Sashe 61
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*Kutuntube mu ta wannan number 📞08129249549*
*📲07011401314*
AUDU
Shirye shirye suke tayi saboda a daren ranar suke saka ran tashin su Binta. Gaba baya ta hargitse gidan ta hada faggon jakunkuna tamkar me zuwa yawon bude ido ba Ibadah ba. Addaba masa tayi akan seya qara mata kudi,
"Kaga fa a can nake so nayi siyayyar kayan haihuwar nan, dan abinda ka bani me naci a ciki me nayo tsaraba sannan duk ciki kake so nayi siyayyar kayan jaririn?" Binta ta fada tana matse fuska sanda yake jaddada mata sisi baze qara mata ba.
Kudade masu kauri ta karba a hannunsa, banda guzurinta ga wanda Babanta ya bata amma a haka take hanqoron se ta sake waftar wasu a hannunsa ya rasa bala'in son kudi irin na Binta kuma ba abin Mamaki bane taje ta dawo daga ita se jakar hannunta dan ya dade da gane Binta bata iya tsinanawa kanta ko waninta da komai a zamansu daga kan sutura zuwa wani abin amfani na gida sabo sedai idan shi ya siyo ko kuma aka mata daga gidansu amma a karan kanta batayi ya kan tuna Bara'atu zamansu duk Azumi zatayi yan kaye kaye ta fitar da tsoffin kayan amfaninta ta maida sababbi banda Bintan.
Data ishe shi da surutu shi kuma ya rantse sile baze qara mata ba se kawai ya shirya ya fita, Gidan Mai ya tafi, mamaki ya kamashi yanda yaransa suke ta yi masa barka da Arziqi Allah ya raya bayan sun gaisa haka ya shige ofishinsa ransa fal da mamakin barkar me ake masa.
Sallama Musbahu yayi ya bashi izinin shiga bakin nan nasa kamar ze taage saboda fara'a ya gaida Audun kana yace
"Yanzu naje na gano yan tagwaye, wlh Baba kamar kayi kaki ka ajiye, duk yaran gidan nan ni banga wanda ma yayi kama da kai kwabo da kwabo kamar su ba".
Kallon Musbahun ya ringayi kamar be fahimci abinda yake fadi ba, so yakeyi ya tambayeshi waya haihu amma kuma ya qiyin hakan a maimakon haka seya miqe yana cewa
"Muje na gano su"
Maganar tasa ta bawa Musbahu mamaki dukda daman yanda ya ganshi tamkar be san da zancen haihuwar ba ya bashi mamaki sannan ya sake shiga duhu akan lamarin, tabbas akwai abinda yake faruwa tun daga daukarsa da Baba Yakubu yayi sukaje can gidan Malam Hassan bayan nan sukaje Asibiti a can din yayi tsammanin tarar da Baba Audun ko matarsa amma yaga akasin haka Inna Balaraba ce kadai se Baba Zayya da suka tafi da ita tare.
Shidai bece komai ba har suka isa Asibitin wanda shi yake tuqi yana gaba Audu na biye dashi a baya har suka isa dakin da aka kwantar Zubaidan tana hutawa. Wani tsalle zuciyar Audu ta buga lokacin da idonsa yayi arba da jinjiri a hannun Baba Zayya tana jujjuyashi, idonsa fes akan yaron ya shiga cikin dakin sosai se ganin mutum sukayi sangangan akan su. Balaraba ta buga tsaki kamar zata tsinke harshenta kafin ta miqe tana cewa Baba Zayyan
"Bari na zagaya"
"Nima bari na biki nasha iska warin magani duk ya cika mun ciki" daga haka ta ajiye jaririn hannunta Musbahu yayi zuruf ya daukeshi suka fice suka barsu a dakin.
Idanu Zubaidan ta rufe tana qara gyarawa yaron data gama shayarwa kwanciya a jikinta, Audu na tsaye tamkar wanda aka sarewa guiwoyi ya kasa gaba ya kasa baya jinin jikinsa ya tsinke haka bugun zuciyarsa ya qaru kamar wanda yake kusa dashi ze iya sauraro. Musbahu ya ajiye yaron hannunsa bayan daya gaka jujjuyashi bakin nan yaqi rufuwa ya fita ganin kamar suna da buqatar sirri. Fitar Musbahun ta dan saukar masa da qwarin guiwa har ya qara taku biyu ya isa gaban gadon sosai yana kallonta tareda yaran da kunyarsu tayi masa lullubi.
