← Book details Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 34 OF 137

Sashe 34

Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

*Ina kuke Mata Yan kwalisa , Ina nufin isassun Mata ,Wai shin Kuna da labarin shahararren company nan namu na GHT wato good healthtreatments*
*Wanda yazo muku da fitattu Kuma* *ingantatattun suppliment ,na dukkan matsalolin ku*❓

*Ina maisan tayi kyau,irin na isassun Mata ya fitar Miki da shef dinki tayi Miki gyara in and out ,nemi royal jelly dinmu na company GHT*
*Wanda aka yishi da xuma ,kundai San amfanin Zuma basai na fada miku ba , hajiya ta kixo ki Yi gyara domin ki kerewa sa,a kije taro ko baki da ko sisi kiji Ana rangada Miki hajiya , saboda yanda Zaki Kara kwarjini ,kina walwali acikin mutane , magungunan ght anti agen ne suna maida tsohuwa* *yarinya ,yarinya Kuma ta koma jaririya*

*Muna da magunguna iri iri*

*NA GYARAN JIKI*
*NA GOGE NANKARWA*
*NA RAGE QIBA*
*NA CIRE TUMBI*
*NA QARIN HIPS*
*NA GIRMAN BREAST*
*NA QARA TSAHON GASHI*

*NA QARIN NI'IMA WANDA ZAI SAUKAR MIKI DA NI'IMA YA QARA MIKI DADI DA ZAQI A GURIN OGA*

*Muna da hadin bita zai zai ,indai kishiyar ki tana Shan magungunan GHT, tohh lallai sunan ki sorry domin kuwa tazarar dake tsakanin ku kamar tazarar sama ne da kasa*

*Muna da Wanda zai matseki ciki da waje Andai na yayin dinki uwargida*,

*Sannan company mu na GHTBai tsaya anan ba*
*Ya kawo muku maganin dukkan matsalolin ku*

*INA MASU HAWAN JINI?*
*INA MASU CIWON ZUCIYA?*
*INA MASU CIWON QODA?*
*INA MASU CIWON HANTA?*
*INA MASU SICKLER?*
*INA MASU HIV?*
*INA MASU CANCER?*
*INA MASU NEMAN HAIHUWA?*

*Tohh Ku matso GHT taxo muku da magungunan matsalolin ku*
*Kuma muna da testimonys da yawa ,na wadanda suka gwada suka da ce*

*Munanan a KANO KUNTAU*
*Kuma muna tura Kaya ko wanne gari cikin aminci da gaskiya , kuma kayan mu muna badashi ne cikin price Mai rahusa ga kyau ga inganci sannan ga Rahusa*

*Kutuntube mu ta wannan number 📞08129249549*
*📲07011401314*

Washe gari.

"Nifa wlh Ji nake kamar na rufeki da duka Bara'atu" Balaraba ta fada kafin taci gaba da cewa
"Banda tsabagen abin haushi Bintar me? Me akayi akayi wata Binta da zaki zauna ta shigo gidanki ta mayar dake yar kallo bayan ke kika ci wuyar Audun kika zauna dashi tun bashi da ko sisi har ya zama mutum ta ganshi ta aura na tabbata wlh a rayuwar da kikayi dashi Binta ko a me wanke mata kaya ba zata dauke shi ba. Amma shine kika zauna kika barta take zuba miki mulki a gida kin zama yar kallo jibeki dan Allah yanda kika qwanjale kika fita hayyacinki tamkar me wani ciwo ita kuwa tana walwala da farin ciki Miji na hannunta wlh tun wuri idan zaki farka gara, ki amshi Mijinki da matsayinki, ke kika sha wuya dashi dan haka yanzu kamata yayi duk wadda zataji dadinsa to a bayanki take".

