Sashe 76
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ke Munirah meye haka? Baki da hankaline kike daga murya baki san bamu kadai bane a gidan nan?" Binta ta fada a rikice tana qoqarin toshe mata baki Muniran ta fizge tana cigaba da cewa
"Ki barni Yaya Binta abin kukane ya sameni dole nayi, daman Yaya Ummu seda ta fada, tace akwai ranar da zamuyu kuka muyi Nadama, seda tace tun muna da sauran lokaci mu kwance qullin da muka daura a lokacin ban dauki maganarta da muhimmaci ba, haka kawai muna zaman zamanmu muka jazawa kanmu masifa ta hanyar shiga haqqin baiwar Allah da bataji ba bata gani ba muka bata mata suna kuma mukayi silar mutuwar Auranta gashi yanzu ta mututu ta bar mu a duniyarda nauyin haqqinta a kanmu nidai Allah ya isa tsakanina daku kun cuceni wlh" ta sake fada muryarta a sama tana rusa kuka.
"Alhamdulillahi! Dadina da gobe saurin zuwa, Allah nagode maka daka matsi bakin Azzaluman bayinka suka tonawa kansu Asuri, kaiconku wlh, kaicon Zuciya me cike da Mugunta da Zalunci irin taku. Yanzu ai ga duniyar nan gaba daya bama gidan Audu ba ta tafi ta bar muku se ku shinfida tabarma ku cigaba da zama kuna kasa abinda kukaga dama a cikin duniyar, amma ku sani wlh cutar da kukayiwa Bara'atu bazata barku ku zauna lafiya ba, yanda kuka saka rayuwarta cikin qunci da takura harta koma ga mahaliccinta da yardar ubangiji haka zaku qare taku" Bilki ta fada idanunta na tsiyayar da hawaye, ta waiwaya ta kalli Audu daya runtse ido kamar yayi bacci a inda yake zaunen tace
"Baka da banbanci kaidasu, yanda zasu qare rayuwarsu suna girbar sharrin da suka shuka kaima haka zaka qare taka kana Nadamar zamanka da Bara'atu"
"Ke Bilki menene haka? Da wanne kike so yaji dan Allah?" Aminu ya katseta. Bata kulashi ba taci gaba da kukanta. A cikin daki kuwa Munirah na gamsheqar kuka Binta na tsaye akanta ta harde hannye gaba daya kanta ya qulle ta rasa abin da zatayi a lokacin, ji take kamar ta rufeta da duka shegiyar yarinya ta kwance mata zani a Kasuwa yanzu da wace kalma take so ta gyara kwabar da tayi mata?
Tana jiyo sanda su Aminu suke fadawa Audu zasu wuce saboda kar suyi dare a hanya.
"Ka daure ka shiga daki ka kwanta, rayuwar kenan daman farkonta da qarshenta dan taqin kadan ita dai Bara'atu tata ta qare kuma In sha Allahu munayi mata kyakykyawan zaton tana Babban masauki addu'a kadai zamu cigaba da bibiyarta da ita kafin tamu tafiyar ta riskemu Allah yasa kuma abinda ya faru a baya ya zame mana darasi a rayuwarmu gaba daya" Aminu ya sake fada masa daga nan suka fara haramar wucewa Bechi.
Cikin yanayi me ban tausayi Audun ya miqe, dakyar ya iya ce musu Allah ya tsarw hanya ya daddafa ya haye samansa a falo yayi zango ya kwanta rigingine a qasa wani zafi da radadi yake ji daga can cikin zuciyarsa, numfashinsa ya ringa fita da sauri da sauri tamkar wanda yayi gudu a, a sannu ya baiwa Idanunsa damar fitarda abinda suke muradi, hawaye ya gangaro ta gefen idanunsa zuwa cikin kunnuwansa, tamkar me tsoron wani ya jishi ya saki kuka kamar mace, kuka me tafe da abubuwa da yawa a cikinsa. Cikin muryar da bata fita yake cewa
"Dana san mutuwa zakiyi Bara'atu da ban rabu dake ba, inama ina da damar maido da baya, dana canza zaman da mukayi zuwa mafarkinki, dana san rayuwarki ba zatayi tsaho ba da...da...." Ya kakare yama rasa abinda ze fada se kawai yaci gaba da kukansa a hankali kewar Bara'atun me nauyi tana dirar masa. Kalamanta na sallamar da tayi masa suka ringa dawo masa kamar sannan take maganar, tace ta yafe masa amma bashida tabbacin Allah baze kamashi da laifin cutar da ita ba wai meya shiga kansa shi? Meyasa ya kasa tantance gaskiya da qarya a zamansa da Bara'atu? Me yasa ya gagara yi mata uzuri ya ringa Muzguna mata yana tozartata? Yanzu gashi ta tafi ta bar masa duniyar dai, tayi masa nisan da baze taba taddota ba.