Ko a rufa ido aka shafa fuskarsa aka shafa ta yaran an sana halitta dayace balle a kalle su ido biyu, bayan kamannin fuska qirar jiki da kammani na jini duk sun bayyana tattare dasu, ya kai hannu ze sauki wanda Musbahu ya ajiye a ba zata yaji ta daka masa tsawa tace
"Akul ka tabamun yara" ta fada har tana nuna shi da yatsa. Yanda tayi maganar cikin sauti me nuna bacin rai matuqa hakan kuma ya nuna a idanunta tilas ya janye hannunsa daga daukar yaron da ya bude ido yana kallonsa tamkar ya sanshi. A sanyaye kai a qasa tamkar ba Audu uban yan Izza ba ya matsa dab da ita cikin karyayyen sauti yace
"Kiyi haquri ki yafe mun, wlh sharrin shaidan ne".
"Babu wani shaidan face kai da Annamimiyar matarka, ni yanzu babu wani abu daya rage tsakanina dakai ubangiji ya gama mun komai daya wankeni daga zargin da kake neman laqabamun, ciki dai gashi na haifeshi watanni goma sha daya a gidanka cikin qudura ta ubangiji kuma ya bani Yaya masu kama da kai kaga duk iya sharrinku da kaida matarka baku isa ku barranta wadannan yayan da Ahalinku ba, fatana kar Allah yasa su gado mugun hali irin naka. Wlh nayi dana sanin Auranka Audu, da ace na san haka can cikin zuciyarka yake baqiqqirin da ban amince da kai ba.
Ka gwada mun hali me kyau, ka yaudareni da Kyakykyawar Dabi'a. Nayi tsammanin na samu Bangon da zan jingina, jigon da ze tallafi rayuwata ya gyarani ashe kai kayi shirin qarasa tarwatsa rayuwa tane. Rayuwata ta baya ta zama tariyi kai kuma ka niyyati shafamun baqin fentin daya fi na baya muni, shin bakayi tunanin halin da mahaifina ze shiga ba idan yaji wannan mummunan abun daka zargeni dashi?
Anya kai ko da zuciya a qirjinka Audu? Me yasa baka tunani da kwakwalwarka ka sakarwa zuciyarka Linzami?
To wlh ka farka tun kafin lokaci ya qure maka, wannan rayuwar da ka dauka ta rashin tunani babu inda zata kai ka illah Nadama da dana sani mara amfani.
Ita kuma matarka ka gaya mata tabi a sannu, ina tausayawa rayuwar da zatayi a gaba haqqi dabaibaye da ita. Se yanzu na fahimci yanda kuka taru kaka kassara rayuwar Bara'atu kuka laqa mata mata mugun qazafi to wlh haqqinta kadai ya isheku a duniya idan har baku nemi yafiyarta ba ina kuma fatan yanda Ubangiji ya wankeni itama ya wanketa ya bayyana gaskiyar duk wani mugun qulli da kukayi akanta" tana gama fadar haka ta gyara kwanciya ta jera yaranta a gabanta bayan ta bashi baya ta rufe ido zuciyarta na tafarfasa tsanar Audu me tsanani tana hudata.
Badan kar tayiwa Allah butulci ba da tace inama ya jinkirta bata wannan gwalalon kyauta a wani gidan inda yafi na Audu Alkhairi? Amma dukda haka ta godewa Allah ta sake gode masa bisa ni'imar da yayi mata.
Tamkar wanda lakarsa ta tsiyaye haka ya ringa jefa qafafu harya fice daga Asibitin, ya manta da Musbahu sukaje hakanan beyi tunanin mota ba ya ringa taka qafafunsa bude ido kawai yayi ya ganshi a qofar gidansa tundaga Asibitin Murtala, tafiya yayi wadda rabon da yayi irinta a qafa dai ze iya cewa tun Zamanin yana Audu qolo. Binta na zaune a tsakar gida da jama'arta da suka zo yi mata Sallama makwafta da kuma Turai da Mardiyya Wata sabuwar qawa da tayi babu dadewa.
Yanda Audun ya shigo ya saka duk matan binsa da kallo kamar ma be lura dasu ba haka ya tsallaka ta tsakaninsu ya wuce sama, Turai ta kalli Binta kafin tayi mata alama da ta bishi ta miqe tana murmushin yaqe ta sallami maqwaftan ya rage Turai da Mardiyya kafin ta haye sama gurin Audu.