"Kema dai kya fada Yaya Balaraba" Aisha ta tsoma musu baki taci gaba da cewa
"Koni da nake zaune a qauye wlh bazanyi sokoncin da Yaya Bara'atu takeyi ba banga wata kishiya da zanji tsoro ba, ba daga Kaduna ba ko daga Ingila ya aurota qarewar Bariki sena gwada mata nawa wayon qauyen dukda shima Yaya Audu da laifinsa ko nace ma yafi kowa laifi. Wancan zuwan da sukayi da Yaya Ummaru ya masa magana akan abinda tayi lokacin auran Saleh cewa yayi wai ayi haquri shi baya iya mata fada saboda idan ya duba yaga komai ya samu yanzu a rayuwa Ubanta ne sila kuma shi uban a duniya babu abinda yake so kamarta shi yasa yake mata lamuni kiji wani rainin hankali fa se kace wata diyar Qaruna ko kuma yanke Talauchi suka bashi".

Balaraba taja tsaki kamar zata tsinke harshenta kafin tace
"Saboda ubanta ya masa silar arziqi se akace tafi kowacce Mace ko yaya? Rabonsa ne a jikinsu kuma ko zasu bashi su haukace se yaci kawai tsabar mugun hali ne irin na maza matar da aka sha wuya tare da ita bola wadda zata diro rana daya itace abokiyar cin arziqi kuma wlh Audu ya bani mamaki a irin yanda kowa yasan yana qaunar Bara'atu ban taba tsammanin ko Gimbiya Elizaabeth ya auro ze fifitata akan Bara'atu ba"

"Abin ne nake ga kamar harda Asiri" Aisha ta sake fada Balaraba ta harareta tace
"Aikin kenan kullun ace Asiri, shin maza basa isakanci dole se an musu Asiri da yawa da haka suke fakewa ayita daukar Alhakin matan da basu ji ba basu gani ba ace asirce su sukayi, shidai Audu daman halinsa ne be fito ba se yanzu daman kuma kinsan kudi shi yake nuna ainihin kalar mutum ita kuma Binta tayi amfani da wannan damar take zuba sharafinta tunda shi ya bata qofa. Ni da Allah tashi kije ki karbo musu idan ba haka ba kuma naje da kaina" ta qarashe tana kallon Bara'atu data sunkuyar da kai idonta ya tara kwalla dalilin maganganun da sukeyi. Tun jiya Balaraba take mitarzancen nan, babu wanda ze fuskanci halin da take ciki kowa sedai yace mata wawuya ko sakarya ta kasa kwatar yan cin kanta ta sakarwa Kishiya ragamar gidanta daga zuwa to dan Allah base ta samu kwarin guiwa da Adalci daga gurin wanda ya ajiye su ba?

"Bari kiga na tashi" Balaraba ta sake fada tana yunqurawa dakyar saboda tsohon cikin dake jikinta nan Bara'atu ta zabura ta miqe tana cewa
"Bari naje, ni magana ce ban so wlh da kun barni yanzu se a dora musu wani tunda dai ta bamu iya rabon mu" da haka ta fice daga dakin tana jin Balaraban na zaginta. Yan Bechi na ganinta sukayi mata caa suna cewa
"Yawwa Hajiya Bara'atu, tun dazu muke jira a qaro abincin kinga yara se kukan yunwa suke wasu ko karin safe ba suyi ba muka fito". Da wani yanayi tace musu
"Kuyi haquri yanzu za'a kawo" ta fice daga falon zuciyarta na bugawa cike da taraddadin abinda ze biyo baya idan taje tace a qara musu abincin, dukda cewar su sukayi wahalar dafashi ita da wasu daga cikin yan uwan Audu da suka fara yowa gaba tun ana jibi suna. Seda suka dafe shinkafa kwano goma sha biyar, dambu kwano bakwai ga tuwon safe na kwano bakwai amma banda su Waina, Funkaso Alale da sauran tarkacensu irin na yan gayu da suka kai akayo musu daga waje amma a ciki tuwo Malmala goma suka basu se shinkafar da bata fi rabin kula madaidaiciya ba tun hantsi be gama dagawa ba kuma suka kusa cinye shi saboda ba'a karya ba duk suna jiran a kammala abinci sannan ga ma'aikatan da suka tayasu duk a ciki ta debar musu suka tafi dashi gidajensu gaba daya yan uwan Bintan suka lode abincin a Kuloli suka kai daki.