Seda yayi kuka me isarsa kafin ya tashi dalilin kiran sallar Azahar da ake tayi yana layi kamar wanda ya shawu ya dauro Alwala, baze iya sauka ba dan haka a nan yayi sallarsa addu'arsa gaba daya ta nemarwa Bara'atu Rahmar ubangiji ce, yana nan zaune yayi zuru zuru kamar wanda ya kwana zawo, motsin hawowa saman ya jiyo, ya waiwaya ya kalli qofa daidai nan Binta ta shigo da Try a hannunta ta doro kulolin abinci jikinta sanye da Zurmemen Hijabi har qasa fuskarta tayi jaa ta kumbura kamar wadda tasha kuka ta qoshi.
A gabansa ta ajiye Try din ta zauna se ji yayi ta fashe da kuka tana hailala da salati, yayi zukudi yana kallonta kawai.
"Mun shiga uku mun lalace Ashe Bara'atu mutuwa zatayi daman? Me yasa yarinyar nan bata haqura munyi zaman lafiya anyi rabuwar arziqi ba?" Yeeee ta sake rushewa da wani kukan.
"Binta" ya kirata cikin kaushin murya, tayi dif daga kukan munafurcin da takeyi ta kalleshi, cikin sautin daya fi na farko ya sake ce mata
"Zan sake tambayarki menene gaskiyar abinda ya faru ranar sunan Zakariyyah?"
"Wace gaskiya kuma wai kake buqatar sani bayan abinda nida yan uwana muka shaida maka tun a waccen ranar? Allah ya jiqan Bara'atu kawai ni daman tun tuni ai nace na yafe mata idanma wannan kake tunani" ta bashi amsa ba tareda ta kalli idonsa ba babu tsammani kuwa taji saukar yatsunsa a kuncinta irin marin nan na bazata seda ta wantsala gefe tana zare ido kafin ta taqarqare ta fasa qara tana kiran
"Ka mareni"
"Na marekin, kuma dukan tsiya zanyi miki yanzu muddin baki bani amsar abinda na tambayeki ba sa'innan na koraki gidanku" ya fada yana miqewa tsaye PPP ll ya razana Bintar bata taba ganin ya birkice haka ba, Bay's play llp ta fara ja ganin yana neme neme da alama abinda ze doketa dashi din yake nema hakan yasa tace
"Zan fada maka wlh, nidai na shiga bandaki ina fitowa kawai na tarar da ita ta zauna akan Jaririn"
"Har yanzu kina da bakin yimun qarya ko?" Ya fada yana nufota da wayar Radion daya zare, ta yunqura zata gudu Hijabin jikinta ya tadeta ji kake timm ta fadi a qasa be ko bata damar biqin radadin faduwar ba ya shiga zabga mata Bulaliya ta ko ina a jikinta. Dukanta yake kamar ya samu qato dan uwansa yana fadin "ba zaki fadamun gaskiya bako?"
Dadai ta tabbatar da gaskiyarta ce zata kwaceta a hannunsa dole ta fada,
"Wlh sune, basu fadamun daman ya mutu tuntuni ba se bayan da aka gama mana shari'a wlh ba laifi na bane kayi haquri ka kyaleni".
Be barta ba seda hannayensa suka gaji zuwa sannan ko motsin kirki bata iyayi ya mata lilis fatar jikinta duk ta fashe nan ya watsar da bulalar ya shige daki ya barta tana jan numfashin wahala dan kukan ma ta kasa cigaba da yinsa. Wanka yayi ya fito ya tsallajeta yayi waje abinsa, Munira na bakin qofar, tunda ta jiyo ihun yar uwar tata ta taho sedai tsoron karta shiga ya hada da ita yasa taci burki a gurin.
"Kar na dawo na tarar daku cikin gidana daga ke har itan" ya fada mata. Ta sauke ajiyar zuciya da be taba lafiyarta ba, seda ya sauka daga qasan kafin ta shiga, yanda taga Bintan ta tsorata ta kamata Binta ta fashe da kuka saboda Azaba ta ko ina jikinta radadi yakeyi mata.
Hudu ta gota sanda Munira ta hada musu yan abinda zasu buqata Binta ta coccogala suka fita daga gidan Audu saboda tsoron abinda ze iya biyo bayan zamansu Alhalin yace su tafi. Gidan Turai suka nufa dan babu halin Tafiya Kaduna a wannan lokacin, suka hadu suka ringa jimamin al'amarin.
