Sashe 54
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Wai sau nawa zan hanaki tsoma mun baki idan ina magana da mutane? Aiki kikeyi dama ko kuwa zaman gulma shiyasa kika maqalw gaban Tv tun dazu kin kasa gama gogewa kenan?"
"Kiyi haquri hajiya ba gulma bace ba maganar gaskiya ce wanda a ganina duk abinda zaku shirya dole ya zamani kunyi akan saitin da ba za'a ruguzaku ba. Akwai hanya me sauqi da zakubi ku heganta cikin nan kona Alhajin ne tunda dai an samu tangardar lissafi girman ciki ya zarta watanninsa" Barira ta sake fada bayan ta saki duster da take goge goge da ita ta juya ga abinda tafi iaywa wato hada tuggu da munafunci, abinda ya kaso mata aure kenan kuma ya korota daga qauyensu saboda an mata tambari duk wata Masifa data taso tsakanin kishiya da kishiya a garin In sha Allahu se kaji sunan Barira a ciki ita ta qullota kuma lafiya lau take zaune da nata Mijin tsabar yanda kawa qara da zuwa shari'a gaban me gari akanta yaqi qarewa yasa ya sallameta shine wata qawarta da ta fito Aikatau Birni ta janyota itama suka taho a gidansu Turai waccen take aiki dan haka da sukazo ita kuma tata me aikin sannan ta tafi gida se Mamarsu tace ta dauki Bariran dukda bata so ba dan bata son me aiki babba kodan irin Mazansu ido a mata amma ganin ta iya aiki kuma dai ta ganta kalar gidadawa kamar ba zata yarda da irin wannan abin ba yasa ta karbeta kuma se take jin dadin zama da ita dan Barira badai ladabi da duk cikin iya takunta.
Bi ta da Turai suka shiru sunasauraronta ita kuma ganin sun bata hankali yasa taci gaba da cewa
"Ina itace naji kunce tsohuwar kilaki?" Turai ta gyada kai alamar haka ne, Barira ta gyara zama tana buga cinya tace
"Yo Allah na tuba kwace goruba a hannun kuturu ai shiyafi komai sauqi, ai kamar yanda Hajiya tace miki ki koma gefe kihya kallo to haka zakiyi amma kafin nan se kin basa bam din da ze tayar da kowa, abu daya zafi fada da ze maida Alhaji hayyacinsa in ma cikinsa ne in ma ba nasa bane kawai kice masa kin gano da cikin ta shigo, zuwa sukayi aka kwantar dashi se yanzu da suke ganin ta dan kwana biyu aka tashe shi kina fada masa hala kija gefe kiyi zamanki kawai ki saka ido, in cikinsa nema zaki gane idan ma na wani ne kin haska masa hanya duk ma yanda akayi ze binciko"
"Amma Barira kanki yana kawo haske, to tsaya dagaske ana kwantar da cikin kar kuma mu fadi abinda ba haka ba" Turai ta fada tana jinjina tunani irin na Barira.
Barirar ta sake washe baki tace
"Kai Hajiya yo wannan har wani abun mamakine ko a nan cikin Binni ai anayi. Mu a karkarar mu kihiya tanawa kihiyarta asiri a kwantar mata da ciki se kiga Mace ta hekara goma da ciki ayita cewa Aljanune nan ba asan Asiri aka mata ya kwanta ba in ta dage da neman magani se kiga ya tahi an haife dan to haka idan Yara suka dakko abin kunya hima zuwa ake a kwantar hi se an kwana biyu a daki lissafi yayi daidai se tayar dahi kiga yarinya ta haihu qalau babu me cewa komai"
"To amma ai ita watanta takwas yanzu fa" Binta ta fada bayan data gama hada lissafi akanta. Barira ta sake sheqewa da dariya irinta shegun qauye tace
"Kai Hajiya yane muke ta maimaita magana amma kamar baku ganewa. Dama ai kintatar lokaci akeyi se a daga cikin kinga in ta haihu nan da sati ko biyu ne ai babu me cewa komai tunda ta shiga wata na tara a daki to amma idan kika bullo da wannan maganar ko shekara tayi kanta haihu kin saka kokwanto a zukatan jama'a musamman da daman tana da tambari sannan shi kansa me gidan kinga lissafin da yakeyi na cikin ai be kai asalin watannin qiyasin girmansa ba ko?"
https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*PAGE 21*
Rai fes Binta ta koma gidase da tayiwa Barira kautar Naira Dari biyu tukuici. Ita kadai ta ringa sakin murmushi a hanya harta koma gida nan ta tarar da Lantana rabe qofar daki tana jiranta.
