Sashe 133
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Baffa ya ringa kallonta har tayi shiru, yafi minti goma kafin ya iya cewa
"Kina nufin tsayin shekara uku da yaron nan yake bibiyarki yana wahalta miki duk ya tashi a banza yanzu zakice ba sonsa kikeyi ba?"
"Wlh Baffa ni ban taɓa cewa yayi mun abu ba, kuma ai ko kai kana hanashi amma se ya dage se yayi kuma ni ina gaya masa ya dena kawai shine baya ji"
Umma ta leƙo a fusace tace
"Dan ubanko dole yanzu kice bakya sonsa mana kuma bake kika saka ya ringa miki wahala ba, Kare ne shi da ze shekara uku saboda rashin zuciya yana tare dake kina nuna masa rashin So kuma yaci gaba da zama dake? Kin gama yaudarar sa kin ɓata masa lokaci saboda baki da mutunchi yanzu zakice bakya Son sa me yasa tun farko baki faɗawa Malam ɗin ba shi da kansa ya kirashi ya sallame shi se yanzu da koɗaɗɗiyar fuskarki zakicewa mutane ke daman bakya son sa to wlh baki isa ba" Umma ta shiga sababi harta manta darene ta muryarta a sama.
Baffa daya kasa magana tuntuni ya kalli Fatima yace ta wuce ɗaki, sum sum ta shige tana jin kamar an sauke mata wani nauyi daga kanta tunda har ta iya furtawa Baffa bata ra'ayin Ahmad tasan magana ta ƙare. A ɗaki Umma ta warwarewa Baffa komai game da zancen Yaron da Afeeyah take so wato Jay ɗan Ƙwallo.
"A ina suka haɗu?" Ya tambayi Umman, ta watsa hannu kafin tace
"Wai acan makarantarsu, Malam ka sanarwa Yaron nan kawai ya turo Iyayensa suzo a ɗaura musu aure kawai idan yaso ta mutu ƙarshen rashin Son Sa".
"Ba za'ayi haka ba, za'a bi komai a hankali, magita zata samu da yardar Allah" inji Baffa. Daren raba shi yayi yana sallah da addu'oi, ya kasance me yawan tsayuwar dare amma yau Umma tasan sallar tasa harda ta neman ɗauki gurin Allah kan wannan abin daya tunkaro shi. Baffa na Son Afeeyah, amma abu ɗaya da tayi imani dashi shine baze bi Son rai ya zubar da ƙimar sa ba shiyasa ya maida lamarin ga buwayin sarki gagara Misali wanda duk hukuncin daya yanke babu wanda ya isa yayi inkari akai.
Kwanaki uku Baffa ya jera yana Istikara cikin tareda tsananta Addu'a da roƙon ubangiji akan Al'amarin, Afeeyah kuwa rai fes dan Ahmad be sake kiranta ba tunda ya tafi kuma ta furta abinda yake ranta dan tasan Umma ta gayawa Baffa zancen Jay babban abinda ya sakat nishaɗi da farin ciki kuma shaida mata da Jay yayi yana tafe Nigeria nan da sati biyu masu zuwa. Saura kwana biyar su koma makaranta semester ƙarshe ce babu Lectures da yawa se aikin project da abinda baza'a rasa ba dan haka ta yanke ba zata koma bahar se yazo tukunna abinda bata taɓayi ba ƙarin hutu tunda ta fara University.
Ta gayawa Badar Jay yana tafe, Badar nason Jay da Afeeyah amma ba kamar yanda take sonta da Ahmad ba kamar yanda take ce mata Ahmad Mijin Aurene Jay kuma na rage lokaci da neman suna domin ita dai bataji a jikinta Jay auran Afeeyah zeyi har yanzu ba duk kuwa da tarin ƙaunar da yake nuna mata akan haka har faɗa suka sakeyi ta dai rabu da ita tana kuma yi mata addu'a a matsayinta na ƙawarta.
