Sashe 132
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ya nisa kamar bazeyi magana ba se kuma yace
"Momy Fatima ce na kasa gane kanta"
"Matsala kuka samu?" Ta tambayeshi tana nazartarsa. Ya karkace kamar zeyi mata kuka yace
"Ni dai babu abinda nayi mata Momy itace dai bansan ko na mata wani abu ba. Gaba ɗaya ta canza duk na kasa gane kanta".
"Ahmad kama Addu'a kuwa akan lamarin yarinyar nan?" Ta tambayeshi, yaja rantsuwa yace
"Wlh ina yi Momy, ko jiya kwana nayi ina sallah ina addu'ar neman zaɓin Allah amma wlh kamar an ƙaramun sonta a maimakon ya ragu a zuciyata"
"Kuma ba addu'ar son rai kakeyi ba? Kana cewa kana neman zaɓin Allah amma kuma ranka ba haka bane ka rigada ka zaɓarwa kanka abinda kake so?" Momy ta sake faɗa tana dubansa yace
"Momy shekara uku fa kenan, na san ba nacina ko dagiyata ce zata bani abinda nale so ba amma kuma Allah na barwa zaɓina ina ganin da inada wani haske daban bayan ita da yanzu na ganshi amma Momy ita ɗin dai ita na gani nake kuma ji a jikina itace matata".
"Toh addu'ar dai ita zamu cigaba dayi akan koma menene Allah ya warware sannan damuwar daka saka a ranka ba zata amfana maka komai ba kayi Ƙoƙari ka cireta, duk abinda Allahya saka cewar rabon bawa ne a duniya seya same shi idan kuma ba rabonka bane duk wuya haka zaka haƙura domin ba zaka sameshi ba. Sannan kuma ni ina ganin cewar harda halinka yasa yarinyar nan take maka koma menene"
Ya zabura yace
"Halina kuma Momy? Me nakeyi?" Momy tace
"Shekara uku kace da bakinka yanzu, wace irin soyayya ce haka har yanzu da za'ace ba za'ayi aure ba? Kaida bakinka kace mun mahaifinta yace maka ko tana cikin makaranta idan ka shirya aurar da ita zeyi to me kake jira har yanzu? Kana tsammanin zata cigaba da zaunawa tana ɓata lokaci dakai ne Alhalin ƙila tana da wasu masoyan da suka fika himma?"
Yayi shiru dan besan bayanin da zeyiwa Momy ta fahimta ba. Baya so ya ɓata Fatima a idonta ta hanyar sanar mata cewar itace har yanzu batayi na'am dashi ba kuma ita taƙi bashi damar ya tura ayi maganar auransu idan kuma yayi shiru Momy zata cigaba da bashi laifi na cewa shi yake ɓatawa Fatiman lokaci wannan yasa ta karkata hankalinta ga wani daya fishi himma kamar yanda tace.
"To ai Momy yanzu tana Level 4 har sun gama First semester da bari nayi tunda son zo ƙarshe kawai ta ƙarasa daganan se aje ayi magana"
"Oh so kakeyi harta gama makarantar tazo ta zauna sa'annan ka gama shiriritarka se aje ayi maganar aure ko? Lallai kuwa kana zaune nan zakaji wani ya aureta. Waima sanyar me kakeyi ne? Ina kace tun tuni ka sanar da Alhaji maganar nan me kake jira da ba zaka sake tayar masa da ita ba tunda ka nace lallai se shi zaka kaiwa maganar auranka?"
"Aa Momy ba haka bane ba, naga ai Alhaji ne Ahaƙƙu da na sanarwa da zancen aurena idan yaso shi kuma ya iya saka wakili ya shige mun gaba" ya bata amsa kai a ƙasa. Momy ta harareshi tace
"Sannu uban fitar da Ƙoƙon Asali, dama dai yanda kake da ƙulafucin uban nan shima haka yake ta taka amma na tabbata yanzu ya manta ma da kunyi wata magana data shafi zancen auranka dashi. Se kaje ka sake samunsa ai ka tuna masa, idan kuma yace Aa kaga aiseka fara sabon lissafi tunda ga tudun dafawar da duk yanda aka ciza ze tsaya maka kace baka san zance ba ba zakaje ta wurinsa ba".