"Ai nazo tuntuni ashe kin fita, Mairo ma tazo ta tafi kin santa ita ba zata iya jira ba" Lantanar ta fada bayan data karni muqullin daki ta bude mata.
Binta ta shiga tana cewa
"Eh ai ita da yake ta fiki tunani tana kuma da abinyi a gida shiyasa ba zata zauna ba tunda babu aikin da zatayi"
"Kai Hajiya" Lantanar ta fada tana yaqe dan taji zafin maganar Bintan kullum haka take yaba mata su da tana da zuciya yaci ace yanzu ta haqura da aiki a gidan gaba daya.
Binta ta shimfide Zakariyya tana miqa tareda wash
"Ai yaci ki dena goyashi haka Hajiya kar ku ringa danne na cikin, in fita ta kama ki ringa cewa na turo miki Aisha ta mana tana tayaki da daukarsa" Lantana da bata daddara ba ta sake fada, se kuma akaci sa'a Bintan ta yarda da shawarar tace zata ringa yin hakan. Tana zaune a Falo tana ayyana yanda maganar nan zata tashi Lantana na share share sega Audu kamar an jefoshi ya fado falon, ta miqe da sauri tana tambayarsa lafiya kuwa yace
"Babu lafiya, yanzu Suleiman ya dawo daga Bechi yake shaidamun Allah yayiwa Babansu Bara'atu Rasuwa, ki shirya yanzu zamu tafi can dukda dai nasan ba zamu samu jana'iza ba amma gara muje din in yaso ma dawo gobe".
Binta taja tsaki bayan data koma ta zauna tana cewa
"Shine ka shigo a gigice har kana fadar mun da gaba na zata ma qata asarar ce ta fadawa Dukiyarmu? To Allah ya jiqan musulmi amma babu inda zani da ranar nan fatsar fatsar".
Zubaida na bacci bacci ya shiga itama ya shaida mata rasuwar, iyakar abinda ta sani kan Bara'atu tsohuwar matarsa ce ba'a fi watanni biyu bama data san itace uwargidansa ba Binta ba a bakin Mairo mewa Binta Girki ranar ta roqeta ta koya mata yanda akeyin Gero da wake shine tace ai Maman Baba ma tana son Abincin a sannan ta tambayeta wacece ita tace mata Bara'atu uwargidan Audun tayi mamaki kwarai jin har yara biyu ne tsakaninsu dan be taba gaya mata ba data yi masa zancen kuma har yajin kwanaki ya mata saboda tace be kyauta ba dakyar suka shirya bayan yaja mata kashedin babu ruwanta da sabgarsa wadda bata shafeta ba, bata san meya rabashi da Bara'atu ba dan haka karta kuskura ta tsoma kanta a ciki shiyasa kidimewar da yayi yanzun da ya gaya mata rasuwar Baban Bara'atun ta bata mamaki, matar daya cire daga rayuwarsa ita da Yayan da suka haifa tare na menene ze dawo dan ta rasa mahaifi?
Haka ta cicciba ta hada abinda zata buqata a yar jaka tana hasaso yanda yan Bechin zasu karbe ta wannan karon, bata sake zuwa ba tun bayan da aka kaita wancan Al'amarin ya faru haka suma A matan Aisha ce kadai tazo babu dadewa tana ciwon Nono Audu yace tazo Kano taga Likita ta kwana hudu a dakin Zubaidan kuma dai lafiya lau babu abinda ya hadasu har suka rabu ta koma.
Bata san banda Binta za'ajwe ba seda yaceta fito su tafi, ta kulle qofarta tana tsaye jikin dakin Tsakar gida wanda Abdullahi yake kwana ciki kafin a kaishi makarantar kwana tun daga nan kuma idan anyi hutu Bechi yake tafiya da Audu ya tambayi ba'asi yace babu komai be matsa ba ya qyale shi kuma dai be fasa yi masa komai ba tamkar yana gidansa ze aikawa da Aminu kudin komai nasa ayi masa.
