← Book details Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 39 OF 137

Sashe 39

Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cikin dare ya koreta, ba tareda yayi tunanin ina zataje ba wane hannu zata fada kuma ya gaya mata karta kuskura taje gurin danginsa kona mahaifiyarsu. Hatta da yan unguwa da suka tausaya mata suka so bata mafaka Tijara yayi musu yace ze hada duk wanda ya shigar masa hurumin gida da hukuma haka ya koreta se tasha taje ta samu mafaka duk akan dalilin Qaddarar data fada mata wadda shine sila. A dalilin kasa sauke nauyinsu da Allah ya dora masa na ciyarwa da sauran buqatu ya tilasta mahaifiyarta fara dora mata tallan shinkafa da wake tana kaiwa Bakin Kasuwa kuma a nan ne qaddara ta hauta wani Azzalumi yayi mata wayo yayi mata fyade, shekararta goma a sannan, ya gana mata Azabar data fitar da ita daga hayyacinta qarshe ta farka ta ganta a gidansu Kwance ga Mahaifiyarta na Kuka Mahaifinta kuma na Sababi kamar zeyi Aman wuta.

Yana ganin kuma ta farka be duba komai ba yace ta tashi ta fitar masa daga gida, a fadar sa daman an sha gaya masa ana ganinta a shagunan Maza, ko a sannan din be yarda Fyade akayi mata ba, a yanda wanda suka tsinto ta suka gaya masa wai ciki ta zubar, wanda ya bata maganin ya gudu se ita suka tsinto cikin Jini a wani kango. Babu dogon tunani babu komai Mahaifinta ya yanke wannan danyan hukunci na korarta a cikin dare. Beyi tsinkayen cewa a sannan ko Al'ada bata fara ba ballantana ace ta dauki ciki, yayi mata korar kare cikin rashin Imani, Mahaifiyarta da qannenta naji suna gani tabar gidan shekaru goma kenan kuma kamar yanda ya fada bata sake koda taka qafarta a qasar Kano ba da Asuba tabi wata mata Mai siyar da Abinci a tasha daman ta santa idan ta kawo tallah tana gaisheta matar tasan abinda ya faru da Zubaidan dan haka data ganta cikin daren bata tambayi ba'asi ba kawai ta dauketa ta kaita dan dakinta na langa langa dake cikin Tashar. A nan ta gyarata tayi mata wanka ta kuma bata Abinci washe gari da Asuba suka hau mota suka bar Kano dan dama taga matar ta hada kayanta tsaf da alama zatayi Balaguro, bata tsinci kanta a ko ina ba se a Kwantagora, da fari Abinci suke siyarwa da giya a nan gidan daga matar ta ingizata zuwa ga wannan rayuwar da take nadama da dana sanin shigarta.

Takanyi kuka tace me yasa bata tsaya ba Babanta ya halakata tunda yace idan bata fita ba seya kasheta? Data sani ta zauna ya kashe ta ta mutu tun sannan qila da tana Aljanna abinta da wannan qazamar rayuwar data jefa kanta a ciki.

Audu na qofar dakin yana jiyo kukan ta daga ciki, kasa daurewa yayi ya koma ya tsaya akanta yana ganin yanda take kuka har jikinta na jijjiga.
"Dan girman Allah kiyi shiru, idanhar maganar so ko aure danayi miki ce ta sakaki wannan kukan na janye na haqura ke dena Kukan haka" ya fada cikin sigar lallashi. Bata bari ba, haka ya kai tsugunne ya ringa lallashinta da kalamai masu kwantar da hankali. Shida kansa yayi mamakin inda ya iyasu, be haqura ba har seda ta dena kukan tana ajiyar rai da jan majina.

"Kiyi tunani akan maganata" ya sake fada mata ba tareda ya sare ba.
"Ta yaya mutum kamarka me kamala, na fahimci ba halinka daya da Abokinka ba ya za'ayi kace zaka auri Karuwa kamata wadda bata da mutunchi ballantana daraja?" Ta fada hawaye na sake sakko mata.

