Sashe 4
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Haka suka ci gaba, Yakubu na matuqar maida hankali ga Karatu yayinda Audu turanci kawai ya saka zuciyarsa ze koya saboda idan ta tabbata sun gama makaranta za'a kaisu turai kar yaje ya rasa bakin magana. A hankali ya faratiwa Makarar asha ruwan tsuntsaye, Sadi, da aka kawosu Almajiranta tare amma shi dan Bagwai ne shiya fara nuna masa hanyar Kasuwa. Da safe idan sun tafi Boko shida Yakubu ze zame ya tafi bakin Asibiti anan zeyi duk wani aiki daya samu, dako ne, aike, duk wani abu da zeyi a biyashi haka ya ringayi kan jiki kan qarfi dake ya saka abin a ransa kuma yana da zuciyar yi se gashi baya jin wahalar kowanne irin aiki indai ze kawo masa kudi.
Da Yakubu ya gane baya zama a makaranta yace ze gayawa Malam seya dakata da zuwa Kasuwa, cikin yan kudaden daya samu ya auno Aya da gyada ya kaiwa Matar Malam da suke kira Nene dayake suna shiri yace tayi masa gyada me gishiri da Aya me siga ya daura abarsa a Boko ya siyar a Allo ya siyar se gashi an gane shi a unguwa Audu me gyada da Aya kuma sosai yake ciniki abinsa. Seda suka shekara biyu kafin sukaje gida, a lokacin sun fara zama samari dan Yakubu nada shekaru sha biyar Audu nada Sha uku. Cikin yan kudaden jarinsa yayiwa Dada da qannensa harda Baffansu tsaraba.
Kowa yaji dadin yanda ya gansu, Dada ce ta ringa masa fada akan ina ya samu kudi yayi wannan siyayya be boye mata ya sanar mata da duk abubuwan da yakeyi harda zancen Boko da sukeyi shida Yakubu ya kuma qara da fada mata gaskiyar dama saboda ya samu damar neman kudi Yakubu kuma yayi karatu yasa sukace zasu Makarantar Allon. A wannan karon kafin su koma seda ta sanar da mahaifinsu gaskiyar komai gudun kar wata rana ya gane yace sun hada baki sun munafurceta, da fari ya ringa fada dan sosai yake Adawa da karatun Boko har yana cewa ba zasu koma Birnin ba se kuma daga baya basu san yanda akayi ya canza ra'ayi ba da kansa yayi musu shirin komawa ya kuma yi musu nasiha tareda gargadin su tsaya a turbar Allah karsu yarda masu jajayen kunnuwa su dorasu akan wata hanya sabanin wadda Addinin Islama ya dora mu akai. Ya sake jawa Audu kunne sosai akan banbance tsakanin Halal da Haram tunda yana zuciyar nema baze daku she shi ba, abinda ya janyo masa sakkowa harya haqura zasu koma dinma bayan sunyi magana da Hashimu dansa na biyu shiya nuna masa Alfanun abinda su Audun sukeyi tunda baya kaucewa shari'a bane.
Yace masa "Baba idan ka dubi yanda rayuwa take tafiya a kullum abubuwa qara yi mana wahala sukeyi dan abinda muke nomawa ba wadatar mu yake yi ba balle har mu samu na siyarwa muyi sauran buqatu kuma ko a cikin karkarar nan idan ka duba masu fita fatauci Abokanan mu zakaga suna samun Abun rufin asiri har su taimaka mana muma, da ace tun muna qanana kamar su muma mun tashi da wannan tunanin qila da rayuwar ta mana sauqi amma yanzu tunda Allah yasa su sun himmatu zasuyi a barsu muyita rakasu da Addu'a Aminu ma da ze bisu suje can birnin yayi Bokon koya kama sana'a kamar Audu duk da hakan yayi".
To haka su Audu suka koma ba tareda Aminu ba dan yace ba zashi ba da yake Auta ne Goggo Fadi bata takura masa ba kuma shi kadai ya rage gabanta tunda duk an aurar da Maryo da Amina Mazan ma Hashimu da Lawan sunyi Aure. Rayuwa taci gaba da garawa Audu da Yakubu a birni, iya wuya Audu neman kudi yakeyi yana kuma riqe da hudubar Mahaifansa akan ya tsaya ga halal karya kuskura yaci abinda Allah be halasta masa ba kuma da yake a lokacin duniya na zaune lafiya cuta da bata gari basuyi yawa ba shiyasa abun yazo masa a sauqaqe. Tun yana Dako a kasuwa ko aikace aikace har ya fara kayi nayi, ze karbi kaya ya fita dasu ya siyar ya cire ribarsa har ta kai ya hada yar tireda yana kasa kayan koi gefe gida kuma ya ajiye Baro duk wani dan itace na marmari da ake yayi a lokaci ze saro ya ringa siyarwa yan kasuwar har mamakinsa suke ganinsa yaro qarami dukda yana da baragen girma amma zafin neman sa ba duk babbaba shiyasa yayi shura a bakin Asibiti babu wanda besan AUDU BECHI ba haka suke masa inkiya da garinsu.