"Ba tare da Maman Zakariyya zamuje ba?" Ta tambayeshi jin yace suje,
"Badani za'aba uwar azagwai" Binta dake tsaye kan Baranderta ta turo dauri gaba irin wanda Zubaidan takeyi ta fada kome ta tuna kuma se tayi saurin sakin fuska ta matso kusada ita tana cewa
"Yauwa kar in manta, idan kun dawo daga Qauyen nan akwai taimakon da zakimun. Wlh in gaya miki qanwar qawatace Ibtila'i ya hauta wani shege ya dirka mata ciki, to kuma ta samu Miji Aure nan da wata biyu wannan abu ya faru shine nace ko zaki taimaka ki kaimu inda kuke zuwa a kwantar muku da ciki a samu asiri ya rufu ayi Auran nan idan yaso intayi wata kamar biyar a tayar dashi ko kinga sahu a likafa babu me cewa wani abu".
Sak Zubaidan tayi tana kallonta har ta kai qarshe yanda take doka murmushi kadai ya isa yasa ka gane babu Allah a ranta makirci ne zallah ta hado, waiwayawa tayi ta kalli inda Audu yake tana fatan ace ya rigada ya fita beji wannan maganar da Bintan takeyi ba amma se taga yana tsaye ya zuba mata ido tamkar yanda Bintan take kallonta tana murmushi.
"Kinyi shiru baki ce komai ba" Bi ta ta sake fada har tana dafata fuska dauke da murmushin makirci se ta saka hannu ta tureta tana cewa
"Bani da lokacin Amsa shirmenki"
Binta tayi shewa harda rangada guda tace
"Allah nawa Annabi na uwata, yarinya ba kecw bakida lokacin amsani ba nice bani da lokacinki, kuma shirme da kikace a tsakaninmu za'a tantance wadda take shirme kwanannan, kiyiwa Bara'atu gaisuwa injini kinji Allah ya jiqan Babanta" daga haka ta juya tana kada Mazaune tana waqa abinta.
Zubaida na tsaye inda take ta kasa motsi har seda Audu yayi mata magana kafin ta shiga daga qafa dakyar har suka fita. Seda suka dauki hanya sosai motar shiru babu me cewa qala kafin ya yanke shirun ta hanyar yi mata maganar data saka qirjinta bugawa dam kamar ze fashe.
"Sanda kikace kin zubar da ciki dagaske kike ya fita ko kuwa qaryarku ta yan bariki kikayimun?"
"Kiyi haquri hajiya ba gulma bace ba maganar gaskiya ce wanda a ganina duk abinda zaku shirya dole ya zamani kunyi akan saitin da ba za'a ruguzaku ba. Akwai hanya me sauqi da zakubi ku heganta cikin nan kona Alhajin ne tunda dai an samu tangardar lissafi girman ciki ya zarta watanninsa" Barira ta sake fada bayan ta saki duster da take goge goge da ita ta juya ga abinda tafi iaywa wato hada tuggu da munafunci, abinda ya kaso mata aure kenan kuma ya korota daga qauyensu saboda an mata tambari duk wata Masifa data taso tsakanin kishiya da kishiya a garin In sha Allahu se kaji sunan Barira a ciki ita ta qullota kuma lafiya lau take zaune da nata Mijin tsabar yanda kawa qara da zuwa shari'a gaban me gari akanta yaqi qarewa yasa ya sallameta shine wata qawarta da ta fito Aikatau Birni ta janyota itama suka taho a gidansu Turai waccen take aiki dan haka da sukazo ita kuma tata me aikin sannan ta tafi gida se Mamarsu tace ta dauki Bariran dukda bata so ba dan bata son me aiki babba kodan irin Mazansu ido a mata amma ganin ta iya aiki kuma dai ta ganta kalar gidadawa kamar ba zata yarda da irin wannan abin ba yasa ta karbeta kuma se take jin dadin zama da ita dan Barira badai ladabi da duk cikin iya takunta.