Audu ya zauna da kyau ganin ta sakko tana so suyi magana yace
"Nima ban sani ba, amma na tabbatar qila Allah ne yaso dana zama silar fitar dake daga wannan rayuwar shiyasa ya doramun sonki. Sannan maganar Mutunchi ko Daraja, ban sanki ba bansan daga inda kika fito ba amma na tabbatar koma daga ina kike kin kasance Mace me Mutunchi da Daraja a baya, qaddara ce ta kawoki nan domin mata kadan ne suk shiga Bariki da son ransu, mafi aka sari Qaddara ce take afka musu wadda mutane suke kasa yi musu uzuri harsu ingizasu ga zuwa abinda yafi wanda ya same su a baya muni.

"Duk abinda dan Adam yake aikatawa muddin be mutu ba yana da damar shiriya ya nemi yafiyar ubangijinsa, kema lokaci be qure miki ba. Ki bar wannan rayuwar da babu komai cikinta se qasqanci, ki koma gida wlh da gaske nakeyi zan aureki bada wasa nake sonki ba".

"Mahaifina ya koreni, yace karna sake komawa gidansa idan har naje be yafe mun ba. Ina so naje, ina kewar mahaifiyata amma bana son na sake shiga wani fushin nasa akan wanda nake ciki" ta fada cikin sauti me ban tausayi.

"Ke din yar wane gari ce? Kuma meya fito dake daga gida?" Audu ya tambayeta. Bata boye masa komai ba na daga labarin rayuwarta ta gaya masa gaskiya, yaji tausayinta kwarai dagaske ya kuma ga baiken Mahaifinta. Irin wannan qaddarar ta fadawa mata da yawa, idan da ace iyaye suna taya Yayansu karban qaddararsu a yanda tazo musu da an samu raguwar masu fantsama Bariki. Da yawan iyaye Sukan manta cewar Abin kunyar da suke tunqahon yayan sun jawo musu har yasa suka kada su duniya kadan ne akan rayuwar da suke jefasu suyi, ga dakon zunubi domin duk abinda suka aikata na barna tare za'a raba musu Sakamakon da iyayen saboda sune suka turasu zuwa ga barnar. A tunanisa da a ringa zunden mutum ana cewa yarsa ta zama Karuwa gara a kira shi uban wadda aka tabayiwa Fyade ko tayi cikin shege ya barta a gabansa ta shiryu har ya aurar da ita wannan haqurin da mutum yayi se ubangiji ya dubeshi ya shirya masa zuri'a amma korar yara akan wata qaddara mara kyau ba daidai bane, su kansu Iyayen sunyi bankwana da kwanciyar hankali daga ranar da suka kori Yayan nasu basa sake samun nutsuwa.

Audu basuje Zariya da niyar kwana ba amma Alamun cin galaba akan Zubaida daya gani ya sakashi kwana a garin. Yayi mata alqawarin ze nemo mata mahaifinta muddin yana raye ze hada su kuma koya mutu ze maida ita gida gurin ragowar yan uwanta. Ya roqeta akan ta shirya su tafi Kano tare, ze bata mafaka har zuwa sanda zata daidaita da iyayenta amma taqi, tace dai yaje ba zata dawo idan har mahaifinta ya mata izini.

Haka washe gari suka dawo Kano gaba daya Audu bashi da kuzari, Bashir nata yi masa shaqiyanci da cewar shima ya zama dan hannu dan tunda suka rabu basu hadu ba seda safe da zasu wuce Kano dan haka besan duk abinda ya faru tsakaninsa da Zubaida ba.