"Ni Momy bana so a sakeyin irinta Yaya Sarki kina kallo dai Alhaji swda yayi ta faɗa akan ya zameshi daga maganar auransa shiyasa amma ba wani abu ba kuma nasan ai dai ko shi na gayawa dole dai Baba Alƙalin ze wakilta" ya sake faɗa Momy tace
"Ai shikenan, amma dai mafita guda ce in har da gaske kake son yarinyar nan manya su shiga maganarku, kaje ka samu ubanka ka fayyace masa komai ya tura a nema maka auranta in kuma zaka zauna nuƙu nuƙun ne kuma shikenan"
"Toh Momy zanje" daga nan suka bar maganar suka shiga wata. Bayan fitarsa ya ringa shiryawa yana warware ta yanda ze sake tunkarar Alhaji da zancen aurensa da Fatima. Amma ta yaya ma ze taso magana alhalin ita wadda za'a aura ɗin bata yarje masa ba?
Ya samu jikin katanga ya lafe ya shiga kiran layinta, yanzu abin ya sake ta'azzara har rejecting take in bata ga damar amsawa ba kuma ya dameta, So hana ganin laifi haka yake jurewa domin ya yarda ƙaddarar sa ce Son Fatima. A kira na biyu ta amsa muryarta ta shaida masa bacci takeyi dan haka yace
"Kiyi haƙuri na tasheki a bacci"
"Babu komai ina zaune ne nima ban san baccin ya kwasheni ba, ina wuni?" Ta gaidashi. Tana da kirki, tana da tarbiyya, Mahaifanta mutane ne kai tana da duk wani quality da yake nema a gurin matar auransa baya zaton idan ya barta ze damu full option abinda yake nema a gurin mace tamkar nata ya ayyana a ransa.
"Kina free yau da dare zanzo?"
"Eh" ta bashi amsa a taƙaice, shikenan ya mata sallama akan se bayan Magriba zeje haka kuwa akayi yaje yayi aski ya ɗan shiga saiti ana sallar Magriba ya sha kwalliya ya tafi gidansu. A can yayi sallar Isha a masallacinsu Baffa kafin suka ƙarasa gidan tare. A ƙofar gida Baffa ya dubeshi yace
"Malam Ahmad na bawa Mamana Saƙo kusan sati nawa amma banji amsa ba".
Da rashin fahimta ya dubi Baffan kafin cikin girmamawa yace
"Ina ganin ta sha'afa ne Baffa ko kuma nine na manta da ta gayamun amma wace magana ce?"
Baffa yayi murmushi yace
"Dama maganar zuwan magabatanka ne nace lokaci yayi daya kamata ace manya sun shiga cikin maganar nan, ni badan ka buye ta tata ba kace a barta ta gama karatun kamar yanda take so ai da tuni kuma ka huta da biyo dare kana maƙalewa jikin katanga" Baffa yayi masa barkwanci. Yayi yar dariya yana sosa Ƙeya, Baffa ya sake cewa
"To ina sake maimaita maka tunda da alama ta sha'afa kamar yanda kace, a sanar musu saboda a san abinda ake ciki"
"In sha Allahu Baffa zan sanar musu" ya faɗa kai a ƙasa, Baffa ya wuce ciki yana masa Addu'a da fatan Alkhairi. Shiya turo masa Fatima wadda ta manta da batun zuwan Ahmad ɗinma seda Baffa yace mata yana waje. Dogon Hijab ta saka, bata shafa ko hoda ba ta fito tana bulbula ƙamshin designer perfumes ɗin da yake kai mata akai akai. Ta gaishe shi ya ringa kallonta kullum ya ganta ƙara sonta yakeyi, jinta yakeyi har tsakiyar ransa shi be taɓa sanin haka So yake ba seda ya afkawa kogin ƙaunar Fatima.