Bi ta da Turai suka shiru sunasauraronta ita kuma ganin sun bata hankali yasa taci gaba da cewa
"Ina itace naji kunce tsohuwar kilaki?" Turai ta gyada kai alamar haka ne, Barira ta gyara zama tana buga cinya tace
"Yo Allah na tuba kwace goruba a hannun kuturu ai shiyafi komai sauqi, ai kamar yanda Hajiya tace miki ki koma gefe kihya kallo to haka zakiyi amma kafin nan se kin basa bam din da ze tayar da kowa, abu daya zafi fada da ze maida Alhaji hayyacinsa in ma cikinsa ne in ma ba nasa bane kawai kice masa kin gano da cikin ta shigo, zuwa sukayi aka kwantar dashi se yanzu da suke ganin ta dan kwana biyu aka tashe shi kina fada masa hala kija gefe kiyi zamanki kawai ki saka ido, in cikinsa nema zaki gane idan ma na wani ne kin haska masa hanya duk ma yanda akayi ze binciko"
"Amma Barira kanki yana kawo haske, to tsaya dagaske ana kwantar da cikin kar kuma mu fadi abinda ba haka ba" Turai ta fada tana jinjina tunani irin na Barira.
Barirar ta sake washe baki tace
"Kai Hajiya yo wannan har wani abun mamakine ko a nan cikin Binni ai anayi. Mu a karkarar mu kihiya tanawa kihiyarta asiri a kwantar mata da ciki se kiga Mace ta hekara goma da ciki ayita cewa Aljanune nan ba asan Asiri aka mata ya kwanta ba in ta dage da neman magani se kiga ya tahi an haife dan to haka idan Yara suka dakko abin kunya hima zuwa ake a kwantar hi se an kwana biyu a daki lissafi yayi daidai se tayar dahi kiga yarinya ta haihu qalau babu me cewa komai"
"To amma ai ita watanta takwas yanzu fa" Binta ta fada bayan data gama hada lissafi akanta. Barira ta sake sheqewa da dariya irinta shegun qauye tace
"Kai Hajiya yane muke ta maimaita magana amma kamar baku ganewa. Dama ai kintatar lokaci akeyi se a daga cikin kinga in ta haihu nan da sati ko biyu ne ai babu me cewa komai tunda ta shiga wata na tara a daki to amma idan kika bullo da wannan maganar ko shekara tayi kanta haihu kin saka kokwanto a zukatan jama'a musamman da daman tana da tambari sannan shi kansa me gidan kinga lissafin da yakeyi na cikin ai be kai asalin watannin qiyasin girmansa ba ko?"
https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*PAGE 21*
Rai fes Binta ta koma gidase da tayiwa Barira kautar Naira Dari biyu tukuici. Ita kadai ta ringa sakin murmushi a hanya harta koma gida nan ta tarar da Lantana rabe qofar daki tana jiranta.
"Ai nazo tuntuni ashe kin fita, Mairo ma tazo ta tafi kin santa ita ba zata iya jira ba" Lantanar ta fada bayan data karni muqullin daki ta bude mata.
Binta ta shiga tana cewa
"Eh ai ita da yake ta fiki tunani tana kuma da abinyi a gida shiyasa ba zata zauna ba tunda babu aikin da zatayi"
"Kai Hajiya" Lantanar ta fada tana yaqe dan taji zafin maganar Bintan kullum haka take yaba mata su da tana da zuciya yaci ace yanzu ta haqura da aiki a gidan gaba daya.
Binta ta shimfide Zakariyya tana miqa tareda wash
"Ai yaci ki dena goyashi haka Hajiya kar ku ringa danne na cikin, in fita ta kama ki ringa cewa na turo miki Aisha ta mana tana tayaki da daukarsa" Lantana da bata daddara ba ta sake fada, se kuma akaci sa'a Bintan ta yarda da shawarar tace zata ringa yin hakan. Tana zaune a Falo tana ayyana yanda maganar nan zata tashi Lantana na share share sega Audu kamar an jefoshi ya fado falon, ta miqe da sauri tana tambayarsa lafiya kuwa yace
"Babu lafiya, yanzu Suleiman ya dawo daga Bechi yake shaidamun Allah yayiwa Babansu Bara'atu Rasuwa, ki shirya yanzu zamu tafi can dukda dai nasan ba zamu samu jana'iza ba amma gara muje din in yaso ma dawo gobe".
Binta taja tsaki bayan data koma ta zauna tana cewa
"Shine ka shigo a gigice har kana fadar mun da gaba na zata ma qata asarar ce ta fadawa Dukiyarmu? To Allah ya jiqan musulmi amma babu inda zani da ranar nan fatsar fatsar".