Takanas taje gidan Anty Sauda tace mata nan zata fara kawo Jay kafin Umma ta sauka daga fushin da takeyi da ita tukunna se ta kaishi gidan.
"Yanzu kina ganin abinda kika zaɓawa kanki daidai ne Afeeyah?" Anty Sauda wadda Umma ta gaya mata duk abinda ya faru ta tambayeta.
"Haba Anty dan Allah wai ana aure dole ne? Naga kema zaɓi aka baki kika kawo wanda kike so me yasa ni ake nema a tauye mun haƙƙi?" Ta jefawa Anty Saudan tambaya. Seta girgiza kai kawai tace mata Allah ya kawo Jafar ɗin lafiya, bata wani jima ba ta koma gida dukda zaman gidan ba wani daɗi yake mata ba yanzu saboda yanda Umma ta canza mata. Daga ita har Baffa babu wanda ya mata zancen ganinbata koma makaranta bama se Yah Malam daya zo hutu ne yace ya ya ganta a gida tace se wani satin zata koma. Baffabe canza mata kamar Umma ba dan ze amsa gaisuwarta har ya sakata aikace aikace kamar yanda ya saba amma Umma ko gaiseta tayi da harara take amsa mata tti duk yanda zatayi Umman ta sakko amma abu yaci tura tasan dai fushin Umma akan Ahmad ne addu'a takeyi Allahya kawo Jafar wanda yace zuwa ɗaya zeyi kafin yayi na biyu za'a tambaya masa auranta dan ya matsu.
"Yah Ahmad ka dena sona wlh, yanzu ace zanzo gida amma babu wani murna ko ɗokin gani na daka sabayi kawai Allah ya kaimu shikenan abinda zaka ce?" Jafar ya dasawa Ahmad mita akan beyi murna daya ce masa zezo gida ba. Ahmad daya kwanta zazzaɓin malaria kamar yanda yayiwa Momy ƙarya amma gaskiyar abinda yake damunsa Love sickness ne. Tun ranar daya baro gidansu Fatiman damuwa ta saukar masa da ciwon kai da zazzaɓi me zafi amma haka yake bankar Anti Malaria da Momy tasa dole yaje asibiti aka rubuto masa.
"I told you bani da lafiya Jafar amma kana ta so se ka sakani magana"
"Ni ai bazanyi maka sannu ba saboda wannan ciwon kai ka ɗorawa kanka, let me ask you please, is this Fatima made of Gold or some sort of precious stone da tayi deserving wannan soyayyar da kakeyi mata?
Yah Ahmad me yake damunka? For heaven sake kana nema ka kashe kanka akan wata banzar mace? Is she the only living woman on earth? Ko dai asiri tayi maka? Oh na manta mayyace believe me ta cinye maka zuciya kuma wlh bata isa ba. Ko waye ubanta she must leave you, seta fita a rayuwanka let me come back first I'm going to deal with her personally, se ta gane bata da hankali wlh" ya ringa sababi kamar ze aro baki daman kuskure Ahmad yayi daya taso masa da maganar gashi yana neman ya sake ƙara masa ciwo.
"I love her, kuma banajin zan iya dena sonta idan da abinda zakayi kasa ta soni i will appreciate it more zaginta da kakeyi dan baka san abinda nake ji bane ba nidai idan kana sona da gaske just help me fight na samu Fatima" Ahmad ya faɗa. Jafar yayi shiruj irin wanda takaici ya gama tiƙewa kafin yace
"Indai haka ne ze sa ka yarda Ina sonka then I don't love you Yah Ahmad and i will never love you indai se naso wannan yarinyar ne ka cireni a jerin ƙannenka, i hate her, i hate her with all my life kuma ko Allah yasa ka aureta bazan taɓa shiga gidanka ba" yana gama magana ya kashe wayansa yanda Ahmad ya jishi yasan ba ƙaramin zafi ya ɗauka ba. Yayi murmushi, yasan rigimar Jafar na lokaci ne zuwa anjima ze sake kiransa kawai dai wannan ƙiyayyar da yakeyi mata me zafi ce ya rasa dalilinta, saboda shine kuma yanzu so yakeyi ya haƙura da ita ba shikenan ba.
