Sashe 87
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Bari nayi sallar La'asar se naci abincin" Alhaji Audu ya faɗa kafin ya yunƙura ya shige banɗakin dake manne da ɗakin barcin nasa. Momy ta zauna kan doguwar kujera kwaya ɗaya dake cikin ɗakin Hajiya kuma har sannna tana zaune kan gado tana ƙarewa Momyn kallo kamae wata farin shigar Maita har Audu ya fito ya tada sallah ya idar ya hau kan abincinsa Binta na zaune ita kuma Momy bata ce mata ta fita ba dukda zaman nata ya ɓata mata rai. Har a yanzu da shekaru suka miƙa tsakanin ita ko Rabi babu wadda ta isa ta shiga Turakar Alhajin a ranakun girkin Hajiya Binta amma ita ko a kwance suke tana iya faɗo musu a yanzu ne kuma Alhaji Audun yake son ya gyara wannan barakar har yake ƙoƙarin taka mata burki wasu lokutan sedai a banza domin ta rigada ta raina shi, bashi da wani kwarjini ko Martaba a idonta da zw ce tayi abu tayi ko ya hanata ta hanu har ila yau kuma zancen tayi laifi ya mata faɗa kamar yanda yake musu fa babu shi, ita lamarin Alhaji da Hajiya Binta ma har rasa matsayin da zata ajiye shi takeyi dan ko a labarai bata taɓa cin karo da Macen da take zuba sharafi a gidan Auranta irin Hakiya Bintan ba.
"Ina kin gaka abinda ya kawoki?" Muryar Audu ta ratsa kunnuwansu, Momy na danna waya ta ɗago so take ta fahimci dawa yake a cikinsu? Ita me girki ko kuwa Binta data zo ta tasasu gaba? Hamshaƙiyar kuwa ƙara gyara zama tayo dan a tsammaninta da Aishar yake seda ya sake maimaita maganar yana kallon idonta kafin ta ankare, ta buɗe baki zata faɗa masa ba dadi se kuma ta gimtse data tuna tanada shirin da take so ta cimma seta miƙe tsaye tana murmushi tace
"Ai to bari naje, duk na shafa'a ne wlh se naga kamar a Ɗakina nake". Tana dafda fita daga ɗakin wayar Momy tayi ƙara alamar shigowar kira, Hajiya ta fice amma ta coge a bakin ƙofa ta kasa kunne, abin ya rigada ya zame mata Ɗabi'a ko ace ciwo, gulma da Laɓe, tsabar yanda ta ɗorawa kanta bala'i ko a hanya take tafe taji wasu na ƙusƙus seta dakata ta kasa kunne ko ba zataji ko ta fahimci abinda suke faɗi ba, ga zargi da tsarguwa ko yayan cikinta taga suna magana seta tsargu da ita suke ko wani abun suke shiryawa.
A cikin ɗakin kuwa a speaker Momy ta saka wayar saboda kunnenta dake mata ciwo kwana biyu bata kara wata a kunnen muryar Ahmad ta ratso wayar yana cewa
"Momy, kin masa maganar kuwa?"
"Tukunna dai, wai idan sauri kakeyi haka ka tareshi da kanka kayi masa maganar mana seni zaka mayar yar aikenka" ta bashi amsa. Daga waje Binta ta sake manna kunne a jikin ƙofa tunda taji muryar Ahmad da kuma cewar anyi magana wace maganace? Abinda take so kunnuwanta su zuƙo mata kenan.
Ahmad ya sake marairaicewa Momy yana cewa
"Haba sweet mother, haba rabin raina kinsan dai bazan iya tunkararsa ba kuma na gaya miki Jafar ya masa magana yace he will get back to us yanzun kusan one month kenan bamuji komai daga gareshi ba and time is really against me Momy, idan baze samu ta hanyar sa ba na sani na nemi wani Alternative ɗin kinji Mamana? Ya ƙarasa maganar kamar ze saka mata kuka yana idarwa kuma tari ya sarƙe shi"
"Bakaje Asibitin da nace kaje ba kenan?" Ta jefa masa tambaya ba tareda tabi ta kan maganar da suka fara ba, Ahmad da tarin ya tsagaita masa yace
"Naje wlh Momy an rubutamun magani na ma farasha, kiyi masa maganar yanzu dan Allah kinji"
"Zanyi" ta faɗa a taƙaice daga nan ta kashe wayar. Alh Audu na cin abincinsa kuma yana sauraron duk wayar da sukeyi tuni kuma ya fahimci zancen da tunin da Ahmad ɗin yake magiyar tayi masa. Ruwa yasha yana kallonta yace
"Shi baze iya zuwa ya sameni muyi magana ba se ya ringa turomun yan aike?"