"Yanzu Baffa yake cemun ya baki saƙo amma baki gaya mun ba" ya faɗa yana kallonta. Ta juya ido abinda ya sake kashe shi kafin tace
"Wane saƙo kenan?"
"Ya wuce ai tunda ya faɗa mun da kansa. Magana ce akan turo magabata na ayi maganar auranmu, na so na gaya masa har yanzu bamu samu fahimtar juna nida ke ba amma kuma na kasa".
Ta ringa kallonsa babu ƙyaftawa harya kai aya kafin ta sauke kanta jikinta nayin sanyi kamar wadda rana ta daka, Ahmad ya harɗe hannu a ƙirji yana kallo ta ya sake cewa
"Baffa da kansa ya mun magana na turo neman auranki, kar kisa ya ɗaukeni a mutumin banza idan na gaza cika umarninsa. Fatima me kike da buƙata? Ki gaya mun dan Allah me nene dalilin daya saka ba zaki bani dama na shiga rayuwarki ba?"
A maimakon tayi masa magana kawai se gani yayi hawaye ya fara mata tsere dan da hasken Nepa tar a ƙofar gidan, ya buɗe baki yana kallonta da mamaki kafin yayi magana ta juya da sauri ta shige gida tana cigaba da kukan. Yayi kasaƙe a gurin, shi ba abin ya bita ciki ba mamakin dalilin kukanta ya rufeshi. Yana tsaye Baffa ya fito be ankate ba seda ya kira sunansa.
"Malam Ahmad lafiya kuwa naga ta shiga gida tana kuka ko wani abu ne ya faru?" Baffan ya tambayeshi. To shi me zece masa yanzu? Gaskiya ze faɗa masa ko kuwa yayi shiru Baffan ya zargi wani abun yayiwa yarsa?
"Wlh Baffa babu abinda ya faru, tambayarta kawai nayi ta amince na turo iyayena shine ta fara kuka ko magana batayi bama ta wuce ciki" ya faɗa cikin rawar murya. Baffa yayi ajiyar zuciya yace
"Kayi tafiyarka kayi abinda nace maka in har da gaske kake son aurenta ka turo magabatanka"
"Nagode Baffa in sha Allahu zaka jini bada daɗewa ba" daga nan yayiwa Baffa Sallama ya wuce, farin cikin daya samu dalilin ganinta ya gushe, har wani ciwon kai yaji yana neman kamashi kukan Fatima ya tabbatar masa da gaske bata sonsa tilas ya haƙura da wannan yarinyar muddin ba rabuwa da ita ne Ajalinta ba.
A can gidansu Fatima kuwa bayan Baffa ya koma ciki tarar da ita yayi tana sharɓar kuka Umma na tsaye kanta tana faɗa kamar zata rufeta da duka.
"Ya isa Zara'u rabu da ita" Baffa ya faɗawa Umman, ta zauna tana tsaki, ji take kamar ta rufe Afeeyar da duka ko zata maidata cikin hayyacinta.
"Duk menene dalilin wannan abun? Me ya sakaki kuka daga yace ze turo magabatansa dama bakya sonsa ne ko kuwa ra'ayi kika canza?" Baffa ya tambayeta. Bata amsashi ba se kuka da takeyi ƙasa ƙasa. Umma ta jefeta da takalmi tana cewa
"Ba magana ake miki ba kinaji kinyi shiru?"
"Nace ki barta Zara'u ko?" Baffa ya faɗa a ɗan fusace. Umma tayi ƙwafa ta wuce ɗakinta. Baffa ya sake duban Afeeyah, yanda taji muryarsa ta tabbata ransa a ɓace yake ta san kuma fushi ba ɗabi'arsa bace tabbas ta kaishi bango ne dan haka yana sake maimaita mata tambayar jiki na rawa taja baya daga kusa dashi kafin tace
"Ni daman Baffa ban taɓa cewa ina sonsa ba kawai bazan iya wulaƙantashi bane amma duk wata alama da ya kamata na nuna masa nayi amma yaƙi ya haƙura".
