Sashe 70
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya gama maganarsa ya basu damar me magana tayi, Binta da kanta ya gama fasuwa da yanda ya nunawa Bara'atun ita ba komai bace yanzu a gurinsa, taji ina ma haka ta kwantar da kai lokacin daya auro Zubaida tabbas da martaba da qimarta a gurinsa ta zarce ta yanzu amma hakan ma babu laifi zatayi duk iyawarta ta sake kafa kanta.
"Nidai babu wani abu daga gurina, Bara'atu daman tun asali yar uwa na dauketa ba kishiya ba ina fatan kuma itama wannan karon zata saki ranta ta zauna dani zuciya daya, sannan kafin a kai ga maganar rabon kwanaki akankwana uku da zakayi mata na qara muku sati kunga kwana Goma kenan saboda kuji dadin Amarci sosai a tuna baya" Bintan ta fada cikin kissa. Wata dariyar Bosawa Audun yayi, Ita dai Bara'atu kanta yana qasa, to me zata ce musu kuma? Tana jinsu suna ta soki burutsunsu shida matarsa kafin aka rufe taro yace taje yana zuwa.
Bata tsammaci zuwansa da wuri ba se gashi ko minti goma bata rufa da komawa ba ya shiga da ledar kayan Marmari da kaza.
Washe gari haka ta tashi mamaki na neman kasheta, wato Namiji ko, Namiji duk wadda taci laya akansa ta shigenge.
Irin yanda Audun ya ringa mata rawar jiki yana fada mata kalamai jinsa kawai ta ringayi, haka da safe be fita ba, Binta da ta kusa hadiye zuciya cikin dare ta mutu saboda baqinciki da kishi amma tun farar Asuba ta tashi ta hau aikin da babu lada domin ba dan Allah tayi shi ba. Lafiyayyen abin kari tayi musu ta kai qofar dakin Bara'atun ta kwankwasa kafin ta ajiye dan ba zata iya shiga ba zata iya manta shiri takeyi ta bazara komai gayyar ta watse. Haka ta ringa musu wannan kabakin arziqi harna kwana uku kafin ta kasa cigaba, yanda Audun ke rawar jiki akan Bara'atun ya tassama haukatata.
Ita dashi yake ce mata daya san ze samu wannan kwanciyar hankalin da nutsuwa a gidansa da Bara'atu ya maido a maimakon ya Auri Zubaida har yana tambayarta me yasa bata kishi da Bara'atu amma lokacin Zubaida taqi kwantar da hankalinta?
Ta rasa amsar da zata bashi, ba abin ta daddana masa Ashar ba se kawai tace saboda ita Bara'atu a gidan ta tararda kuma Zubaida ba wai kishi da ita takeyi ba kawai Asalinta ne be mata ba da ace itama a gaban Iyayenta ya aurota tamkar Bara'atun da lafiya lau zasu zauna.
Ango Audu dai ya ci karensa babu babbaka ya murji soyayya yanda ya kamata shi da kansa ya tabbatar da akwai banbanci tsakanin Abinda zuciyarka ce take sonsa da kuma wanda wani dalili yasa kake tare dashi. Bazeyi qarya ba yana son Bara'atu, haka Zubaida da kansa ya ganta yaji yana sonta har kuma yanzun da da dama ze maidata itama suci gaba da zama yanda yake jin su biyun a zuciyarsa Binta bata kama qafarsu ba amma kuma ya rasa yanda akayi ta fisu tasiri a ransa, yafi girmamawa da daukar maganarta fiye da tasu menene dalilin hakan?
Seda ya kwana uku cif yana hutun Angwanci kafinya koma fita aiki a ranar kuma Binta ta sauke hau din data dorawa kanta ta yi mush girki ta bar Mairo taci gaba. Baqin cikin data qunsa a kwanakin Allah yayi yawa dashi tana nan kuma tana jiran ranar ramuwa kwanaki goman nan cif su ta bawa Bara'atun matsayin kwanakin farin cikinta a gidan daga nan kuma wasan ze canza salo.