****************
"Alhaji, ni tun kwanaki naji kana zancen Amadu ya samu mata ko? Ashe ma ya taɓa kaiwa Ummu ita, se jiya da muke magana Jafaru yace daya zo za'aje masa neman aure shine tace mun zancen ai taga budurwar Amadun ma ya ɗaukota daga makaranta suka biya gidanta wai ya karɓowa Aisha Leshi, wai a Zaria take makaranta, nace Yayan masu kuɗi suna zuwa wannan makarantar kuwa?"
Alhaji Audu na kurɓar baƙin shayi daya sha spices, Girkin Hajiya Rabi ne ita ta dafa masa tana kawowa Hajiya Bintan tazo ta kankane gurin dole ta fita ta bata guri dan har ta fara sakar mata maganganu tana ci mata zarafi shi kuma Gwankin na zaune shirim bece komai ba. Ya gama sauraron Hajiyar kafin yace
"Oh ya samu mata kenan da yake ke zaki nemo masa auran shiyasa ya fara sanar dake?"
"Shi wa? Ummu nace maka ni a suwa Amadu ze faɗamun ya samu Matar Aure Aisha ce ni kowa?" Ta faɗa tana wani taɓe baki. Alhaji ya sake zuba shayinsa yana sha yace
"Shi Ɗan naki nake magana"
"Wai Jafaru? Dama idan be gaya mun ba toh wa kake so yaje ya fara sanarwa ko yana da wata uwar ne bayan ni a duniya?"
"Aa bance ba, shi Ahmad ɗin dake ya ɗaukeni uba ai tun fara neman yarinyar da yakeyi ya sanar dani, kawai inda ya nemo auran ne be gama kwanta mun a rai ba shiyasa ma kika ga an kawo yanzu maganar bata tashi ba amma yafi shekara da sanar dani".
Har wani zullo tayi kamar zata kwanta a gabansa tace
"Ashe maganar ta daɗe? Daman Ummu tace anfi wata shida da zuwan nasu tun kafin lokacin bikin su Hafsatu to ashema ka sani toh naji kace gidan daya nemo auran ne beyi maka ba, da akwai matsala kenan?"
Da zuciya ɗaya yace mata
"Yar wani Bakanike ce yarinyar Malam Hafizu akace sunansa a Alfindiki yake, a binciken da na saka akayimun dai Mahaifin yarinyar nace bashi da matsala mutumin kirki ne toh amma ita yarinyarce surutu yayi yawa akan yanda Samari suke zuwa gurinta wannan yazo wannan ya tafi gashi a matsayin mahaifinta irin rayuwar da akace tanayi ta wadata ya zarce ace shi yakeyi mata, kinsan yaran yanzu, zakiga Iyaye suna iyakacin ƙoƙarinsu gurin tarbiyya amma idan sun fita se abinda hali yayi musamman masu tafiya karatu wasu garuruwan ba gaban Iyayen nasu ba to wannan yasa na dakata kuma shima Ahmad ɗin tun maganar farko da mukayi be sake tayar mun da zancen ba dukda dai ina da labarin suna tare haryanzu kuma ita kaɗai yake kulawa ta yuwu yana jira ta kammala makaranta ne tunda ance shekarar ƙarshe take".
"Kina nufin tsayin shekara uku da yaron nan yake bibiyarki yana wahalta miki duk ya tashi a banza yanzu zakice ba sonsa kikeyi ba?"