"Wane shi? Wannan ai se Yayan gida Yayan So" ta bashi amsa hankalinta na kan wayarta se yayi shiru yana kallonta, a yan shekarun nan Aishar ta fara canzawa, idan tayi wani abun se yaga kamar ta fara gajiyawa dashi ne kamar me neman wani dalili da ze janyo saɓani a tsakaninsu. Ajiyar rai yayi yace
"Ai shikenan, kice masa gobe ya sameni a gidan Gona na Kwanar Dawaki se mu tattauna maganar kuma yazo da takaddun"
"Baka da lambar wayarsa kaima kenan?" Ta faɗa tana tsareshi da ido, tamke fuska yayi be kuma bata amsa ba ya shige banɗaki wanko hannu.
Tayi tsaki a ranta wani abu me ɗaci yana taso mata seta miƙe ta shiga tattara kwanukan daya gama dasu ta ɗora akan Try ɗin data kawo su ta fita. A bakin ƙofa sukayi kiciɓus da Hajiya dake dakon jiran a faɗi gundarin abinda take so taji buƙatar da Ahmad ɗin yake nema a gurin Alhajin da har yace ya sameshi a gidan Gona.
Kardai fa tufka take ta baya tana warwarewa tana nan tana haƙilon ganin sun danne komai Aisha ta ringa mata zagon ƙasa suna wawasa ita da Yayanta? Dole ta Ƙara saka idanu kenan akan harkar shige da ficen gidan da duk abinda yake faruwa wannan maganar ma da ba'a ƙarasa ba seta bi diddiginta tunda sunan Jafar ya fito a ciki shi zata tambaya dukda dai shegen Yaro ne ba lallai ya faɗa mata ba tunda sirrin ubansa Ahmad ne. Tana ganin Momyn ta ɗan diririce se kuma ta waske ta tura ƙofar irin dawowa ta sakeyi zata shiga. Momyn ta kaɗa kai kawai ta wuce, ba yau Hajiyar ta sababa Laɓe ya zame mata ɗabi'a.
Hajiya na ganin Momy ta sauka ta juyo itama ta fice dan akwai abinda yake a gabanta yanzu kafin ta juya takan zancen Ahmad ɗin, ɗakinta ta wuce ta tarar da YAKUBU na cin abinci, Hajiya ƙarama na tsaye gaban console mirror dake falon tana gyara ɗaurin kallabinta. Ganinta yasaka Binta sakin fuska ta washe haƙwaranta duka, guda biyu data sakawa Haƙorin Makka na zinari sunata ƙyalli, Umarar Bara da sukaje ta cire Asalin guda daya na bakinta daya cinye aka saka mata biyun.
"Kinyi kyau uwar masu gida, yau zuciyar mahassada sedai ta buga dan baƙin ciki" Hajiyar ta faɗa tana ƙarasawa kusa da ita. Hajiya ƙarama ta saki murmushi kafin ta shiga juyawa dan ta nunawa Hajiyar kwalliyarta dakyau, Fitted gown ce ta wani cotton London Brocade a jikinta dark blue me zanen flower sea green da fari a jiki, kudinsa ya tasamma dubu sittin, Jafar ne ya aikowa da Hajiyar su sun kai guda goma yace a ɗinka mata dogayen riguna saboda laushinsa yasan zeyi dadin sakawa shine Hajiya ƙaramar ta kwashe uku dan tasan ba ɗinkawa Hajiyar zatayi ba ta kai aka mata lalatattun dinkuna a ciki wannan fitted gown din itace me ɗan dama dama dan ta rufe mata jiki gaba daya illarta kawai shape dinta daya bayyana ƙarara.
"Kin fa gama haɗewa Yar nan babu makusa" Hajiyar ta sake faɗa tana bata hannu suka kashe daidai nan wayarta tayi ƙara, sunan Abba Tee ya bayyana akan screen ɗin. Tsanar dadi harda wani maƙale hannaye Hajiya tayi sama kamar Kangaroo bakin nan ko har maƙogaronta ana hangowa, Hajiya ƙarama ta amsa wayar cikin muryar shagwaɓa kamar zata fashe da kuka tace
"Harka iso"
"Yes Babe, ina waje" ya bata amsa daga cikin wayar, ta sake narkewa tana cewa
"Baka shigo ciki ba? Issa baya nan ne? Kayi horn ze buɗe maka Get ya shogar dakai palour kafin na fito"
"He isn't here, oh kamar gashi nan wani Buzu ko? ya buɗe Get ɗin bari na shigo"
" Saurayin ya sake Faɗa kafin ya katse wayar.