"Momy Fatima ce na kasa gane kanta"
"Matsala kuka samu?" Ta tambayeshi tana nazartarsa. Ya karkace kamar zeyi mata kuka yace
"Ni dai babu abinda nayi mata Momy itace dai bansan ko na mata wani abu ba. Gaba ɗaya ta canza duk na kasa gane kanta".
"Ahmad kama Addu'a kuwa akan lamarin yarinyar nan?" Ta tambayeshi, yaja rantsuwa yace
"Wlh ina yi Momy, ko jiya kwana nayi ina sallah ina addu'ar neman zaɓin Allah amma wlh kamar an ƙaramun sonta a maimakon ya ragu a zuciyata"
"Kuma ba addu'ar son rai kakeyi ba? Kana cewa kana neman zaɓin Allah amma kuma ranka ba haka bane ka rigada ka zaɓarwa kanka abinda kake so?" Momy ta sake faɗa tana dubansa yace
"Momy shekara uku fa kenan, na san ba nacina ko dagiyata ce zata bani abinda nale so ba amma kuma Allah na barwa zaɓina ina ganin da inada wani haske daban bayan ita da yanzu na ganshi amma Momy ita ɗin dai ita na gani nake kuma ji a jikina itace matata".
"Toh addu'ar dai ita zamu cigaba dayi akan koma menene Allah ya warware sannan damuwar daka saka a ranka ba zata amfana maka komai ba kayi Ƙoƙari ka cireta, duk abinda Allahya saka cewar rabon bawa ne a duniya seya same shi idan kuma ba rabonka bane duk wuya haka zaka haƙura domin ba zaka sameshi ba. Sannan kuma ni ina ganin cewar harda halinka yasa yarinyar nan take maka koma menene"
Ya zabura yace
"Halina kuma Momy? Me nakeyi?" Momy tace
"Shekara uku kace da bakinka yanzu, wace irin soyayya ce haka har yanzu da za'ace ba za'ayi aure ba? Kaida bakinka kace mun mahaifinta yace maka ko tana cikin makaranta idan ka shirya aurar da ita zeyi to me kake jira har yanzu? Kana tsammanin zata cigaba da zaunawa tana ɓata lokaci dakai ne Alhalin ƙila tana da wasu masoyan da suka fika himma?"
Yayi shiru dan besan bayanin da zeyiwa Momy ta fahimta ba. Baya so ya ɓata Fatima a idonta ta hanyar sanar mata cewar itace har yanzu batayi na'am dashi ba kuma ita taƙi bashi damar ya tura ayi maganar auransu idan kuma yayi shiru Momy zata cigaba da bashi laifi na cewa shi yake ɓatawa Fatiman lokaci wannan yasa ta karkata hankalinta ga wani daya fishi himma kamar yanda tace.
"To ai Momy yanzu tana Level 4 har sun gama First semester da bari nayi tunda son zo ƙarshe kawai ta ƙarasa daganan se aje ayi magana"
"Oh so kakeyi harta gama makarantar tazo ta zauna sa'annan ka gama shiriritarka se aje ayi maganar aure ko? Lallai kuwa kana zaune nan zakaji wani ya aureta. Waima sanyar me kakeyi ne? Ina kace tun tuni ka sanar da Alhaji maganar nan me kake jira da ba zaka sake tayar masa da ita ba tunda ka nace lallai se shi zaka kaiwa maganar auranka?"
"Aa Momy ba haka bane ba, naga ai Alhaji ne Ahaƙƙu da na sanarwa da zancen aurena idan yaso shi kuma ya iya saka wakili ya shige mun gaba" ya bata amsa kai a ƙasa. Momy ta harareshi tace
"Sannu uban fitar da Ƙoƙon Asali, dama dai yanda kake da ƙulafucin uban nan shima haka yake ta taka amma na tabbata yanzu ya manta ma da kunyi wata magana data shafi zancen auranka dashi. Se kaje ka sake samunsa ai ka tuna masa, idan kuma yace Aa kaga aiseka fara sabon lissafi tunda ga tudun dafawar da duk yanda aka ciza ze tsaya maka kace baka san zance ba ba zakaje ta wurinsa ba".
