← Book details Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 63 OF 137

Sashe 63

Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Se haquri ki kuma cigaba da lallabawa daman ai ba kullum ake kwana a gado ba dole wata rana a samu yanda ake so wata rana kuma aka sin haka sannan ba yanzu muke dubawa ba gaba zamu gina lokacin Jin dadib ai be ma zoba tukunna qawata kedai Allah yayi mana tsahon rai musha shagali" Inji Turai. Binta ta murmusa tace

"Ai ni dole ma nayi tsahon rai dan munyi Gadonsa"

"Ke karkiyiwa Allah gatsali wlh yanzun kijiki a rami" Turai ta fada tana zare ido, Binta ta rufe baki tace

"Uffararan Allah na tuba ba haka zance ba, dangin mu dai sunyi Gadon tsahon rai kinga nima zanyi" ta sake sakin wani shirmen Turai ta miqe tana cewa

"Bari kiga nayi nan iskancina be kai shiga hurumin Allah ba, to mutuwa dai ba ruwanta da gadon tsayin rai ko gajartarsa in lokaci yayi dole a tafi" da haka hirar ta watse saboda Binta tace kan me kuma ana hirar arziqi zata sako musu zacen mutuwa.

Bayan ta yada wanka ta cewa Audu zataje Bechi ta kwana biyu, wannan yasa ya sassauto daga daure dauren fuskar da yake fama dashi tun rabuwarsa da Zubaida. Ya shirya mata tafiyar Ado sabon Direban daya dauka yake jigila dashi ne ya kaita Bechin niqi niqi da kayan tsarabar data loda dan Hajji Kam taje tayo tsince tsincen su Zam Zam, Dabino Bagaruwa su kallo kallo na yara da sauran tarkacen tsaraba ta tafi.

Kadaran kadahan suka karbeta musamman da basu san da zuwanta ba dan haka babu wani tanadi da akayi mata ta bude dakinta ta shiga a ranta tana tsine musu babu wanda ya bita ko suce zasu tayata kimtsa guri sun dai karbi Naziru yana can hannun Sauda Amaryar Aminu. Ta gama kakkabe dakin ta kimtsa abinda zata kimtsa kafin ta bude jakar tsaraba ta shiga kasawa gida gida.

Yara ne sukayita shelar zuwanta garin, Aisha ta biya gidan Bilki akan tazo suje yiwa matar Yayan nasu Barka da zuwa amma tace babu inda zataje. Haka ta tafi ita kadai ta tarar da Yaya Mairo da Yaya Amina da matan Yayyensu duk sunzo Goggo Fadi ta aika an gayo musu. Kamar yanda Turai ta fada kuwa duk wadda ta shigo fuska a murtuke dan ba a son ransu suka zo din ba dan dai bazasu tsallake kiran Sirikarsu bane amma data miqa musu qullin tsaraba se kaga sun hau washe baki suna godiya daga nan se a shantake a fara hira kuma wannan tasa Aisha ta tarar da dakin cike da Mata suka gaisa ta karbi yaron da daman shine maqasudin zuwanta bawai ganin Bintan ba tana tambayarta Yayansa tace mata Yana Kaduna tunda suka zo suna suka tafi dashi. Bata jima ba tayi musu sallama tace se gobe zata dawo.

Bayan Isha Jamila Uwargidan Hashimu ta sake dawowa da Langa tuwo da miya data sakowa Binta abincin dare. Tana daki bayan ta lallaba Naziru yayi bacci, qullin uban Nama ne a gabanta da damammiyar fura take ci Baballiya ne ya kawo mata bada jimawa ba tayi mamakin ganinsa a Bechi wato ya zo Kano amma koya leqa can gidansu da tayi masa tsiya yace mata ai yaje Kanon amma a Kamfani suka hadu da Yaya Audu dake ba jimawa zeyi ba anyi posting nasa can qasar Kudu yazo yiwa yan gida sallama ne shiyasa be shiga can gidan sun gaisa ba ya ajiye mata saqon ya wuce ta bishi da kallo tana mamakin girman da yayi, idan ba'ayi wasa ba zefi Audu tsaho da qirar qarfi yanzun.