A hankali take gifta matan dake zaune tsakar gidan yan suna, wasu maqwaftansu ne wasu kuma qawayen Binta da matana Abokanan Audu wanda suke hulda da ita kadai duk kuma rukunin data wuce zata musu sannu wasu su amsa wasu suyi mata banza harta dangana da qofar falon Binta,
"Maman Baba" taji an kirata ta waiwaya fuskarta ta fadada da murmushi ganin Maman Kabir ce maqociyarta guda daya da suke sabgar Arziqi gaba daya sauran Binta ta kwace su ko tace sun koma gurin Bintan.

"Se yanzu zaki shigo mana" ta fada tana jan kumatun Kabir dake hannunta ya kuwa janye ya lafewa mamansa tayi dariya tace
"Maquyacin kawai"
"Tun safe naso na leqo baqi nayi wlh se yanzu suka tafi" Maman Kabir din ta fada. Bara'atu tayi murmushi tace
"Na sani tsokanarki nakeyi dazu Shamsiyya ta shigo ai tace Yayan Baban Kabir ne yazo, qarasa ciki to yanzu zanzo abu zan karbo gurin Binta".

"Ai gara na biki nima naga Jinjiri kafin na zauna" Maman Kabir ta fada hakan yasa suka shiga falon Bintan tare. Yayyenta na tsaitsaye a falon sun hada kai suna magana sallamar su Bara'atu ta sakasu zabura tamkar marasa gaskiya, Yaya Salima ta qaqalo fara'a ta yabawa fuskarta tana kallon Bara'atu tace
"Aa uwargida an leqo? Sannunku fa da aiki"
"Uhm" Bara'atun tace kafin kanta a qasa cike da taraddadi tace mata
"Daman yan Bechi da suka zo yanzu ne Abinci be isa ba shine nace ko za'a dan qaro musu"

"Aikin kenan abinci Abinci koda yake ba a saba ci ba, banda jaraba ma suna amma anyo gayya kamar wani Bikin fari wato za'azo aci banza to babu kowa ya nade yunwarsa ya koma da ita" Munira wadda take autarsu Bintan amma ta rigata aure ta fada cikin Fitsara se Yaya Saliman tayi saurin tareta tana cewa
"Haba ke kuwa Munira Abinci dai Allah na tuba abin aci ayi kashi kuma fa mutanen nan dangin me gidan ne idan ba'a basu ba to su za'a bawa? Barta dan Allah Bara'atu shiga ciki ki gayawa yar uwartaki se muji kamar Adadin da za'a zuba musu" ta qarasa tana nuna mata qofar dakin Bara'atu.

Maman Kabir da takaici ya quleta, ba abin tayi magana ba ta jawa Bara'atun ta juya kawai ta fita tana ce mata
"Bari naje an jima kan na tafi ma gaisa da ita" Bara'atu kuwa a sanyaye ta tura qofar dakin Bintan da sallama wanda tun zuwanta gidan shekara guda sau daya ta taba takashi randa aka kawota, ko ranar da zata haihu a qofar falo suka hadu ta taimaka mata suka tafi Asibiti. Zuciyarta duk babu dadi ta shiga, ita abincinma ko kalarsa bata dandana a harshenta ba da suka gama girkin shayi ta kada tasha saboda yanda ta gaji sannan duk taron Jama'ar da suke iqirarin sunzo cin banza Jininta biyu ne a ciki Hadiza wadda dama tare suke zama se Ubaida data biyo yan zuwa suna saboda taga Yan uwan nata ragowar dukfa Dangin Audu ne, qanne da yayyensa da Matan yan uwansa se Maman Kabir Qawarta tilo da ta shigo yanzu wadda tana da tabbacin harta fita be zama lalle ko ruwan fanfon gidan tasha ba.
Chapter 34 · 0% Book details