yan uwan su fara masa magana ta yanda laifin Binta ze fito. Cikin siyasa da kwarewar aikinsa ya saka masa maganar a baki, yana da labarin yawace yawacen da yakeyi da wannan yayi amfani yace an gaya masa acan ya hadu da Amaryar tasa.

"Haka ne, amma ban aureta ba seda na maida ita gidansu tayi Istibra'i tukunna" ya bashi amsa kai tsaye. Yakubu ya ringa kallonsa ya gaza cewa komai, dakyar ya iya bude baki yace
"Amma yanzu na tabbatar da Audu baka da tunani sam, duk matan duniya ka rasa macen Aure se karuwa ko kuma asiri tayi maka?"

"Ni babu Asirin da tayi mun kuma ka dena cewa Karuwa tunda ta tuba ta bari sannan babu inda Shari'a ta haramta Aurena da ita tunda dai tayi tsarki sannan ni ina sonta a haka kuma nasan har a gurin Allah nayi aikin alkhairi jihadi babba nayi" Audun ya fada cikin yanayin ko in kula,

"Haka ne" Yakubu ya bashi amsa daga nan yasa kai ya shige gida ya bar Audun a tsaye.

*MAMAN MARYAM ONLINE BUSSINESS*

*Ina kuke Mata Yan kwalisa , Ina nufin isassun Mata ,Wai shin Kuna da labarin shahararren company nan namu na GHT wato good healthtreatments*
*Wanda yazo muku da fitattu Kuma* *ingantatattun suppliment ,na dukkan matsalolin ku*❓

*Ina maisan tayi kyau,irin na isassun Mata ya fitar Miki da shef dinki tayi Miki gyara in and out ,nemi royal jelly dinmu na company GHT*
*Wanda aka yishi da xuma ,kundai San amfanin Zuma basai na fada miku ba , hajiya ta kixo ki Yi gyara domin ki kerewa sa,a kije taro ko baki da ko sisi kiji Ana rangada Miki hajiya , saboda yanda Zaki Kara kwarjini ,kina walwali acikin mutane , magungunan ght anti agen ne suna maida tsohuwa* *yarinya ,yarinya Kuma ta koma jaririya*

*Muna da magunguna iri iri*

*NA GYARAN JIKI*
*NA GOGE NANKARWA*
*NA RAGE QIBA*
*NA CIRE TUMBI*
*NA QARIN HIPS*
*NA GIRMAN BREAST*
*NA QARA TSAHON GASHI*

*NA QARIN NI'IMA WANDA ZAI SAUKAR MIKI DA NI'IMA YA QARA MIKI DADI DA ZAQI A GURIN OGA*

*Muna da hadin bita zai zai ,indai kishiyar ki tana Shan magungunan GHT, tohh lallai sunan ki sorry domin kuwa tazarar dake tsakanin ku kamar tazarar sama ne da kasa*

*Muna da Wanda zai matseki ciki da waje Andai na yayin dinki uwargida*,

*Sannan company mu na GHTBai tsaya anan ba*
*Ya kawo muku maganin dukkan matsalolin ku*

*INA MASU HAWAN JINI?*
*INA MASU CIWON ZUCIYA?*
*INA MASU CIWON QODA?*
*INA MASU CIWON HANTA?*
*INA MASU SICKLER?*
*INA MASU HIV?*
*INA MASU CANCER?*
*INA MASU NEMAN HAIHUWA?*

*Tohh Ku matso GHT taxo muku da magungunan matsalolin ku*
*Kuma muna da testimonys da yawa ,na wadanda suka gwada suka da ce*

*Munanan a KANO KUNTAU*
*Kuma muna tura Kaya ko wanne gari cikin aminci da gaskiya , kuma kayan mu muna badashi ne cikin price Mai rahusa ga kyau ga inganci sannan ga Rahusa*

*Kutuntube mu ta wannan number 📞08129249549*
*📲07011401314*

Tabbas yasan wannan lokacin zezo shiyasa yake yawan nunawa Dada rashin amfanin baiwa Audu damar yanke duk hukuncin da yayi masa ba tareda ya shawarci kuwa ba. Ita ta bashi wannan damar, shi a matsayinsa na babba bata taba daukar Maganarsa da muhimmanci ba domin a sannan tana ganin Audu ya fishi wayewa da sanin rayuwa, yasha gaya mata hakan bashida kyau domin idan ya yanke hukuncin daidai qata rana ze yanke akasin haka kuma baze taba ganin cewar yanayin abinda ba daidai din ba tunda ya saba cewar akoda yaushe shi yake bada shawara ba dai a bashi ba, yau da ace ta gina su akan turbar su shawarci junansu sannan su yanke hukunci akan duk wani al'amari na rayuwarsu ya tabbatar koda Audu na da taurin kai da kafiya tilas a wani bangaren yayi yanda ake so, gashi yanzu yana yankewa kansa danyan hukuncin da idan ba'ayi wasa ba se yayi nadamar su a gaba.

Tamkar dai Yakubun dmsanda su Yaya Baba suka tareshi suma tabbacin gaskiyar maganar ya basu be kuma saurari komai daga bakinsu ba ya shige daki inda Binta ta kasa kunne tana jira ta jiyo magana ta tashi amma shiru, washe gari Juma'a yan uwan Amarya Zubaida suka yiwa Bechi tsinke, su biyar se ita ta shida, dayan dakin dake kusada na Binta aka shigar da ita Mata nata turuwar zuwa ganin fuskar Amarya amma babu dama dan a rufe take daman gulma da munafunci ne kawai ya kaisu suga fuskar tsohuwar Karuwa. Binta na cikin Dakinta a kwance abin duniya ya isheta ta kasa fita har sanda aka fito da Amarya tsakar gida inda akayi shimfidu aka zaunar da ita Bilki ta shiga ta kira Bintan saboda Al'adace za'a danqa amanar Amarya a hannun uwargida.

Daurewa tayi ta qara barbada hoda, daman Leshi tasa me kyau daya qara fitar mata da suffar ta gaba gaba ta tura dauri gaba ta fita tana qoqarin danne shadan dake raya mata data fita ta cakumi Amaryar ta mata dukan mutuwa. Haka ta ringa yaqe har aka gama komai aka bude fuskar Amarya, ganinta tayi yar yarinya da kadan ta fi Bara'atu cika amma kyakykyawace kwarai duk da baqace, kaso ashirin na fargabarta taji ya ragu dan ta saka ran ganin matar da idanunta kadai zasu firgitata amma se ta raina zubinta.
Chapter 48 · 0% Book details