"An auna arziqi dabe furta ya sake ki ba ai, lokaci kawai zaki bashi ya danyi fushinsa ya sakko komai ze daidaita" Turai ta fada.
Binta dake kwance magashiyyan Zazzabi na nuqurqusarta a haka ma wai taje Chemis an bata maganin rage radadi dana zazzabin shine taji dama dama.
"Yanzu ta mutuma amma tsinanniyar matar nan ba zata barni na zauna lafiya da Mijina ba Allah ya isa tsakanina da Bara'atu" ta fada tana sakin kuka. Munirah tace
"Yanzu ashe ba zaki saduda ba Yaya Binta? Wannan abun be isa ya zame miki ishara ba?"
"Zanci uwarki idan kika sake saka mun baki a magana" ta fadawa Muniran daga nan tayi shiru tana jinsu da Turai suna maganganu akan matakin daya kamata su dauka, ita dai Allah ya gani tayi nadama kuma tana fatan itama Bintan ta ganr gaskiya tun lokaci be qure mata ba sannan da sun je gida dole ta warwarewa Iyayensu komai daya faru saboda ayiwa tufkar hanci, muddin Binta bata rabu da wannan matar da alamu suka nuna ita take sake dorata a hanyar banza ba ba zata taba komawa ga Allah ba. Washr gari suka tattara suka wuce Kaduna, Binta bata tsammaci abinda ta gani bayan da Munirah ta fasa kwai ba, gigicewar da Salima da Sakina sukayi ba kadan bace Ummu ko fadi take
"Kun gani ko? Kunga abinda nake jiye muku ko? Yanzu wa gari ya waya? Gashi nan ta mutu ta bar muku duniyar kuji da dakon haqqinta".
Alhaji Zakariyya wanda yake fama da ciwon bugawar zuciya kusan shekara hudu kenan da ciwon ya ta'azzara masa abu kadan yake tayar masa dashi wannan tashin hankali daya riskeshi na abinda Yaran nasa suka aikata ya sake motsa masa ciwon sosai, ita kanta Maman Seda Hawan jininta ya tashi, Allah ya sani daga ita har Mijinta babu me muguwar zuciya da baqin rai irin wanda Yaransu suka gwada. Rashin lafiyar Alhajin tasa basu bi takan Binta ba qoqarin yanda zasu cetoshi kawai sukeyi a sannan.
"Ki barni Yaya Binta abin kukane ya sameni dole nayi, daman Yaya Ummu seda ta fada, tace akwai ranar da zamuyu kuka muyi Nadama, seda tace tun muna da sauran lokaci mu kwance qullin da muka daura a lokacin ban dauki maganarta da muhimmaci ba, haka kawai muna zaman zamanmu muka jazawa kanmu masifa ta hanyar shiga haqqin baiwar Allah da bataji ba bata gani ba muka bata mata suna kuma mukayi silar mutuwar Auranta gashi yanzu ta mututu ta bar mu a duniyarda nauyin haqqinta a kanmu nidai Allah ya isa tsakanina daku kun cuceni wlh" ta sake fada muryarta a sama tana rusa kuka.
"Alhamdulillahi! Dadina da gobe saurin zuwa, Allah nagode maka daka matsi bakin Azzaluman bayinka suka tonawa kansu Asuri, kaiconku wlh, kaicon Zuciya me cike da Mugunta da Zalunci irin taku. Yanzu ai ga duniyar nan gaba daya bama gidan Audu ba ta tafi ta bar muku se ku shinfida tabarma ku cigaba da zama kuna kasa abinda kukaga dama a cikin duniyar, amma ku sani wlh cutar da kukayiwa Bara'atu bazata barku ku zauna lafiya ba, yanda kuka saka rayuwarta cikin qunci da takura harta koma ga mahaliccinta da yardar ubangiji haka zaku qare taku" Bilki ta fada idanunta na tsiyayar da hawaye, ta waiwaya ta kalli Audu daya runtse ido kamar yayi bacci a inda yake zaunen tace
"Baka da banbanci kaidasu, yanda zasu qare rayuwarsu suna girbar sharrin da suka shuka kaima haka zaka qare taka kana Nadamar zamanka da Bara'atu"
"Ke Bilki menene haka? Da wanne kike so yaji dan Allah?" Aminu ya katseta. Bata kulashi ba taci gaba da kukanta. A cikin daki kuwa Munirah na gamsheqar kuka Binta na tsaye akanta ta harde hannye gaba daya kanta ya qulle ta rasa abin da zatayi a lokacin, ji take kamar ta rufeta da duka shegiyar yarinya ta kwance mata zani a Kasuwa yanzu da wace kalma take so ta gyara kwabar da tayi mata?