Zubaida na bacci bacci ya shiga itama ya shaida mata rasuwar, iyakar abinda ta sani kan Bara'atu tsohuwar matarsa ce ba'a fi watanni biyu bama data san itace uwargidansa ba Binta ba a bakin Mairo mewa Binta Girki ranar ta roqeta ta koya mata yanda akeyin Gero da wake shine tace ai Maman Baba ma tana son Abincin a sannan ta tambayeta wacece ita tace mata Bara'atu uwargidan Audun tayi mamaki kwarai jin har yara biyu ne tsakaninsu dan be taba gaya mata ba data yi masa zancen kuma har yajin kwanaki ya mata saboda tace be kyauta ba dakyar suka shirya bayan yaja mata kashedin babu ruwanta da sabgarsa wadda bata shafeta ba, bata san meya rabashi da Bara'atu ba dan haka karta kuskura ta tsoma kanta a ciki shiyasa kidimewar da yayi yanzun da ya gaya mata rasuwar Baban Bara'atun ta bata mamaki, matar daya cire daga rayuwarsa ita da Yayan da suka haifa tare na menene ze dawo dan ta rasa mahaifi?
Haka ta cicciba ta hada abinda zata buqata a yar jaka tana hasaso yanda yan Bechin zasu karbe ta wannan karon, bata sake zuwa ba tun bayan da aka kaita wancan Al'amarin ya faru haka suma A matan Aisha ce kadai tazo babu dadewa tana ciwon Nono Audu yace tazo Kano taga Likita ta kwana hudu a dakin Zubaidan kuma dai lafiya lau babu abinda ya hadasu har suka rabu ta koma.
Bata san banda Binta za'ajwe ba seda yaceta fito su tafi, ta kulle qofarta tana tsaye jikin dakin Tsakar gida wanda Abdullahi yake kwana ciki kafin a kaishi makarantar kwana tun daga nan kuma idan anyi hutu Bechi yake tafiya da Audu ya tambayi ba'asi yace babu komai be matsa ba ya qyale shi kuma dai be fasa yi masa komai ba tamkar yana gidansa ze aikawa da Aminu kudin komai nasa ayi masa.
"Ba tare da Maman Zakariyya zamuje ba?" Ta tambayeshi jin yace suje,
"Badani za'aba uwar azagwai" Binta dake tsaye kan Baranderta ta turo dauri gaba irin wanda Zubaidan takeyi ta fada kome ta tuna kuma se tayi saurin sakin fuska ta matso kusada ita tana cewa
"Yauwa kar in manta, idan kun dawo daga Qauyen nan akwai taimakon da zakimun. Wlh in gaya miki qanwar qawatace Ibtila'i ya hauta wani shege ya dirka mata ciki, to kuma ta samu Miji Aure nan da wata biyu wannan abu ya faru shine nace ko zaki taimaka ki kaimu inda kuke zuwa a kwantar muku da ciki a samu asiri ya rufu ayi Auran nan idan yaso intayi wata kamar biyar a tayar dashi ko kinga sahu a likafa babu me cewa wani abu".
Sak Zubaidan tayi tana kallonta har ta kai qarshe yanda take doka murmushi kadai ya isa yasa ka gane babu Allah a ranta makirci ne zallah ta hado, waiwayawa tayi ta kalli inda Audu yake tana fatan ace ya rigada ya fita beji wannan maganar da Bintan takeyi ba amma se taga yana tsaye ya zuba mata ido tamkar yanda Bintan take kallonta tana murmushi.
"Kinyi shiru baki ce komai ba" Bi ta ta sake fada har tana dafata fuska dauke da murmushin makirci se ta saka hannu ta tureta tana cewa
"Bani da lokacin Amsa shirmenki"
Binta tayi shewa harda rangada guda tace
"Allah nawa Annabi na uwata, yarinya ba kecw bakida lokacin amsani ba nice bani da lokacinki, kuma shirme da kikace a tsakaninmu za'a tantance wadda take shirme kwanannan, kiyiwa Bara'atu gaisuwa injini kinji Allah ya jiqan Babanta" daga haka ta juya tana kada Mazaune tana waqa abinta.
Zubaida na tsaye inda take ta kasa motsi har seda Audu yayi mata magana kafin ta shiga daga qafa dakyar har suka fita. Seda suka dauki hanya sosai motar shiru babu me cewa qala kafin ya yanke shirun ta hanyar yi mata maganar data saka qirjinta bugawa dam kamar ze fashe.
"Sanda kikace kin zubar da ciki dagaske kike ya fita ko kuwa qaryarku ta yan bariki kikayimun?"