"Wlh Baffa ni ban taɓa cewa yayi mun abu ba, kuma ai ko kai kana hanashi amma se ya dage se yayi kuma ni ina gaya masa ya dena kawai shine baya ji"
Umma ta leƙo a fusace tace
"Dan ubanko dole yanzu kice bakya sonsa mana kuma bake kika saka ya ringa miki wahala ba, Kare ne shi da ze shekara uku saboda rashin zuciya yana tare dake kina nuna masa rashin So kuma yaci gaba da zama dake? Kin gama yaudarar sa kin ɓata masa lokaci saboda baki da mutunchi yanzu zakice bakya Son sa me yasa tun farko baki faɗawa Malam ɗin ba shi da kansa ya kirashi ya sallame shi se yanzu da koɗaɗɗiyar fuskarki zakicewa mutane ke daman bakya son sa to wlh baki isa ba" Umma ta shiga sababi harta manta darene ta muryarta a sama.
Baffa daya kasa magana tuntuni ya kalli Fatima yace ta wuce ɗaki, sum sum ta shige tana jin kamar an sauke mata wani nauyi daga kanta tunda har ta iya furtawa Baffa bata ra'ayin Ahmad tasan magana ta ƙare. A ɗaki Umma ta warwarewa Baffa komai game da zancen Yaron da Afeeyah take so wato Jay ɗan Ƙwallo.
"A ina suka haɗu?" Ya tambayi Umman, ta watsa hannu kafin tace
"Wai acan makarantarsu, Malam ka sanarwa Yaron nan kawai ya turo Iyayensa suzo a ɗaura musu aure kawai idan yaso ta mutu ƙarshen rashin Son Sa".
"Ba za'ayi haka ba, za'a bi komai a hankali, magita zata samu da yardar Allah" inji Baffa. Daren raba shi yayi yana sallah da addu'oi, ya kasance me yawan tsayuwar dare amma yau Umma tasan sallar tasa harda ta neman ɗauki gurin Allah kan wannan abin daya tunkaro shi. Baffa na Son Afeeyah, amma abu ɗaya da tayi imani dashi shine baze bi Son rai ya zubar da ƙimar sa ba shiyasa ya maida lamarin ga buwayin sarki gagara Misali wanda duk hukuncin daya yanke babu wanda ya isa yayi inkari akai.
Kwanaki uku Baffa ya jera yana Istikara cikin tareda tsananta Addu'a da roƙon ubangiji akan Al'amarin, Afeeyah kuwa rai fes dan Ahmad be sake kiranta ba tunda ya tafi kuma ta furta abinda yake ranta dan tasan Umma ta gayawa Baffa zancen Jay babban abinda ya sakat nishaɗi da farin ciki kuma shaida mata da Jay yayi yana tafe Nigeria nan da sati biyu masu zuwa. Saura kwana biyar su koma makaranta semester ƙarshe ce babu Lectures da yawa se aikin project da abinda baza'a rasa ba dan haka ta yanke ba zata koma bahar se yazo tukunna abinda bata taɓayi ba ƙarin hutu tunda ta fara University.
Ta gayawa Badar Jay yana tafe, Badar nason Jay da Afeeyah amma ba kamar yanda take sonta da Ahmad ba kamar yanda take ce mata Ahmad Mijin Aurene Jay kuma na rage lokaci da neman suna domin ita dai bataji a jikinta Jay auran Afeeyah zeyi har yanzu ba duk kuwa da tarin ƙaunar da yake nuna mata akan haka har faɗa suka sakeyi ta dai rabu da ita tana kuma yi mata addu'a a matsayinta na ƙawarta.
Takanas taje gidan Anty Sauda tace mata nan zata fara kawo Jay kafin Umma ta sauka daga fushin da takeyi da ita tukunna se ta kaishi gidan.
"Yanzu kina ganin abinda kika zaɓawa kanki daidai ne Afeeyah?" Anty Sauda wadda Umma ta gaya mata duk abinda ya faru ta tambayeta.