Tana jiyo sanda su Aminu suke fadawa Audu zasu wuce saboda kar suyi dare a hanya.
"Ka daure ka shiga daki ka kwanta, rayuwar kenan daman farkonta da qarshenta dan taqin kadan ita dai Bara'atu tata ta qare kuma In sha Allahu munayi mata kyakykyawan zaton tana Babban masauki addu'a kadai zamu cigaba da bibiyarta da ita kafin tamu tafiyar ta riskemu Allah yasa kuma abinda ya faru a baya ya zame mana darasi a rayuwarmu gaba daya" Aminu ya sake fada masa daga nan suka fara haramar wucewa Bechi.
Cikin yanayi me ban tausayi Audun ya miqe, dakyar ya iya ce musu Allah ya tsarw hanya ya daddafa ya haye samansa a falo yayi zango ya kwanta rigingine a qasa wani zafi da radadi yake ji daga can cikin zuciyarsa, numfashinsa ya ringa fita da sauri da sauri tamkar wanda yayi gudu a, a sannu ya baiwa Idanunsa damar fitarda abinda suke muradi, hawaye ya gangaro ta gefen idanunsa zuwa cikin kunnuwansa, tamkar me tsoron wani ya jishi ya saki kuka kamar mace, kuka me tafe da abubuwa da yawa a cikinsa. Cikin muryar da bata fita yake cewa
"Dana san mutuwa zakiyi Bara'atu da ban rabu dake ba, inama ina da damar maido da baya, dana canza zaman da mukayi zuwa mafarkinki, dana san rayuwarki ba zatayi tsaho ba da...da...." Ya kakare yama rasa abinda ze fada se kawai yaci gaba da kukansa a hankali kewar Bara'atun me nauyi tana dirar masa. Kalamanta na sallamar da tayi masa suka ringa dawo masa kamar sannan take maganar, tace ta yafe masa amma bashida tabbacin Allah baze kamashi da laifin cutar da ita ba wai meya shiga kansa shi? Meyasa ya kasa tantance gaskiya da qarya a zamansa da Bara'atu? Me yasa ya gagara yi mata uzuri ya ringa Muzguna mata yana tozartata? Yanzu gashi ta tafi ta bar masa duniyar dai, tayi masa nisan da baze taba taddota ba.
Seda yayi kuka me isarsa kafin ya tashi dalilin kiran sallar Azahar da ake tayi yana layi kamar wanda ya shawu ya dauro Alwala, baze iya sauka ba dan haka a nan yayi sallarsa addu'arsa gaba daya ta nemarwa Bara'atu Rahmar ubangiji ce, yana nan zaune yayi zuru zuru kamar wanda ya kwana zawo, motsin hawowa saman ya jiyo, ya waiwaya ya kalli qofa daidai nan Binta ta shigo da Try a hannunta ta doro kulolin abinci jikinta sanye da Zurmemen Hijabi har qasa fuskarta tayi jaa ta kumbura kamar wadda tasha kuka ta qoshi.
A gabansa ta ajiye Try din ta zauna se ji yayi ta fashe da kuka tana hailala da salati, yayi zukudi yana kallonta kawai.
"Mun shiga uku mun lalace Ashe Bara'atu mutuwa zatayi daman? Me yasa yarinyar nan bata haqura munyi zaman lafiya anyi rabuwar arziqi ba?" Yeeee ta sake rushewa da wani kukan.
"Binta" ya kirata cikin kaushin murya, tayi dif daga kukan munafurcin da takeyi ta kalleshi, cikin sautin daya fi na farko ya sake ce mata
"Zan sake tambayarki menene gaskiyar abinda ya faru ranar sunan Zakariyyah?"
"Wace gaskiya kuma wai kake buqatar sani bayan abinda nida yan uwana muka shaida maka tun a waccen ranar? Allah ya jiqan Bara'atu kawai ni daman tun tuni ai nace na yafe mata idanma wannan kake tunani" ta bashi amsa ba tareda ta kalli idonsa ba babu tsammani kuwa taji saukar yatsunsa a kuncinta irin marin nan na bazata seda ta wantsala gefe tana zare ido kafin ta taqarqare ta fasa qara tana kiran
"Ka mareni"
"Na marekin, kuma dukan tsiya zanyi miki yanzu muddin baki bani amsar abinda na tambayeki ba sa'innan na koraki gidanku" ya fada yana miqewa tsaye PPP ll ya razana Bintar bata taba ganin ya birkice haka ba, Bay's play llp ta fara ja ganin yana neme neme da alama abinda ze doketa dashi din yake nema hakan yasa tace
"Zan fada maka wlh, nidai na shiga bandaki ina fitowa kawai na tarar da ita ta zauna akan Jaririn"
"Har yanzu kina da bakin yimun qarya ko?" Ya fada yana nufota da wayar Radion daya zare, ta yunqura zata gudu Hijabin jikinta ya tadeta ji kake timm ta fadi a qasa be ko bata damar biqin radadin faduwar ba ya shiga zabga mata Bulaliya ta ko ina a jikinta. Dukanta yake kamar ya samu qato dan uwansa yana fadin "ba zaki fadamun gaskiya bako?"