Kamar yanda ta qudurta kuwa haka ce ta kasance kwana goma Audu yayi a dakin Bara'atu wadda zata iya cewa kwanaki goman nan sun zarce shekaru goma na rayuwarta dadi dominbata taba sanin dadin Aure ba a zaman da tayi da Audu kamar na wannan kwanakin. Ya shayar da ita madarar qauna tarairaya da soyayya ba'a magana gaba daya ya goge mata hadda ya kuma goge duk wani shakku da take dashi akansa na cewar ya dena sonta ko yana da wata manufa akan maidota da yayi, walwalarta ta qaru har wani kyau da sheqi ta qara kana ganinta kasan hankalinta a kwance yake Yanda kuma Bintan take sabgogin gabanta bata shige mata irin na wancan karon yasa ta fara tunanin da gaske ta aje makaman yaqinta zasuyi zamane na babu ruwan kowa da kowa wanda zata so hakan.
Randa Audun ze bar dakinta zuwa na Binta har kuka ta masa ya ringa rarrashinta akan kwana biyu ne kacal ze dawo sannan a qarshen satin zasuje su dakko su Babangida ma su dawo gida a saka su a makaranta dan Zakariyya ma za'a dawo dashi duka za'a hadasu a kaisu makaranta me kyau wannan yasa ta dan rage damuwa. Lafiya lau yayi kwanaki biyunsa dakin Binta randa ya dawo matasuka tafi Legas wanda tafiyar tazo mata a bazata ce mata kawai yayi ta shirya zasuje wani guri ta dauki kaya kala biyu farko ma ta dauka Bechi zasuje seda ta ganta a filin jirgi ta shiga zare ido, yau gata zata hau jirgi itama bata sake tsinkewa ba seda suka sauka yace mata Legas sukazo ta ringa tsalle kamar yarinya kamar wasa se gasu a gidan su Yakubu.
https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*PAGE 27*
Da murna tayi musu yawa ita da Balaraban se kawai suka fasa kuka, Yakubu ko bakinsa ya kasa rufuwa, Audun ya shammaceshi dan besan duk abinda ya faru ba wannan abun da yayi kuma ya saka ya wanke duk fushin sa da yake damfare a ransa yaji matuqar dadin ganinsu ko ba'a fada ba kuma yasan hankalin kowannensu a kwance yake.
Aka ringa hirar yaushe gamo, A gidan sukayi kwanaki biyunsu dukda Audu yaso su kama Hotel tunda gidan qarami ne dakuna biyu ne daga nasu Yakubun se na yaransu amma Yakubu yace dole su zauna haka baquntar kwana biyu dai haka suka dawo Kano cike da kewa dan kwanaki biyun ba qaramin dadi yayi musu ba sun fita yawo har bakin ruwa sukaje aka musu hotuna Audu be taho ba seda aka wanke musu hotunan suka taho da kwafi dinsu.
A kwanaki biyu ba qaramin Ilimi Balarana ta zazzagawa Bara'atu ba da kuma wanda ta gani da idonta ta koyo, sun dawo ta qudiri niyyar tabuka abin kirki a wannan karon itama, zatayi amfani da duk dabarun data koya mata na riqe Miji, zatayi iyakar yinta yanda ba fata takeyi ba koda ace wani abu ya sake faruwa badai a zargeta da sakarci ko rashin sanin ciwon kai ne ya janyo mata ba.
Tafiyarsu Legas ta qara rura wutar bala'i a zuciyar Binta, dukda ya gaya mata kafin su tafi abin ya zafeta matuqa harta kasa jurewa ranar da suka dawo a dakinta ya sauka bata iya shanyewa bata amayar masa da abin da yake cikinta tas akaci sa'a be kulata ba domin shima ya qaro karatun zama da mata, ya san da akwai abubuwan da mace zatayi wanda Kishine yake tunzurasu babu yanda kuma zakayi da ita dole kayi haquri.
Watanni uku da dawowar Bara'atu, a hankali kyakykyawan zaman daya fara ginuwa tsakanin Ma'auratan ya fara samun tazgado, salon da Binta tayi amfani dashi a zamansu na farko da Bara'atu shita sake maidowa na cusguna mata ta hanyar bautar da ita da kuma zaginta tareda muzantata sedai a wannan karon ta canza salo ta kuma biyo ta hanyar da a qaramin wayo da Dabarar Bara'atu ba zata iya kaucewa Kaidinta ba.