Hajiya ta sake bata hannu suka kashe tana cewa
"Wai, Allah ya taimakemu, maza kije ki ƙara turare, duba ɗakina akwai wannan Disaina da kike nacin na baki na gurin Yayanki ki ɗauka, bari na duba abincin idan sun kammala"
"An gama kumai har na shirya a Try kaowa kawai za'ayi" Inji Hajiya ƙarama
"Yauwa yar gari, jeki to kar yayita zama Allah ya bada sa'a" cewar Binta. Hajiya ƙarama ta wuce ɗaki ta ƙaro turare kamar yanda Binta tace ta fito tana takun yauƙi Albarkatun jikinta na motsawa danma kayan jikin nata sun matseta kam hakan ya rage musu samun damar rangaji yanda ya kamata.
Yanda Yaran Alhaji Audu Maza suke Dogaye ginannu idan ka cire Ahmad daya ɗauki Jikin Aisha bashida ƙiba sam haka beyi irin tsahonsu ba to Matan ma duk haka suke dogaye masu cikakken jiki, Allah ya taimake su da ƙira mai kyau ta jiki data fuska musamman da dukansu se akayi katari suka ɗauko fuskar Dada, Farare tas ɗin cikinsu Amina, Aslmaiyya da Hajiya ƙarama da yan Biyun Hajiya Rabi Baba Bilki takance kamanninsu kwabo da kwabo da Dadarsu.
"Yauwa, saura kuma ki sake maimaita abinda kikayi wancan karon kika saka yayi fushi, kina kallo dai har dubuta dari Turai ta damfareni, koda yake kwalliya ta biya kuɗin sabulu tunda an janyoshi yazo, soyayyar nan ta zamani ke sekace ba wayayya ba da ita ake kama samarin nan, banda abinki waye ze kwasheki haka siɗan ba tareda ya tabbatar kin iya kalar soyayyar da yake da buƙata ba, yar rungumar nan da kis ne dai Allah na tuba ai ba wani abu bane, ban dai ce kije ki buɗe kafa ba ki saka mu shiga uku kuma kuyi a hankali Alhaji ma sama ze iya saukowa kowan...."
"Hajiya!" YAKUBU da ke cin abincinsa tun shigarta be tanka maganar da sukeyi ba ya kira sunanta cikin ɗaga murya me kama da tsawa dan a firgice daga ita har Hajiya ƙaramar suka kalleta kowacce na tsammanin da ita yake. Farantin gabansa ya ture ya miƙe tsaye fuskar sa tamkar zatayi aman bacin ran daya turnuƙeshi lokaci daya.
"Ina kin gaka abinda ya kawoki?" Muryar Audu ta ratsa kunnuwansu, Momy na danna waya ta ɗago so take ta fahimci dawa yake a cikinsu? Ita me girki ko kuwa Binta data zo ta tasasu gaba? Hamshaƙiyar kuwa ƙara gyara zama tayo dan a tsammaninta da Aishar yake seda ya sake maimaita maganar yana kallon idonta kafin ta ankare, ta buɗe baki zata faɗa masa ba dadi se kuma ta gimtse data tuna tanada shirin da take so ta cimma seta miƙe tsaye tana murmushi tace
"Ai to bari naje, duk na shafa'a ne wlh se naga kamar a Ɗakina nake". Tana dafda fita daga ɗakin wayar Momy tayi ƙara alamar shigowar kira, Hajiya ta fice amma ta coge a bakin ƙofa ta kasa kunne, abin ya rigada ya zame mata Ɗabi'a ko ace ciwo, gulma da Laɓe, tsabar yanda ta ɗorawa kanta bala'i ko a hanya take tafe taji wasu na ƙusƙus seta dakata ta kasa kunne ko ba zataji ko ta fahimci abinda suke faɗi ba, ga zargi da tsarguwa ko yayan cikinta taga suna magana seta tsargu da ita suke ko wani abun suke shiryawa.
A cikin ɗakin kuwa a speaker Momy ta saka wayar saboda kunnenta dake mata ciwo kwana biyu bata kara wata a kunnen muryar Ahmad ta ratso wayar yana cewa
"Momy, kin masa maganar kuwa?"