"Ni Momy bana so a sakeyin irinta Yaya Sarki kina kallo dai Alhaji swda yayi ta faɗa akan ya zameshi daga maganar auransa shiyasa amma ba wani abu ba kuma nasan ai dai ko shi na gayawa dole dai Baba Alƙalin ze wakilta" ya sake faɗa Momy tace
"Ai shikenan, amma dai mafita guda ce in har da gaske kake son yarinyar nan manya su shiga maganarku, kaje ka samu ubanka ka fayyace masa komai ya tura a nema maka auranta in kuma zaka zauna nuƙu nuƙun ne kuma shikenan"
"Toh Momy zanje" daga nan suka bar maganar suka shiga wata. Bayan fitarsa ya ringa shiryawa yana warware ta yanda ze sake tunkarar Alhaji da zancen aurensa da Fatima. Amma ta yaya ma ze taso magana alhalin ita wadda za'a aura ɗin bata yarje masa ba?
Ya samu jikin katanga ya lafe ya shiga kiran layinta, yanzu abin ya sake ta'azzara har rejecting take in bata ga damar amsawa ba kuma ya dameta, So hana ganin laifi haka yake jurewa domin ya yarda ƙaddarar sa ce Son Fatima. A kira na biyu ta amsa muryarta ta shaida masa bacci takeyi dan haka yace
"Kiyi haƙuri na tasheki a bacci"
"Babu komai ina zaune ne nima ban san baccin ya kwasheni ba, ina wuni?" Ta gaidashi. Tana da kirki, tana da tarbiyya, Mahaifanta mutane ne kai tana da duk wani quality da yake nema a gurin matar auransa baya zaton idan ya barta ze damu full option abinda yake nema a gurin mace tamkar nata ya ayyana a ransa.
"Kina free yau da dare zanzo?"
"Eh" ta bashi amsa a taƙaice, shikenan ya mata sallama akan se bayan Magriba zeje haka kuwa akayi yaje yayi aski ya ɗan shiga saiti ana sallar Magriba ya sha kwalliya ya tafi gidansu. A can yayi sallar Isha a masallacinsu Baffa kafin suka ƙarasa gidan tare. A ƙofar gida Baffa ya dubeshi yace
"Malam Ahmad na bawa Mamana Saƙo kusan sati nawa amma banji amsa ba".
Da rashin fahimta ya dubi Baffan kafin cikin girmamawa yace
"Ina ganin ta sha'afa ne Baffa ko kuma nine na manta da ta gayamun amma wace magana ce?"
Baffa yayi murmushi yace
"Dama maganar zuwan magabatanka ne nace lokaci yayi daya kamata ace manya sun shiga cikin maganar nan, ni badan ka buye ta tata ba kace a barta ta gama karatun kamar yanda take so ai da tuni kuma ka huta da biyo dare kana maƙalewa jikin katanga" Baffa yayi masa barkwanci. Yayi yar dariya yana sosa Ƙeya, Baffa ya sake cewa
"To ina sake maimaita maka tunda da alama ta sha'afa kamar yanda kace, a sanar musu saboda a san abinda ake ciki"
"In sha Allahu Baffa zan sanar musu" ya faɗa kai a ƙasa, Baffa ya wuce ciki yana masa Addu'a da fatan Alkhairi. Shiya turo masa Fatima wadda ta manta da batun zuwan Ahmad ɗinma seda Baffa yace mata yana waje. Dogon Hijab ta saka, bata shafa ko hoda ba ta fito tana bulbula ƙamshin designer perfumes ɗin da yake kai mata akai akai. Ta gaishe shi ya ringa kallonta kullum ya ganta ƙara sonta yakeyi, jinta yakeyi har tsakiyar ransa shi be taɓa sanin haka So yake ba seda ya afkawa kogin ƙaunar Fatima.