"Sangangan kenan sudai sunyo gadon girmaz wai yanzu haka nawa Yayan zasu tashi kenan kamar dakarun yaqi? Allah yasa dai su kwaso hankalin wancan me baqar zuciyar Wan uban nasu dan ta nan ya banbanta da sauran" ita kadai take sambatu tana danna lomar Nama abinta Jamilan tayi sallama. Tsaki taja qasa qasa kafin ta amsa, babu damar ta boye abinda take ci dan ta rigada ta shigo dan haka ta hade fuska dan ba zata sammata ba.

"Aa, Hajiya irin wannan rabasha haka kice gashin Haladu aka kawo miki" Jamila ta fada tana kallon ledar kamar ta dumbula hannu yawunta ya tsinke dan qamshin naman ua cika dakin duka. Yaqe kawai Binta tayi ba tareda tace komai ba a ranta tana mamakin meya maido matar nan kuma? Yan cikin gidan ma sun barta ta huta kuma se ita zata kwaso jiki tazo ta isheta a daren nan daga zangar ta dan basu fuska dazu.

"Daman Tuwo na kawo miki, yo ahe ke tuni kin makari da babban yanka" Ta sake fada tana bude Langar tuwo da miyar data jere a qasa. Warin daddawa da kuka suka daki Binta a ranta ta danna Ashar tace
"Ni zanci wannan baqin tuwon da miya kamar yawun Kaza?"
"Zabuwa Babansu yace a yanka a zuba miki a miyar" Jamilar ta sake fada tana karkato mata da kwanon miyar dan taga Namomin da suke ciki wanda qarya takeyi ba Hashimu ne ya bada ba satar mata Zabo tayi tasa aka yanka tasan kuma da zarar labari ya isa kunnensa gobe akwai bala'i dan da tace masa Bintan tazo ma seda ya kora mata ashar yace ina ruwansa da wata Binta.

"Allah sarki aiko nagode, bari na ajiye da safe se a dumamamun nayi kari dashi"

"Aiko daman yafi dadin ci dumamen" Jamila ta sake fada tana gyara zama. Hira ta shiga sokowa Binta kamo nan kamo can, da taga bata da niyyar tashi dole ta bude naman ta mata bismilla aiko ta dirar masa seka rantse bata ci a gida bayan iyakar qoqari Mazajensu sunayi da wuya ayi miya lami a gida. Seda suka tada naman tas wanda Jamila ce ta cinye Rabi Binta ta janye Furarta gefe dan wannan kam ba zata bata ba.

"Uhm bari na tashi dare ya fara nisawa, nace da safe in Allah ya kaimu nazo na rakaki ki gano gidan ummarsu Babangida ko?" Jamila ta fada yana miqewa tsaye da shirin tafiya.

"Wace Ummarsu Babangida kuma?" Ta tambayeta cikin rashin fahimtar wa take nufi.

*MAMAN MARYAM ONLINE BUSSINESS*

*Ina kuke Mata Yan kwalisa , Ina nufin isassun Mata ,Wai shin Kuna da labarin shahararren company nan namu na GHT wato good healthtreatments*
*Wanda yazo muku da fitattu Kuma* *ingantatattun suppliment ,na dukkan matsalolin ku*❓

*Ina maisan tayi kyau,irin na isassun Mata ya fitar Miki da shef dinki tayi Miki gyara in and out ,nemi royal jelly dinmu na company GHT*
*Wanda aka yishi da xuma ,kundai San amfanin Zuma basai na fada miku ba , hajiya ta kixo ki Yi gyara domin ki kerewa sa,a kije taro ko baki da ko sisi kiji Ana rangada Miki hajiya , saboda yanda Zaki Kara kwarjini ,kina walwali acikin mutane , magungunan ght anti agen ne suna maida tsohuwa* *yarinya ,yarinya Kuma ta koma jaririya*