Duk qarshen shekara suke zuwa gida kuma duk sanda zasu tafi haka ze hada tsaraba himili duk wanda ya shafe shi seya riqe masa wani abu ya kai masa dan badaga nan ba Audu akwai kyauta kuma a wannan yanayi Girma da Wahala suka fara kwantar da mahaifinsu dukda shekarunsa basu kai ace ya kwanta tun yanzu ba amma yanda rayuwar ta faro tun quruciya jiki yana wahalar data zarce abinda ze dauka shiya janyo masa ciwo yayi masa kwaf yau lafiya gobe babu haka yasa idan zasu je gida Audu ze siyi magungunan ya tafi masa dasu da irin mayukan zafi saboda qorafin ciwon jiki da yake yawanyi.
A wannan gantafalfala suka kammala Primary tareda Saukar alqur'ani ta biye wadda Audu dai ba zuwanta yake ba a sati befi ya leqa sau daya ba ita kanta Allon Karatun dare kadai yake zama Gwani yayi fadan yayi nasihar amma Audu ya toshe kunne, dadinta daya yana biya karatu daidai ya wanke Allonsa akan lokaci wannan yasa Gwani yake daga masa qafa Bokon ma idan ana jaraba zeje yayi kuma zeci ga turancin daya saka kansa ya iya radau dan ko Yakubu me qulafucin Bokon Albarka shiyasa Malaman suke ji dashi, Audu akwai rashin ji amma akwai kwakwalawar daukar Karatu.
Yakubu ya tafi makarantar kwana dan cigaba da karatun sa, burinsa ne ya zama Alqali Audu kuwa yace yayi sallama da Boko ya kama neman kudi kuma. Shi yayiwa Yakubu duk wani shiri na tafiya makarantar, haka kuma yana kai masa ziyara idan anyi hutu Yakubun Bechi yake tafiya yayi hutunsa acan Audu kuma ana Kano ana ta fafutukar rayuwa. Inda ya kafa yar tiredar tasa aikin fadada titi yabi ta gun dole ya tashi daga qarshe ya koma zuba kayan kolin nasa a Baro yayi ta zaga kasuwa yana waqa ta kiran customers yanda yake waqar abin dariya yake saka wasu siya badan ma sunyi niyya ba. Yakubu yana shekara ta uku a makaranta lokacin kuma aka aurar da Bilki wadda take bin Audu, ba qaramar Bajinta Audu yayi a auran nan ba dan dama ya dade yana tanadi saboda mutuniyarsa ce ko irin fadan sako da sakon nan basa yi da akwai fahinta sosai a tsakaninsu a kuma Bikin Bilkin ya dabbaqa soyayyarsa ga Bara'atu wadda tayiwa Bilki babbar qawa. Tun suna yan yara Audu yake sonta an dauka yarinta ce ashe shi har ransa ya riqe abun yanzun daya furta yana son ta da yawa wasa suka dauki abun saboda idan ka dubi a yanda akewa yara aure Bara'atu ta isa kaiwa daki dukda shekarunta sha biyu ne a sannan amma ga Bilki da take sa'arta an mata aure itama Audu kuwa yana shekara sha bakwai koda Maza suna saurin Aure a qauyen amma be isa ba tukunna, ga Yakubu me sha tara da Aminu me Ashirin da biyu nan basuyi aure ba bare Azo kansa haka dai ya ringa hurewa Bara'atu kunne da soyayyarsa seda ya tabbata ta mato ta yanda ko ya koma birni ba zata saurari wani ba zata jira shi kafin ya koma Birni ya bar Audu da suke hutun makaranta zasu shiga Aji hudu a sannan.