Yana zaune akan kujera yayi irin zaman nan na balance ya bude qafafu da hannayensa kana kallonsa kasan da akwai abinda yake damunsa. Cikin salo da kissa ta bude firji ta dakko ruwan sanyi ta matsa gabansa ta tsiyaya masa tana cewa
"Lafiya dai ka shigo kamar baka cikin hayyacinka?"
Seda ya kwalwale ruwan ya miqa mata kofin kafin ya yunqura ya gyara zamansa yana kallonta dakyau yace
"Zubaida ta haihu"
"An ganta kenan, a ina? To mema ya shafemu da ita ko haihuwar ta? Halan gurin farkan nata ta je ta haihu acan ko?" Ta yi maganar tana yatsina fuska. Miqewa yayi ya nufi daki yana tafiya a hankali yace
"Ta haifi tagwaye duka maza, kamanninsu daya dani"
"Me kake nufi?" Ta miqe a zabure qirjinta na dukan dubu dubu kunnenta na mata amsa kuwwar Tagwaye Maza da ya fada, se ya waiwaya ya kalleta yace
"Karmu fara wannan maganar ma. Kin cuceni kin rabani da matata, waima meye dalilinki na sheganta mun Yaya Binta? Me yasa kikayi haka?"
"Ni na sheganta maka yaya? A yaushe akayi haka? Tsakaninka da Allah ni da kai mun taba magana nace maka cikin Zubaida shegene? Hasashena nayi na fada kai kuma tunda kasan da walakin goro a miya ka tabbatar haka ne to kuma se kazo kace na cuce ka dana maka me? Da kake wannan babatun ma me kake nufi ka karbi cikin kenan ko Yaya?"
"Ciki daman nawane" ya bata amsa yana shigewa ciki dan in ya tsaya din be san me zece mata ba. Gaskiya ta fada magana tayi me harshen damo shi kuma ya hau ya zauna daram wato ta tabbata ya zama wawa kamar yanda Yakubu ya fada Bintan ta karanci rashin tunani irin nasa shiyasa tayi amfani da wannan ta cusa masa tunani a kwakwalwarsa harta kaishi ga yanke danyan hukunci yanzu gashi tun ba'aje ko ina ba ya dawo yana dana sani mara amfani dan yasan ya rasa Zubaida ba zata sake yarda ta komo gidansa a matsayin matar aurensa ba.
*📲07011401314*
AUDU
Shirye shirye suke tayi saboda a daren ranar suke saka ran tashin su Binta. Gaba baya ta hargitse gidan ta hada faggon jakunkuna tamkar me zuwa yawon bude ido ba Ibadah ba. Addaba masa tayi akan seya qara mata kudi,
"Kaga fa a can nake so nayi siyayyar kayan haihuwar nan, dan abinda ka bani me naci a ciki me nayo tsaraba sannan duk ciki kake so nayi siyayyar kayan jaririn?" Binta ta fada tana matse fuska sanda yake jaddada mata sisi baze qara mata ba.
Kudade masu kauri ta karba a hannunsa, banda guzurinta ga wanda Babanta ya bata amma a haka take hanqoron se ta sake waftar wasu a hannunsa ya rasa bala'in son kudi irin na Binta kuma ba abin Mamaki bane taje ta dawo daga ita se jakar hannunta dan ya dade da gane Binta bata iya tsinanawa kanta ko waninta da komai a zamansu daga kan sutura zuwa wani abin amfani na gida sabo sedai idan shi ya siyo ko kuma aka mata daga gidansu amma a karan kanta batayi ya kan tuna Bara'atu zamansu duk Azumi zatayi yan kaye kaye ta fitar da tsoffin kayan amfaninta ta maida sababbi banda Bintan.
Data ishe shi da surutu shi kuma ya rantse sile baze qara mata ba se kawai ya shirya ya fita, Gidan Mai ya tafi, mamaki ya kamashi yanda yaransa suke ta yi masa barka da Arziqi Allah ya raya bayan sun gaisa haka ya shige ofishinsa ransa fal da mamakin barkar me ake masa.
Sallama Musbahu yayi ya bashi izinin shiga bakin nan nasa kamar ze taage saboda fara'a ya gaida Audun kana yace
"Yanzu naje na gano yan tagwaye, wlh Baba kamar kayi kaki ka ajiye, duk yaran gidan nan ni banga wanda ma yayi kama da kai kwabo da kwabo kamar su ba".