*Muna da magunguna iri iri*

*NA GYARAN JIKI*
*NA GOGE NANKARWA*
*NA RAGE QIBA*
*NA CIRE TUMBI*
*NA QARIN HIPS*
*NA GIRMAN BREAST*
*NA QARA TSAHON GASHI*

*NA QARIN NI'IMA WANDA ZAI SAUKAR MIKI DA NI'IMA YA QARA MIKI DADI DA ZAQI A GURIN OGA*

*Muna da hadin bita zai zai ,indai kishiyar ki tana Shan magungunan GHT, tohh lallai sunan ki sorry domin kuwa tazarar dake tsakanin ku kamar tazarar sama ne da kasa*

*Muna da Wanda zai matseki ciki da waje Andai na yayin dinki uwargida*,

*Sannan company mu na GHTBai tsaya anan ba*
*Ya kawo muku maganin dukkan matsalolin ku*

*INA MASU HAWAN JINI?*
*INA MASU CIWON ZUCIYA?*
*INA MASU CIWON QODA?*
*INA MASU CIWON HANTA?*
*INA MASU SICKLER?*
*INA MASU HIV?*
*INA MASU CANCER?*
*INA MASU NEMAN HAIHUWA?*

*Tohh Ku matso GHT taxo muku da magungunan matsalolin ku*
*Kuma muna da testimonys da yawa ,na wadanda suka gwada suka da ce*

*Munanan a KANO KUNTAU*
*Kuma muna tura Kaya ko wanne gari cikin aminci da gaskiya , kuma kayan mu muna badashi ne cikin price Mai rahusa ga kyau ga inganci sannan ga Rahusa*

*Kutuntube mu ta wannan number 📞08129249549*
*📲07011401314*

"Au, Bara'atu zance miki ko zaki fi ganewa. Juma'a idan tazo mako uku kenan da tarewarsu, kinga gida badai gida ba tamkar naku ba Birni, ai gaskiya Alhaji Audu yayi karamci ya kuma kyauta saboda dangin uban nan nata tasamma ci musu mutunchi sukayi wlh, kinsan basa son uwarta ta fa daman akace. To yana mutuwa suka tada bala'i wai gidan da yake ciki gadonsu ne su goma ya hana a raba ya ke zaune ciki dan haka se su fitar musu a gida a raba sannan su san kasonsu, kinga dan taqin da akace sun cire musu a matsayin rabon baban nasu? Ai badan Alhaji Audu ba a garin nan bamu san Ina Inna Hajara da yayanta zasu tsoma ransu ba shine fa ana gaya masa ya aiko aka far....."

"Ya isa haka dan Allah, kije Allah ya kaimu goben se kizo ki rakani" Binta ta dakatar da Jamila daga zubar da takeyi tamkar famfon daya lalace. Jamilar ta fice bayan ta mata sallama tana dariya kamar wata wawiya tana fita Binta ta mayar da qofa ta rufe, wani kalar tashin hankali ke rufzo mata dukda yanayin garin babu zafi amma ita zufa ce take keto mata ta kafofin gashin jikinta. Ta ri ga safa da marwa a dakin tana huce ita kadai tama rasa ta ina zata fara tunani, Audu ya ginawa Bara'atu gida yaushe akayi haka bata sani ba kuma akan me?

To kodai sun maida Auransu ne bata sani ba tana can gaho? Ta jefawa kanta tambayar seta zabura a fili tace
"Kut**uba kenan ma ai kuwa da anyi yaqi duniya ni za'a yaudara a ninke baibai?"

Kukan da Naziru ya sakane ya ankarar da ita hayagagar da takeyi ta daukeshi taci gaba da zaga dakin tana jijjigashi, wato mutanen nan anyi qungurumayen munafukai, ashe da Jamila bata gaya mata ba haka zata gama zamanta ta tafi ba tareda ta samu wannan mugun labarin ba aikuwa zasuga tatura, seta nuna musu ta fisu iya tashanci wato uta zasu hadewa kai?
Tabbas Turai tayi gaskita da tace tana can Bihim zasu rabe komai a barta da zare ido gashi kuwa an fara.
Chapter 63 · 0% Book details