Da farko ta dakatar da Lantana da Mairo daga zuwa aikinsu wanda tayiwa Audu qaryar Lantana sata takeyi mata shiyasa ta koreta ita kuma Mairo ta dakatar da ita ne kawai su ringayin girkinsu da kansu be kyautu ace abincin me aiki ze ringa ci ba bayan yana da mata har biyu sauran Ayyukan gidan ma duk bazasu gagaresu,
"Da ze yuwu mu zauna da Maman su Baba mu tsara yanda zamu ringa ayyukanmu kawai ba se wani ya taimaka mana ba. A gidan Yaya Aminu naga irin tsarin ya burgeni kuma hakan ya qara shaquwa da fahimta a tsakanin matansa kana gani duk gidanku babu Kishiyoyi masu fahimtar Juna kamar matansa haka yayansa kansu a hade baka ma iya banbance wannan na waye to nima irin zaman da nake so mu gina a gidan nan kenan duk abubuwan da suka faru a baya su zama tarihi mu tun kari gaban mu" abinda Bintan ta tsarawa Audu kenan cikin salo na zallar kissa da iya hada tuggu.
Audun yayi na'am da shawararta kuma yaji dadi, tabbas Matan Aminun abin kwatance ne yanda suke zaune tamkar Dadansu da Goggo Fadi kafin rasuwar Malam Tijjani, haka suka tashi gidansu aiki da komai tare su Dadan su keyi kwana a Turakar megida ne kadai ze nuna maka wadda take da Girki a cikinsu shiyasa shawarar tayi masa dadi yasan kuma Bara'atu ma zatayi Na'am da hakan itama.
Sanda ya sanarda Bara'atu hukuncin da Bintan ta yanke na sallamar su Lanatana batace komai ba saboda daman ba ita suke yiwa aiki ba, sharar tsakar gida kadai abinda take mora a aikin nasu tunda ba Girki daya sukeyi ba kamar dai farkon zamansu ne me Miji tayi abinci dashi har gara Mairon tana kama mata wasu abubuwan idan tana girki a Kitchen din tsakar gidan Lantana kuwa kallon Arziqi ma baya hadasu balle aje a ga batun tayata aiki shiyasa sallamar masu aikin bata dameta ba.
Anyi kwana biyu da maganar ya tarasu falonsa domin tsara yanda zasu raba aikin gidan, Binta ce da girki ranar tana ta kai kawon hada musu abinci su duka gaba daya harda yaran dan sun dawo Abdullahi ma anyi hutun makaranta yana komawa gida ya samu labarin Innarsa ta koma Kano kwanansa biyu shima ya hado kayansa ya taho Audu da Binta suka ringa masa tsiya.
Seda aka qare cin abincin suka sallami yaran suka sauka qasa kafin suka nutsu cikin kujera dan yin maganar data tarasu din.
"Nidai babu wani abu daga gurina, Bara'atu daman tun asali yar uwa na dauketa ba kishiya ba ina fatan kuma itama wannan karon zata saki ranta ta zauna dani zuciya daya, sannan kafin a kai ga maganar rabon kwanaki akankwana uku da zakayi mata na qara muku sati kunga kwana Goma kenan saboda kuji dadin Amarci sosai a tuna baya" Bintan ta fada cikin kissa. Wata dariyar Bosawa Audun yayi, Ita dai Bara'atu kanta yana qasa, to me zata ce musu kuma? Tana jinsu suna ta soki burutsunsu shida matarsa kafin aka rufe taro yace taje yana zuwa.
Bata tsammaci zuwansa da wuri ba se gashi ko minti goma bata rufa da komawa ba ya shiga da ledar kayan Marmari da kaza.
Washe gari haka ta tashi mamaki na neman kasheta, wato Namiji ko, Namiji duk wadda taci laya akansa ta shigenge.
Irin yanda Audun ya ringa mata rawar jiki yana fada mata kalamai jinsa kawai ta ringayi, haka da safe be fita ba, Binta da ta kusa hadiye zuciya cikin dare ta mutu saboda baqinciki da kishi amma tun farar Asuba ta tashi ta hau aikin da babu lada domin ba dan Allah tayi shi ba. Lafiyayyen abin kari tayi musu ta kai qofar dakin Bara'atun ta kwankwasa kafin ta ajiye dan ba zata iya shiga ba zata iya manta shiri takeyi ta bazara komai gayyar ta watse. Haka ta ringa musu wannan kabakin arziqi harna kwana uku kafin ta kasa cigaba, yanda Audun ke rawar jiki akan Bara'atun ya tassama haukatata.
Ita dashi yake ce mata daya san ze samu wannan kwanciyar hankalin da nutsuwa a gidansa da Bara'atu ya maido a maimakon ya Auri Zubaida har yana tambayarta me yasa bata kishi da Bara'atu amma lokacin Zubaida taqi kwantar da hankalinta?