Kallon Musbahun ya ringayi kamar be fahimci abinda yake fadi ba, so yakeyi ya tambayeshi waya haihu amma kuma ya qiyin hakan a maimakon haka seya miqe yana cewa
"Muje na gano su"
Maganar tasa ta bawa Musbahu mamaki dukda daman yanda ya ganshi tamkar be san da zancen haihuwar ba ya bashi mamaki sannan ya sake shiga duhu akan lamarin, tabbas akwai abinda yake faruwa tun daga daukarsa da Baba Yakubu yayi sukaje can gidan Malam Hassan bayan nan sukaje Asibiti a can din yayi tsammanin tarar da Baba Audun ko matarsa amma yaga akasin haka Inna Balaraba ce kadai se Baba Zayya da suka tafi da ita tare.
Shidai bece komai ba har suka isa Asibitin wanda shi yake tuqi yana gaba Audu na biye dashi a baya har suka isa dakin da aka kwantar Zubaidan tana hutawa. Wani tsalle zuciyar Audu ta buga lokacin da idonsa yayi arba da jinjiri a hannun Baba Zayya tana jujjuyashi, idonsa fes akan yaron ya shiga cikin dakin sosai se ganin mutum sukayi sangangan akan su. Balaraba ta buga tsaki kamar zata tsinke harshenta kafin ta miqe tana cewa Baba Zayyan
"Bari na zagaya"
"Nima bari na biki nasha iska warin magani duk ya cika mun ciki" daga haka ta ajiye jaririn hannunta Musbahu yayi zuruf ya daukeshi suka fice suka barsu a dakin.
Idanu Zubaidan ta rufe tana qara gyarawa yaron data gama shayarwa kwanciya a jikinta, Audu na tsaye tamkar wanda aka sarewa guiwoyi ya kasa gaba ya kasa baya jinin jikinsa ya tsinke haka bugun zuciyarsa ya qaru kamar wanda yake kusa dashi ze iya sauraro. Musbahu ya ajiye yaron hannunsa bayan daya gaka jujjuyashi bakin nan yaqi rufuwa ya fita ganin kamar suna da buqatar sirri. Fitar Musbahun ta dan saukar masa da qwarin guiwa har ya qara taku biyu ya isa gaban gadon sosai yana kallonta tareda yaran da kunyarsu tayi masa lullubi.
Ko a rufa ido aka shafa fuskarsa aka shafa ta yaran an sana halitta dayace balle a kalle su ido biyu, bayan kamannin fuska qirar jiki da kammani na jini duk sun bayyana tattare dasu, ya kai hannu ze sauki wanda Musbahu ya ajiye a ba zata yaji ta daka masa tsawa tace
"Akul ka tabamun yara" ta fada har tana nuna shi da yatsa. Yanda tayi maganar cikin sauti me nuna bacin rai matuqa hakan kuma ya nuna a idanunta tilas ya janye hannunsa daga daukar yaron da ya bude ido yana kallonsa tamkar ya sanshi. A sanyaye kai a qasa tamkar ba Audu uban yan Izza ba ya matsa dab da ita cikin karyayyen sauti yace
"Kiyi haquri ki yafe mun, wlh sharrin shaidan ne".
"Babu wani shaidan face kai da Annamimiyar matarka, ni yanzu babu wani abu daya rage tsakanina dakai ubangiji ya gama mun komai daya wankeni daga zargin da kake neman laqabamun, ciki dai gashi na haifeshi watanni goma sha daya a gidanka cikin qudura ta ubangiji kuma ya bani Yaya masu kama da kai kaga duk iya sharrinku da kaida matarka baku isa ku barranta wadannan yayan da Ahalinku ba, fatana kar Allah yasa su gado mugun hali irin naka. Wlh nayi dana sanin Auranka Audu, da ace na san haka can cikin zuciyarka yake baqiqqirin da ban amince da kai ba.
Ka gwada mun hali me kyau, ka yaudareni da Kyakykyawar Dabi'a. Nayi tsammanin na samu Bangon da zan jingina, jigon da ze tallafi rayuwata ya gyarani ashe kai kayi shirin qarasa tarwatsa rayuwa tane. Rayuwata ta baya ta zama tariyi kai kuma ka niyyati shafamun baqin fentin daya fi na baya muni, shin bakayi tunanin halin da mahaifina ze shiga ba idan yaji wannan mummunan abun daka zargeni dashi?
Anya kai ko da zuciya a qirjinka Audu? Me yasa baka tunani da kwakwalwarka ka sakarwa zuciyarka Linzami?