"Tukunna dai, wai idan sauri kakeyi haka ka tareshi da kanka kayi masa maganar mana seni zaka mayar yar aikenka" ta bashi amsa. Daga waje Binta ta sake manna kunne a jikin ƙofa tunda taji muryar Ahmad da kuma cewar anyi magana wace maganace? Abinda take so kunnuwanta su zuƙo mata kenan.
Ahmad ya sake marairaicewa Momy yana cewa
"Haba sweet mother, haba rabin raina kinsan dai bazan iya tunkararsa ba kuma na gaya miki Jafar ya masa magana yace he will get back to us yanzun kusan one month kenan bamuji komai daga gareshi ba and time is really against me Momy, idan baze samu ta hanyar sa ba na sani na nemi wani Alternative ɗin kinji Mamana? Ya ƙarasa maganar kamar ze saka mata kuka yana idarwa kuma tari ya sarƙe shi"
"Bakaje Asibitin da nace kaje ba kenan?" Ta jefa masa tambaya ba tareda tabi ta kan maganar da suka fara ba, Ahmad da tarin ya tsagaita masa yace
"Naje wlh Momy an rubutamun magani na ma farasha, kiyi masa maganar yanzu dan Allah kinji"
"Zanyi" ta faɗa a taƙaice daga nan ta kashe wayar. Alh Audu na cin abincinsa kuma yana sauraron duk wayar da sukeyi tuni kuma ya fahimci zancen da tunin da Ahmad ɗin yake magiyar tayi masa. Ruwa yasha yana kallonta yace
"Shi baze iya zuwa ya sameni muyi magana ba se ya ringa turomun yan aike?"
"Wane shi? Wannan ai se Yayan gida Yayan So" ta bashi amsa hankalinta na kan wayarta se yayi shiru yana kallonta, a yan shekarun nan Aishar ta fara canzawa, idan tayi wani abun se yaga kamar ta fara gajiyawa dashi ne kamar me neman wani dalili da ze janyo saɓani a tsakaninsu. Ajiyar rai yayi yace
"Ai shikenan, kice masa gobe ya sameni a gidan Gona na Kwanar Dawaki se mu tattauna maganar kuma yazo da takaddun"
"Baka da lambar wayarsa kaima kenan?" Ta faɗa tana tsareshi da ido, tamke fuska yayi be kuma bata amsa ba ya shige banɗaki wanko hannu.
Tayi tsaki a ranta wani abu me ɗaci yana taso mata seta miƙe ta shiga tattara kwanukan daya gama dasu ta ɗora akan Try ɗin data kawo su ta fita. A bakin ƙofa sukayi kiciɓus da Hajiya dake dakon jiran a faɗi gundarin abinda take so taji buƙatar da Ahmad ɗin yake nema a gurin Alhajin da har yace ya sameshi a gidan Gona.
Kardai fa tufka take ta baya tana warwarewa tana nan tana haƙilon ganin sun danne komai Aisha ta ringa mata zagon ƙasa suna wawasa ita da Yayanta? Dole ta Ƙara saka idanu kenan akan harkar shige da ficen gidan da duk abinda yake faruwa wannan maganar ma da ba'a ƙarasa ba seta bi diddiginta tunda sunan Jafar ya fito a ciki shi zata tambaya dukda dai shegen Yaro ne ba lallai ya faɗa mata ba tunda sirrin ubansa Ahmad ne. Tana ganin Momyn ta ɗan diririce se kuma ta waske ta tura ƙofar irin dawowa ta sakeyi zata shiga. Momyn ta kaɗa kai kawai ta wuce, ba yau Hajiyar ta sababa Laɓe ya zame mata ɗabi'a.
Hajiya na ganin Momy ta sauka ta juyo itama ta fice dan akwai abinda yake a gabanta yanzu kafin ta juya takan zancen Ahmad ɗin, ɗakinta ta wuce ta tarar da YAKUBU na cin abinci, Hajiya ƙarama na tsaye gaban console mirror dake falon tana gyara ɗaurin kallabinta. Ganinta yasaka Binta sakin fuska ta washe haƙwaranta duka, guda biyu data sakawa Haƙorin Makka na zinari sunata ƙyalli, Umarar Bara da sukaje ta cire Asalin guda daya na bakinta daya cinye aka saka mata biyun.