Satin Audu daya da tafiya jikin Malam Tijjani ya motsa kuma ciwon yafi na ko yaushe zafi dole Yakubu ya bazamo Kano neman Audu saboda Malam din da yake ta nanata a kira masa Audu gashi babu waya a sannan, kwanansa daya suka juya hankali tashe yanda ya tarar da jikin Mahaifin nasa ya tayar masa da hankali ya shawarci manyan yayyensu akan su tafi da Malam Kano a akaishi Asibiti amma suka qi a cewarsu anayin na gargajiya wai a yanda ya ganshi ma jikin da sauqi, cikin daren Ranar Malam Tijjani ya amsa kiran Ubangiji har yaja numfashinsa na qarshe kuwa be dena maimaita musu su tsaya akan gaskiya ba kuma duk rintai duk wahala karsu yada zumunchi suci gaba da hada kansu kamar yanda suka tashi.
Sunyi kuka sosai da jimamin rasuwar mahaifin nasu, daga Audu har Yakubu suka kasa komawa inda suka fito saboda mahaifiyarsu da mutuwar Malam din ta tabata sosai har itama ta kwanta jinya, ita din bata da kowa a yanzu se Malam dasu yayanta dan Iyayenta duk sun rasu Yayyenta biyu suma shekara uku kenan Babban Ya rasu me bi masa kuma be cika shekara da rasuwa ba shima yanzu ga Malam shima ya tafi. Seda sukayi dagaske suka qarfafa mata guiwa kafin ta dangana taci gaba da zaman takaba. Audu ya damu Yakubu akan batun komawa makaranta dan tuni hutu ya qare an Koma amma duk sanda yayi masa maganar se yayi shiru yaqi ce masa komai. Audu be fahimci dalilin Yakubu naqin komawa makaranta ba seda akayi sadakar Arba'in din Mahaifinsu, a ranar kuma dattawan qauyen suka zaunar dasu akan maganar rabon gado.
*Batoul Fashion and Boutique* online store ne na sai da kayan 'yan gayu dandasa-dandasa na gani na fada, na kece raini a taro, masu tashin kan Habeeby ❤️ Kuma masu sa kishiya kwalla😂🏃🏻♀
Muna da Laces, Atampa, Voiles, Shoes, Bags, Gowns, Veils and Jewelry masu kyau a farashi me sauqi, Muna Bada sari Kuma Muna siyar da daidai, Muna hada lefe masu Aji🔥🍻kada na cika ku da surutu😌ku garzaya IG page dn www.instagram.com/batoul_fashion_and_boutique don shaida bayanan da na muku da Kuma tabbatarwa ko ku shiga WhatsApp group dn ta https://chat.whatsapp.com/Fi0iCJcvtGKEYcVrbZwxfw za ku iya tuntubarmu a 07025420431
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*MARUBUCOYAR*
*WATA KISHIYAR*
RUBUTACCIYAR QADDARAH*
*HALIN KISHI*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
Da Yakubu ya gane baya zama a makaranta yace ze gayawa Malam seya dakata da zuwa Kasuwa, cikin yan kudaden daya samu ya auno Aya da gyada ya kaiwa Matar Malam da suke kira Nene dayake suna shiri yace tayi masa gyada me gishiri da Aya me siga ya daura abarsa a Boko ya siyar a Allo ya siyar se gashi an gane shi a unguwa Audu me gyada da Aya kuma sosai yake ciniki abinsa. Seda suka shekara biyu kafin sukaje gida, a lokacin sun fara zama samari dan Yakubu nada shekaru sha biyar Audu nada Sha uku. Cikin yan kudaden jarinsa yayiwa Dada da qannensa harda Baffansu tsaraba.
Kowa yaji dadin yanda ya gansu, Dada ce ta ringa masa fada akan ina ya samu kudi yayi wannan siyayya be boye mata ya sanar mata da duk abubuwan da yakeyi harda zancen Boko da sukeyi shida Yakubu ya kuma qara da fada mata gaskiyar dama saboda ya samu damar neman kudi Yakubu kuma yayi karatu yasa sukace zasu Makarantar Allon. A wannan karon kafin su koma seda ta sanar da mahaifinsu gaskiyar komai gudun kar wata rana ya gane yace sun hada baki sun munafurceta, da fari ya ringa fada dan sosai yake Adawa da karatun Boko har yana cewa ba zasu koma Birnin ba se kuma daga baya basu san yanda akayi ya canza ra'ayi ba da kansa yayi musu shirin komawa ya kuma yi musu nasiha tareda gargadin su tsaya a turbar Allah karsu yarda masu jajayen kunnuwa su dorasu akan wata hanya sabanin wadda Addinin Islama ya dora mu akai. Ya sake jawa Audu kunne sosai akan banbance tsakanin Halal da Haram tunda yana zuciyar nema baze daku she shi ba, abinda ya janyo masa sakkowa harya haqura zasu koma dinma bayan sunyi magana da Hashimu dansa na biyu shiya nuna masa Alfanun abinda su Audun sukeyi tunda baya kaucewa shari'a bane.