Dadai ta tabbatar da gaskiyarta ce zata kwaceta a hannunsa dole ta fada,
"Wlh sune, basu fadamun daman ya mutu tuntuni ba se bayan da aka gama mana shari'a wlh ba laifi na bane kayi haquri ka kyaleni".
Be barta ba seda hannayensa suka gaji zuwa sannan ko motsin kirki bata iyayi ya mata lilis fatar jikinta duk ta fashe nan ya watsar da bulalar ya shige daki ya barta tana jan numfashin wahala dan kukan ma ta kasa cigaba da yinsa. Wanka yayi ya fito ya tsallajeta yayi waje abinsa, Munira na bakin qofar, tunda ta jiyo ihun yar uwar tata ta taho sedai tsoron karta shiga ya hada da ita yasa taci burki a gurin.
"Kar na dawo na tarar daku cikin gidana daga ke har itan" ya fada mata. Ta sauke ajiyar zuciya da be taba lafiyarta ba, seda ya sauka daga qasan kafin ta shiga, yanda taga Bintan ta tsorata ta kamata Binta ta fashe da kuka saboda Azaba ta ko ina jikinta radadi yakeyi mata.
Hudu ta gota sanda Munira ta hada musu yan abinda zasu buqata Binta ta coccogala suka fita daga gidan Audu saboda tsoron abinda ze iya biyo bayan zamansu Alhalin yace su tafi. Gidan Turai suka nufa dan babu halin Tafiya Kaduna a wannan lokacin, suka hadu suka ringa jimamin al'amarin.
"An auna arziqi dabe furta ya sake ki ba ai, lokaci kawai zaki bashi ya danyi fushinsa ya sakko komai ze daidaita" Turai ta fada.
Binta dake kwance magashiyyan Zazzabi na nuqurqusarta a haka ma wai taje Chemis an bata maganin rage radadi dana zazzabin shine taji dama dama.
"Yanzu ta mutuma amma tsinanniyar matar nan ba zata barni na zauna lafiya da Mijina ba Allah ya isa tsakanina da Bara'atu" ta fada tana sakin kuka. Munirah tace
"Yanzu ashe ba zaki saduda ba Yaya Binta? Wannan abun be isa ya zame miki ishara ba?"
"Zanci uwarki idan kika sake saka mun baki a magana" ta fadawa Muniran daga nan tayi shiru tana jinsu da Turai suna maganganu akan matakin daya kamata su dauka, ita dai Allah ya gani tayi nadama kuma tana fatan itama Bintan ta ganr gaskiya tun lokaci be qure mata ba sannan da sun je gida dole ta warwarewa Iyayensu komai daya faru saboda ayiwa tufkar hanci, muddin Binta bata rabu da wannan matar da alamu suka nuna ita take sake dorata a hanyar banza ba ba zata taba komawa ga Allah ba. Washr gari suka tattara suka wuce Kaduna, Binta bata tsammaci abinda ta gani bayan da Munirah ta fasa kwai ba, gigicewar da Salima da Sakina sukayi ba kadan bace Ummu ko fadi take
"Kun gani ko? Kunga abinda nake jiye muku ko? Yanzu wa gari ya waya? Gashi nan ta mutu ta bar muku duniyar kuji da dakon haqqinta".
Alhaji Zakariyya wanda yake fama da ciwon bugawar zuciya kusan shekara hudu kenan da ciwon ya ta'azzara masa abu kadan yake tayar masa dashi wannan tashin hankali daya riskeshi na abinda Yaran nasa suka aikata ya sake motsa masa ciwon sosai, ita kanta Maman Seda Hawan jininta ya tashi, Allah ya sani daga ita har Mijinta babu me muguwar zuciya da baqin rai irin wanda Yaransu suka gwada. Rashin lafiyar Alhajin tasa basu bi takan Binta ba qoqarin yanda zasu cetoshi kawai sukeyi a sannan.