"Yanzu Baffa yake cemun ya baki saƙo amma baki gaya mun ba" ya faɗa yana kallonta. Ta juya ido abinda ya sake kashe shi kafin tace
"Wane saƙo kenan?"
"Ya wuce ai tunda ya faɗa mun da kansa. Magana ce akan turo magabata na ayi maganar auranmu, na so na gaya masa har yanzu bamu samu fahimtar juna nida ke ba amma kuma na kasa".
Ta ringa kallonsa babu ƙyaftawa harya kai aya kafin ta sauke kanta jikinta nayin sanyi kamar wadda rana ta daka, Ahmad ya harɗe hannu a ƙirji yana kallo ta ya sake cewa
"Baffa da kansa ya mun magana na turo neman auranki, kar kisa ya ɗaukeni a mutumin banza idan na gaza cika umarninsa. Fatima me kike da buƙata? Ki gaya mun dan Allah me nene dalilin daya saka ba zaki bani dama na shiga rayuwarki ba?"
A maimakon tayi masa magana kawai se gani yayi hawaye ya fara mata tsere dan da hasken Nepa tar a ƙofar gidan, ya buɗe baki yana kallonta da mamaki kafin yayi magana ta juya da sauri ta shige gida tana cigaba da kukan. Yayi kasaƙe a gurin, shi ba abin ya bita ciki ba mamakin dalilin kukanta ya rufeshi. Yana tsaye Baffa ya fito be ankate ba seda ya kira sunansa.
"Malam Ahmad lafiya kuwa naga ta shiga gida tana kuka ko wani abu ne ya faru?" Baffan ya tambayeshi. To shi me zece masa yanzu? Gaskiya ze faɗa masa ko kuwa yayi shiru Baffan ya zargi wani abun yayiwa yarsa?
"Wlh Baffa babu abinda ya faru, tambayarta kawai nayi ta amince na turo iyayena shine ta fara kuka ko magana batayi bama ta wuce ciki" ya faɗa cikin rawar murya. Baffa yayi ajiyar zuciya yace
"Kayi tafiyarka kayi abinda nace maka in har da gaske kake son aurenta ka turo magabatanka"
"Nagode Baffa in sha Allahu zaka jini bada daɗewa ba" daga nan yayiwa Baffa Sallama ya wuce, farin cikin daya samu dalilin ganinta ya gushe, har wani ciwon kai yaji yana neman kamashi kukan Fatima ya tabbatar masa da gaske bata sonsa tilas ya haƙura da wannan yarinyar muddin ba rabuwa da ita ne Ajalinta ba.
A can gidansu Fatima kuwa bayan Baffa ya koma ciki tarar da ita yayi tana sharɓar kuka Umma na tsaye kanta tana faɗa kamar zata rufeta da duka.
"Ya isa Zara'u rabu da ita" Baffa ya faɗawa Umman, ta zauna tana tsaki, ji take kamar ta rufe Afeeyar da duka ko zata maidata cikin hayyacinta.
"Duk menene dalilin wannan abun? Me ya sakaki kuka daga yace ze turo magabatansa dama bakya sonsa ne ko kuwa ra'ayi kika canza?" Baffa ya tambayeta. Bata amsashi ba se kuka da takeyi ƙasa ƙasa. Umma ta jefeta da takalmi tana cewa
"Ba magana ake miki ba kinaji kinyi shiru?"
"Nace ki barta Zara'u ko?" Baffa ya faɗa a ɗan fusace. Umma tayi ƙwafa ta wuce ɗakinta. Baffa ya sake duban Afeeyah, yanda taji muryarsa ta tabbata ransa a ɓace yake ta san kuma fushi ba ɗabi'arsa bace tabbas ta kaishi bango ne dan haka yana sake maimaita mata tambayar jiki na rawa taja baya daga kusa dashi kafin tace
"Ni daman Baffa ban taɓa cewa ina sonsa ba kawai bazan iya wulaƙantashi bane amma duk wata alama da ya kamata na nuna masa nayi amma yaƙi ya haƙura".