Yace masa "Baba idan ka dubi yanda rayuwa take tafiya a kullum abubuwa qara yi mana wahala sukeyi dan abinda muke nomawa ba wadatar mu yake yi ba balle har mu samu na siyarwa muyi sauran buqatu kuma ko a cikin karkarar nan idan ka duba masu fita fatauci Abokanan mu zakaga suna samun Abun rufin asiri har su taimaka mana muma, da ace tun muna qanana kamar su muma mun tashi da wannan tunanin qila da rayuwar ta mana sauqi amma yanzu tunda Allah yasa su sun himmatu zasuyi a barsu muyita rakasu da Addu'a Aminu ma da ze bisu suje can birnin yayi Bokon koya kama sana'a kamar Audu duk da hakan yayi".
To haka su Audu suka koma ba tareda Aminu ba dan yace ba zashi ba da yake Auta ne Goggo Fadi bata takura masa ba kuma shi kadai ya rage gabanta tunda duk an aurar da Maryo da Amina Mazan ma Hashimu da Lawan sunyi Aure. Rayuwa taci gaba da garawa Audu da Yakubu a birni, iya wuya Audu neman kudi yakeyi yana kuma riqe da hudubar Mahaifansa akan ya tsaya ga halal karya kuskura yaci abinda Allah be halasta masa ba kuma da yake a lokacin duniya na zaune lafiya cuta da bata gari basuyi yawa ba shiyasa abun yazo masa a sauqaqe. Tun yana Dako a kasuwa ko aikace aikace har ya fara kayi nayi, ze karbi kaya ya fita dasu ya siyar ya cire ribarsa har ta kai ya hada yar tireda yana kasa kayan koi gefe gida kuma ya ajiye Baro duk wani dan itace na marmari da ake yayi a lokaci ze saro ya ringa siyarwa yan kasuwar har mamakinsa suke ganinsa yaro qarami dukda yana da baragen girma amma zafin neman sa ba duk babbaba shiyasa yayi shura a bakin Asibiti babu wanda besan AUDU BECHI ba haka suke masa inkiya da garinsu.
Duk qarshen shekara suke zuwa gida kuma duk sanda zasu tafi haka ze hada tsaraba himili duk wanda ya shafe shi seya riqe masa wani abu ya kai masa dan badaga nan ba Audu akwai kyauta kuma a wannan yanayi Girma da Wahala suka fara kwantar da mahaifinsu dukda shekarunsa basu kai ace ya kwanta tun yanzu ba amma yanda rayuwar ta faro tun quruciya jiki yana wahalar data zarce abinda ze dauka shiya janyo masa ciwo yayi masa kwaf yau lafiya gobe babu haka yasa idan zasu je gida Audu ze siyi magungunan ya tafi masa dasu da irin mayukan zafi saboda qorafin ciwon jiki da yake yawanyi.
A wannan gantafalfala suka kammala Primary tareda Saukar alqur'ani ta biye wadda Audu dai ba zuwanta yake ba a sati befi ya leqa sau daya ba ita kanta Allon Karatun dare kadai yake zama Gwani yayi fadan yayi nasihar amma Audu ya toshe kunne, dadinta daya yana biya karatu daidai ya wanke Allonsa akan lokaci wannan yasa Gwani yake daga masa qafa Bokon ma idan ana jaraba zeje yayi kuma zeci ga turancin daya saka kansa ya iya radau dan ko Yakubu me qulafucin Bokon Albarka shiyasa Malaman suke ji dashi, Audu akwai rashin ji amma akwai kwakwalawar daukar Karatu.