Ta rasa amsar da zata bashi, ba abin ta daddana masa Ashar ba se kawai tace saboda ita Bara'atu a gidan ta tararda kuma Zubaida ba wai kishi da ita takeyi ba kawai Asalinta ne be mata ba da ace itama a gaban Iyayenta ya aurota tamkar Bara'atun da lafiya lau zasu zauna.
Ango Audu dai ya ci karensa babu babbaka ya murji soyayya yanda ya kamata shi da kansa ya tabbatar da akwai banbanci tsakanin Abinda zuciyarka ce take sonsa da kuma wanda wani dalili yasa kake tare dashi. Bazeyi qarya ba yana son Bara'atu, haka Zubaida da kansa ya ganta yaji yana sonta har kuma yanzun da da dama ze maidata itama suci gaba da zama yanda yake jin su biyun a zuciyarsa Binta bata kama qafarsu ba amma kuma ya rasa yanda akayi ta fisu tasiri a ransa, yafi girmamawa da daukar maganarta fiye da tasu menene dalilin hakan?
Seda ya kwana uku cif yana hutun Angwanci kafinya koma fita aiki a ranar kuma Binta ta sauke hau din data dorawa kanta ta yi mush girki ta bar Mairo taci gaba. Baqin cikin data qunsa a kwanakin Allah yayi yawa dashi tana nan kuma tana jiran ranar ramuwa kwanaki goman nan cif su ta bawa Bara'atun matsayin kwanakin farin cikinta a gidan daga nan kuma wasan ze canza salo.
Kamar yanda ta qudurta kuwa haka ce ta kasance kwana goma Audu yayi a dakin Bara'atu wadda zata iya cewa kwanaki goman nan sun zarce shekaru goma na rayuwarta dadi dominbata taba sanin dadin Aure ba a zaman da tayi da Audu kamar na wannan kwanakin. Ya shayar da ita madarar qauna tarairaya da soyayya ba'a magana gaba daya ya goge mata hadda ya kuma goge duk wani shakku da take dashi akansa na cewar ya dena sonta ko yana da wata manufa akan maidota da yayi, walwalarta ta qaru har wani kyau da sheqi ta qara kana ganinta kasan hankalinta a kwance yake Yanda kuma Bintan take sabgogin gabanta bata shige mata irin na wancan karon yasa ta fara tunanin da gaske ta aje makaman yaqinta zasuyi zamane na babu ruwan kowa da kowa wanda zata so hakan.
Randa Audun ze bar dakinta zuwa na Binta har kuka ta masa ya ringa rarrashinta akan kwana biyu ne kacal ze dawo sannan a qarshen satin zasuje su dakko su Babangida ma su dawo gida a saka su a makaranta dan Zakariyya ma za'a dawo dashi duka za'a hadasu a kaisu makaranta me kyau wannan yasa ta dan rage damuwa. Lafiya lau yayi kwanaki biyunsa dakin Binta randa ya dawo matasuka tafi Legas wanda tafiyar tazo mata a bazata ce mata kawai yayi ta shirya zasuje wani guri ta dauki kaya kala biyu farko ma ta dauka Bechi zasuje seda ta ganta a filin jirgi ta shiga zare ido, yau gata zata hau jirgi itama bata sake tsinkewa ba seda suka sauka yace mata Legas sukazo ta ringa tsalle kamar yarinya kamar wasa se gasu a gidan su Yakubu.
https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*PAGE 27*
Da murna tayi musu yawa ita da Balaraban se kawai suka fasa kuka, Yakubu ko bakinsa ya kasa rufuwa, Audun ya shammaceshi dan besan duk abinda ya faru ba wannan abun da yayi kuma ya saka ya wanke duk fushin sa da yake damfare a ransa yaji matuqar dadin ganinsu ko ba'a fada ba kuma yasan hankalin kowannensu a kwance yake.
Aka ringa hirar yaushe gamo, A gidan sukayi kwanaki biyunsu dukda Audu yaso su kama Hotel tunda gidan qarami ne dakuna biyu ne daga nasu Yakubun se na yaransu amma Yakubu yace dole su zauna haka baquntar kwana biyu dai haka suka dawo Kano cike da kewa dan kwanaki biyun ba qaramin dadi yayi musu ba sun fita yawo har bakin ruwa sukaje aka musu hotuna Audu be taho ba seda aka wanke musu hotunan suka taho da kwafi dinsu.