A gida ya tarar da Binta cikin yanayi na neman tashin hankali dan yana shiga tambayar data fara jefa masa itace
"Daga gidan uban wa kake?"
A lokacin yanayin sanyin jiki da kuma martabar mahaifinta da ya wuce ya zageshi ya saka ya qi tanka maka amma kaitsaye zuciyarsa ta ringa raya masa ya gaya mata daga gidan ubanta yake ko da abinda zatayi akai. Bata haqura ba ta bishi har daki tana ihu da hargagi tareda fadar maganganu. Baturiya matar Ali ce ta gaya mata Audun sun tafi wani gari gurin Mata tareda Bashir itama tsintar zancen tayi a gurin Mijinta yana gayawa wani Abokinsa daya je gidan shine ta wanke qafa ta tafi gidan Binta ta gaya mata ranar bata iya runtsawa ba a tsaye ta kwana tana jiran taga ta inda ze bullo amma be dawo na se yanzun.

Duk kalar rashin mutunchin data ringa zazzagawa be tanka mata ba ya shige daki ya kullo qofa ya shiga wanka. A ranar yake so yaje ya fara binciken iyayen Zubaida data gaya masa ita din haifaffiyar unguwar Alkantara ce, sanda ya fito Binta ta sauka daga saman harya fita kuma beji motsinta ba ya dauki mota ya bi kwatancen da Zubaida tayi masa besha wahala ba saboda sunan Mahaifinta data gaya masa Malam Hassan Na'ibi yana fada aka kaishi har qofar gidan lokacin qarfe biyar na yamma rana tayi sanyi a qofar gidan ya tarar da Malam Hassan din da wasu dattijai guda biyu kan tabarma suna hira.

Ya ringa kallon mutumin, kamanninsa daya da Zubaidar, sedai yanayinsa ya nuna kamar bashi da lafiya saboda a kishingide ma yake be iya zama sosai. Audu ya qarasa kan tabarmar ya zauna suka gaisa duk suna masa kallon rashin sani.
"Gurinka nazo Baba, idan babu damuwa ina so zamuyi magana ne" ya fada yana kallon Malam Hassan ganin haka ya saka ragowar suka gane baqonsa ne.

*MAMAN MARYAM ONLINE BUSSINESS*

*Ina kuke Mata Yan kwalisa , Ina nufin isassun Mata ,Wai shin Kuna da labarin shahararren company nan namu na GHT wato good healthtreatments*
*Wanda yazo muku da fitattu Kuma* *ingantatattun suppliment ,na dukkan matsalolin ku*❓

*Ina maisan tayi kyau,irin na isassun Mata ya fitar Miki da shef dinki tayi Miki gyara in and out ,nemi royal jelly dinmu na company GHT*
*Wanda aka yishi da xuma ,kundai San amfanin Zuma basai na fada miku ba , hajiya ta kixo ki Yi gyara domin ki kerewa sa,a kije taro ko baki da ko sisi kiji Ana rangada Miki hajiya , saboda yanda Zaki Kara kwarjini ,kina walwali acikin mutane , magungunan ght anti agen ne suna maida tsohuwa* *yarinya ,yarinya Kuma ta koma jaririya*

*Muna da magunguna iri iri*

*NA GYARAN JIKI*
*NA GOGE NANKARWA*
*NA RAGE QIBA*
*NA CIRE TUMBI*
*NA QARIN HIPS*
*NA GIRMAN BREAST*
*NA QARA TSAHON GASHI*

*NA QARIN NI'IMA WANDA ZAI SAUKAR MIKI DA NI'IMA YA QARA MIKI DADI DA ZAQI A GURIN OGA*

*Muna da hadin bita zai zai ,indai kishiyar ki tana Shan magungunan GHT, tohh lallai sunan ki sorry domin kuwa tazarar dake tsakanin ku kamar tazarar sama ne da kasa*

*Muna da Wanda zai matseki ciki da waje Andai na yayin dinki uwargida*,

*Sannan company mu na GHTBai tsaya anan ba*
*Ya kawo muku maganin dukkan matsalolin ku*

*INA MASU HAWAN JINI?*
*INA MASU CIWON ZUCIYA?*
*INA MASU CIWON QODA?*
*INA MASU CIWON HANTA?*
*INA MASU SICKLER?*
*INA MASU HIV?*
*INA MASU CANCER?*
*INA MASU NEMAN HAIHUWA?*
Chapter 39 · 0% Book details