"Kinyi kyau uwar masu gida, yau zuciyar mahassada sedai ta buga dan baƙin ciki" Hajiyar ta faɗa tana ƙarasawa kusa da ita. Hajiya ƙarama ta saki murmushi kafin ta shiga juyawa dan ta nunawa Hajiyar kwalliyarta dakyau, Fitted gown ce ta wani cotton London Brocade a jikinta dark blue me zanen flower sea green da fari a jiki, kudinsa ya tasamma dubu sittin, Jafar ne ya aikowa da Hajiyar su sun kai guda goma yace a ɗinka mata dogayen riguna saboda laushinsa yasan zeyi dadin sakawa shine Hajiya ƙaramar ta kwashe uku dan tasan ba ɗinkawa Hajiyar zatayi ba ta kai aka mata lalatattun dinkuna a ciki wannan fitted gown din itace me ɗan dama dama dan ta rufe mata jiki gaba daya illarta kawai shape dinta daya bayyana ƙarara.
"Kin fa gama haɗewa Yar nan babu makusa" Hajiyar ta sake faɗa tana bata hannu suka kashe daidai nan wayarta tayi ƙara, sunan Abba Tee ya bayyana akan screen ɗin. Tsanar dadi harda wani maƙale hannaye Hajiya tayi sama kamar Kangaroo bakin nan ko har maƙogaronta ana hangowa, Hajiya ƙarama ta amsa wayar cikin muryar shagwaɓa kamar zata fashe da kuka tace
"Harka iso"
"Yes Babe, ina waje" ya bata amsa daga cikin wayar, ta sake narkewa tana cewa
"Baka shigo ciki ba? Issa baya nan ne? Kayi horn ze buɗe maka Get ya shogar dakai palour kafin na fito"
"He isn't here, oh kamar gashi nan wani Buzu ko? ya buɗe Get ɗin bari na shigo"
" Saurayin ya sake Faɗa kafin ya katse wayar.
Hajiya ta sake bata hannu suka kashe tana cewa
"Wai, Allah ya taimakemu, maza kije ki ƙara turare, duba ɗakina akwai wannan Disaina da kike nacin na baki na gurin Yayanki ki ɗauka, bari na duba abincin idan sun kammala"
"An gama kumai har na shirya a Try kaowa kawai za'ayi" Inji Hajiya ƙarama
"Yauwa yar gari, jeki to kar yayita zama Allah ya bada sa'a" cewar Binta. Hajiya ƙarama ta wuce ɗaki ta ƙaro turare kamar yanda Binta tace ta fito tana takun yauƙi Albarkatun jikinta na motsawa danma kayan jikin nata sun matseta kam hakan ya rage musu samun damar rangaji yanda ya kamata.
Yanda Yaran Alhaji Audu Maza suke Dogaye ginannu idan ka cire Ahmad daya ɗauki Jikin Aisha bashida ƙiba sam haka beyi irin tsahonsu ba to Matan ma duk haka suke dogaye masu cikakken jiki, Allah ya taimake su da ƙira mai kyau ta jiki data fuska musamman da dukansu se akayi katari suka ɗauko fuskar Dada, Farare tas ɗin cikinsu Amina, Aslmaiyya da Hajiya ƙarama da yan Biyun Hajiya Rabi Baba Bilki takance kamanninsu kwabo da kwabo da Dadarsu.
"Yauwa, saura kuma ki sake maimaita abinda kikayi wancan karon kika saka yayi fushi, kina kallo dai har dubuta dari Turai ta damfareni, koda yake kwalliya ta biya kuɗin sabulu tunda an janyoshi yazo, soyayyar nan ta zamani ke sekace ba wayayya ba da ita ake kama samarin nan, banda abinki waye ze kwasheki haka siɗan ba tareda ya tabbatar kin iya kalar soyayyar da yake da buƙata ba, yar rungumar nan da kis ne dai Allah na tuba ai ba wani abu bane, ban dai ce kije ki buɗe kafa ba ki saka mu shiga uku kuma kuyi a hankali Alhaji ma sama ze iya saukowa kowan...."
"Hajiya!" YAKUBU da ke cin abincinsa tun shigarta be tanka maganar da sukeyi ba ya kira sunanta cikin ɗaga murya me kama da tsawa dan a firgice daga ita har Hajiya ƙaramar suka kalleta kowacce na tsammanin da ita yake. Farantin gabansa ya ture ya miƙe tsaye fuskar sa tamkar zatayi aman bacin ran daya turnuƙeshi lokaci daya.