To wlh ka farka tun kafin lokaci ya qure maka, wannan rayuwar da ka dauka ta rashin tunani babu inda zata kai ka illah Nadama da dana sani mara amfani.
Ita kuma matarka ka gaya mata tabi a sannu, ina tausayawa rayuwar da zatayi a gaba haqqi dabaibaye da ita. Se yanzu na fahimci yanda kuka taru kaka kassara rayuwar Bara'atu kuka laqa mata mata mugun qazafi to wlh haqqinta kadai ya isheku a duniya idan har baku nemi yafiyarta ba ina kuma fatan yanda Ubangiji ya wankeni itama ya wanketa ya bayyana gaskiyar duk wani mugun qulli da kukayi akanta" tana gama fadar haka ta gyara kwanciya ta jera yaranta a gabanta bayan ta bashi baya ta rufe ido zuciyarta na tafarfasa tsanar Audu me tsanani tana hudata.
Badan kar tayiwa Allah butulci ba da tace inama ya jinkirta bata wannan gwalalon kyauta a wani gidan inda yafi na Audu Alkhairi? Amma dukda haka ta godewa Allah ta sake gode masa bisa ni'imar da yayi mata.
Tamkar wanda lakarsa ta tsiyaye haka ya ringa jefa qafafu harya fice daga Asibitin, ya manta da Musbahu sukaje hakanan beyi tunanin mota ba ya ringa taka qafafunsa bude ido kawai yayi ya ganshi a qofar gidansa tundaga Asibitin Murtala, tafiya yayi wadda rabon da yayi irinta a qafa dai ze iya cewa tun Zamanin yana Audu qolo. Binta na zaune a tsakar gida da jama'arta da suka zo yi mata Sallama makwafta da kuma Turai da Mardiyya Wata sabuwar qawa da tayi babu dadewa.
Yanda Audun ya shigo ya saka duk matan binsa da kallo kamar ma be lura dasu ba haka ya tsallaka ta tsakaninsu ya wuce sama, Turai ta kalli Binta kafin tayi mata alama da ta bishi ta miqe tana murmushin yaqe ta sallami maqwaftan ya rage Turai da Mardiyya kafin ta haye sama gurin Audu.
Yana zaune akan kujera yayi irin zaman nan na balance ya bude qafafu da hannayensa kana kallonsa kasan da akwai abinda yake damunsa. Cikin salo da kissa ta bude firji ta dakko ruwan sanyi ta matsa gabansa ta tsiyaya masa tana cewa
"Lafiya dai ka shigo kamar baka cikin hayyacinka?"
Seda ya kwalwale ruwan ya miqa mata kofin kafin ya yunqura ya gyara zamansa yana kallonta dakyau yace
"Zubaida ta haihu"
"An ganta kenan, a ina? To mema ya shafemu da ita ko haihuwar ta? Halan gurin farkan nata ta je ta haihu acan ko?" Ta yi maganar tana yatsina fuska. Miqewa yayi ya nufi daki yana tafiya a hankali yace
"Ta haifi tagwaye duka maza, kamanninsu daya dani"
"Me kake nufi?" Ta miqe a zabure qirjinta na dukan dubu dubu kunnenta na mata amsa kuwwar Tagwaye Maza da ya fada, se ya waiwaya ya kalleta yace
"Karmu fara wannan maganar ma. Kin cuceni kin rabani da matata, waima meye dalilinki na sheganta mun Yaya Binta? Me yasa kikayi haka?"
"Ni na sheganta maka yaya? A yaushe akayi haka? Tsakaninka da Allah ni da kai mun taba magana nace maka cikin Zubaida shegene? Hasashena nayi na fada kai kuma tunda kasan da walakin goro a miya ka tabbatar haka ne to kuma se kazo kace na cuce ka dana maka me? Da kake wannan babatun ma me kake nufi ka karbi cikin kenan ko Yaya?"
"Ciki daman nawane" ya bata amsa yana shigewa ciki dan in ya tsaya din be san me zece mata ba. Gaskiya ta fada magana tayi me harshen damo shi kuma ya hau ya zauna daram wato ta tabbata ya zama wawa kamar yanda Yakubu ya fada Bintan ta karanci rashin tunani irin nasa shiyasa tayi amfani da wannan ta cusa masa tunani a kwakwalwarsa harta kaishi ga yanke danyan hukunci yanzu gashi tun ba'aje ko ina ba ya dawo yana dana sani mara amfani dan yasan ya rasa Zubaida ba zata sake yarda ta komo gidansa a matsayin matar aurensa ba.