A kwanaki biyu ba qaramin Ilimi Balarana ta zazzagawa Bara'atu ba da kuma wanda ta gani da idonta ta koyo, sun dawo ta qudiri niyyar tabuka abin kirki a wannan karon itama, zatayi amfani da duk dabarun data koya mata na riqe Miji, zatayi iyakar yinta yanda ba fata takeyi ba koda ace wani abu ya sake faruwa badai a zargeta da sakarci ko rashin sanin ciwon kai ne ya janyo mata ba.
Tafiyarsu Legas ta qara rura wutar bala'i a zuciyar Binta, dukda ya gaya mata kafin su tafi abin ya zafeta matuqa harta kasa jurewa ranar da suka dawo a dakinta ya sauka bata iya shanyewa bata amayar masa da abin da yake cikinta tas akaci sa'a be kulata ba domin shima ya qaro karatun zama da mata, ya san da akwai abubuwan da mace zatayi wanda Kishine yake tunzurasu babu yanda kuma zakayi da ita dole kayi haquri.
Watanni uku da dawowar Bara'atu, a hankali kyakykyawan zaman daya fara ginuwa tsakanin Ma'auratan ya fara samun tazgado, salon da Binta tayi amfani dashi a zamansu na farko da Bara'atu shita sake maidowa na cusguna mata ta hanyar bautar da ita da kuma zaginta tareda muzantata sedai a wannan karon ta canza salo ta kuma biyo ta hanyar da a qaramin wayo da Dabarar Bara'atu ba zata iya kaucewa Kaidinta ba.
Da farko ta dakatar da Lantana da Mairo daga zuwa aikinsu wanda tayiwa Audu qaryar Lantana sata takeyi mata shiyasa ta koreta ita kuma Mairo ta dakatar da ita ne kawai su ringayin girkinsu da kansu be kyautu ace abincin me aiki ze ringa ci ba bayan yana da mata har biyu sauran Ayyukan gidan ma duk bazasu gagaresu,
"Da ze yuwu mu zauna da Maman su Baba mu tsara yanda zamu ringa ayyukanmu kawai ba se wani ya taimaka mana ba. A gidan Yaya Aminu naga irin tsarin ya burgeni kuma hakan ya qara shaquwa da fahimta a tsakanin matansa kana gani duk gidanku babu Kishiyoyi masu fahimtar Juna kamar matansa haka yayansa kansu a hade baka ma iya banbance wannan na waye to nima irin zaman da nake so mu gina a gidan nan kenan duk abubuwan da suka faru a baya su zama tarihi mu tun kari gaban mu" abinda Bintan ta tsarawa Audu kenan cikin salo na zallar kissa da iya hada tuggu.
Audun yayi na'am da shawararta kuma yaji dadi, tabbas Matan Aminun abin kwatance ne yanda suke zaune tamkar Dadansu da Goggo Fadi kafin rasuwar Malam Tijjani, haka suka tashi gidansu aiki da komai tare su Dadan su keyi kwana a Turakar megida ne kadai ze nuna maka wadda take da Girki a cikinsu shiyasa shawarar tayi masa dadi yasan kuma Bara'atu ma zatayi Na'am da hakan itama.
Sanda ya sanarda Bara'atu hukuncin da Bintan ta yanke na sallamar su Lanatana batace komai ba saboda daman ba ita suke yiwa aiki ba, sharar tsakar gida kadai abinda take mora a aikin nasu tunda ba Girki daya sukeyi ba kamar dai farkon zamansu ne me Miji tayi abinci dashi har gara Mairon tana kama mata wasu abubuwan idan tana girki a Kitchen din tsakar gidan Lantana kuwa kallon Arziqi ma baya hadasu balle aje a ga batun tayata aiki shiyasa sallamar masu aikin bata dameta ba.
Anyi kwana biyu da maganar ya tarasu falonsa domin tsara yanda zasu raba aikin gidan, Binta ce da girki ranar tana ta kai kawon hada musu abinci su duka gaba daya harda yaran dan sun dawo Abdullahi ma anyi hutun makaranta yana komawa gida ya samu labarin Innarsa ta koma Kano kwanansa biyu shima ya hado kayansa ya taho Audu da Binta suka ringa masa tsiya.
Seda aka qare cin abincin suka sallami yaran suka sauka qasa kafin suka nutsu cikin kujera dan yin maganar data tarasu din.