Yakubu ya tafi makarantar kwana dan cigaba da karatun sa, burinsa ne ya zama Alqali Audu kuwa yace yayi sallama da Boko ya kama neman kudi kuma. Shi yayiwa Yakubu duk wani shiri na tafiya makarantar, haka kuma yana kai masa ziyara idan anyi hutu Yakubun Bechi yake tafiya yayi hutunsa acan Audu kuma ana Kano ana ta fafutukar rayuwa. Inda ya kafa yar tiredar tasa aikin fadada titi yabi ta gun dole ya tashi daga qarshe ya koma zuba kayan kolin nasa a Baro yayi ta zaga kasuwa yana waqa ta kiran customers yanda yake waqar abin dariya yake saka wasu siya badan ma sunyi niyya ba. Yakubu yana shekara ta uku a makaranta lokacin kuma aka aurar da Bilki wadda take bin Audu, ba qaramar Bajinta Audu yayi a auran nan ba dan dama ya dade yana tanadi saboda mutuniyarsa ce ko irin fadan sako da sakon nan basa yi da akwai fahinta sosai a tsakaninsu a kuma Bikin Bilkin ya dabbaqa soyayyarsa ga Bara'atu wadda tayiwa Bilki babbar qawa. Tun suna yan yara Audu yake sonta an dauka yarinta ce ashe shi har ransa ya riqe abun yanzun daya furta yana son ta da yawa wasa suka dauki abun saboda idan ka dubi a yanda akewa yara aure Bara'atu ta isa kaiwa daki dukda shekarunta sha biyu ne a sannan amma ga Bilki da take sa'arta an mata aure itama Audu kuwa yana shekara sha bakwai koda Maza suna saurin Aure a qauyen amma be isa ba tukunna, ga Yakubu me sha tara da Aminu me Ashirin da biyu nan basuyi aure ba bare Azo kansa haka dai ya ringa hurewa Bara'atu kunne da soyayyarsa seda ya tabbata ta mato ta yanda ko ya koma birni ba zata saurari wani ba zata jira shi kafin ya koma Birni ya bar Audu da suke hutun makaranta zasu shiga Aji hudu a sannan.
Satin Audu daya da tafiya jikin Malam Tijjani ya motsa kuma ciwon yafi na ko yaushe zafi dole Yakubu ya bazamo Kano neman Audu saboda Malam din da yake ta nanata a kira masa Audu gashi babu waya a sannan, kwanansa daya suka juya hankali tashe yanda ya tarar da jikin Mahaifin nasa ya tayar masa da hankali ya shawarci manyan yayyensu akan su tafi da Malam Kano a akaishi Asibiti amma suka qi a cewarsu anayin na gargajiya wai a yanda ya ganshi ma jikin da sauqi, cikin daren Ranar Malam Tijjani ya amsa kiran Ubangiji har yaja numfashinsa na qarshe kuwa be dena maimaita musu su tsaya akan gaskiya ba kuma duk rintai duk wahala karsu yada zumunchi suci gaba da hada kansu kamar yanda suka tashi.
Sunyi kuka sosai da jimamin rasuwar mahaifin nasu, daga Audu har Yakubu suka kasa komawa inda suka fito saboda mahaifiyarsu da mutuwar Malam din ta tabata sosai har itama ta kwanta jinya, ita din bata da kowa a yanzu se Malam dasu yayanta dan Iyayenta duk sun rasu Yayyenta biyu suma shekara uku kenan Babban Ya rasu me bi masa kuma be cika shekara da rasuwa ba shima yanzu ga Malam shima ya tafi. Seda sukayi dagaske suka qarfafa mata guiwa kafin ta dangana taci gaba da zaman takaba. Audu ya damu Yakubu akan batun komawa makaranta dan tuni hutu ya qare an Koma amma duk sanda yayi masa maganar se yayi shiru yaqi ce masa komai. Audu be fahimci dalilin Yakubu naqin komawa makaranta ba seda akayi sadakar Arba'in din Mahaifinsu, a ranar kuma dattawan qauyen suka zaunar dasu akan maganar rabon gado.
*Batoul Fashion and Boutique* online store ne na sai da kayan 'yan gayu dandasa-dandasa na gani na fada, na kece raini a taro, masu tashin kan Habeeby ❤️ Kuma masu sa kishiya kwalla😂🏃🏻♀
Muna da Laces, Atampa, Voiles, Shoes, Bags, Gowns, Veils and Jewelry masu kyau a farashi me sauqi, Muna Bada sari Kuma Muna siyar da daidai, Muna hada lefe masu Aji🔥🍻kada na cika ku da surutu😌ku garzaya IG page dn www.instagram.com/batoul_fashion_and_boutique don shaida bayanan da na muku da Kuma tabbatarwa ko ku shiga WhatsApp group dn ta https://chat.whatsapp.com/Fi0iCJcvtGKEYcVrbZwxfw za ku iya tuntubarmu a 07025420431
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*MARUBUCOYAR*
*WATA KISHIYAR*
RUBUTACCIYAR QADDARAH*
*HALIN KISHI*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*