"Haba Anty dan Allah wai ana aure dole ne? Naga kema zaɓi aka baki kika kawo wanda kike so me yasa ni ake nema a tauye mun haƙƙi?" Ta jefawa Anty Saudan tambaya. Seta girgiza kai kawai tace mata Allah ya kawo Jafar ɗin lafiya, bata wani jima ba ta koma gida dukda zaman gidan ba wani daɗi yake mata ba yanzu saboda yanda Umma ta canza mata. Daga ita har Baffa babu wanda ya mata zancen ganinbata koma makaranta bama se Yah Malam daya zo hutu ne yace ya ya ganta a gida tace se wani satin zata koma. Baffabe canza mata kamar Umma ba dan ze amsa gaisuwarta har ya sakata aikace aikace kamar yanda ya saba amma Umma ko gaiseta tayi da harara take amsa mata tti duk yanda zatayi Umman ta sakko amma abu yaci tura tasan dai fushin Umma akan Ahmad ne addu'a takeyi Allahya kawo Jafar wanda yace zuwa ɗaya zeyi kafin yayi na biyu za'a tambaya masa auranta dan ya matsu.
"Yah Ahmad ka dena sona wlh, yanzu ace zanzo gida amma babu wani murna ko ɗokin gani na daka sabayi kawai Allah ya kaimu shikenan abinda zaka ce?" Jafar ya dasawa Ahmad mita akan beyi murna daya ce masa zezo gida ba. Ahmad daya kwanta zazzaɓin malaria kamar yanda yayiwa Momy ƙarya amma gaskiyar abinda yake damunsa Love sickness ne. Tun ranar daya baro gidansu Fatiman damuwa ta saukar masa da ciwon kai da zazzaɓi me zafi amma haka yake bankar Anti Malaria da Momy tasa dole yaje asibiti aka rubuto masa.
"I told you bani da lafiya Jafar amma kana ta so se ka sakani magana"
"Ni ai bazanyi maka sannu ba saboda wannan ciwon kai ka ɗorawa kanka, let me ask you please, is this Fatima made of Gold or some sort of precious stone da tayi deserving wannan soyayyar da kakeyi mata?
Yah Ahmad me yake damunka? For heaven sake kana nema ka kashe kanka akan wata banzar mace? Is she the only living woman on earth? Ko dai asiri tayi maka? Oh na manta mayyace believe me ta cinye maka zuciya kuma wlh bata isa ba. Ko waye ubanta she must leave you, seta fita a rayuwanka let me come back first I'm going to deal with her personally, se ta gane bata da hankali wlh" ya ringa sababi kamar ze aro baki daman kuskure Ahmad yayi daya taso masa da maganar gashi yana neman ya sake ƙara masa ciwo.
"I love her, kuma banajin zan iya dena sonta idan da abinda zakayi kasa ta soni i will appreciate it more zaginta da kakeyi dan baka san abinda nake ji bane ba nidai idan kana sona da gaske just help me fight na samu Fatima" Ahmad ya faɗa. Jafar yayi shiruj irin wanda takaici ya gama tiƙewa kafin yace
"Indai haka ne ze sa ka yarda Ina sonka then I don't love you Yah Ahmad and i will never love you indai se naso wannan yarinyar ne ka cireni a jerin ƙannenka, i hate her, i hate her with all my life kuma ko Allah yasa ka aureta bazan taɓa shiga gidanka ba" yana gama magana ya kashe wayansa yanda Ahmad ya jishi yasan ba ƙaramin zafi ya ɗauka ba. Yayi murmushi, yasan rigimar Jafar na lokaci ne zuwa anjima ze sake kiransa kawai dai wannan ƙiyayyar da yakeyi mata me zafi ce ya rasa dalilinta, saboda shine kuma yanzu so yakeyi ya haƙura da ita ba shikenan ba.
****************
"Alhaji, ni tun kwanaki naji kana zancen Amadu ya samu mata ko? Ashe ma ya taɓa kaiwa Ummu ita, se jiya da muke magana Jafaru yace daya zo za'aje masa neman aure shine tace mun zancen ai taga budurwar Amadun ma ya ɗaukota daga makaranta suka biya gidanta wai ya karɓowa Aisha Leshi, wai a Zaria take makaranta, nace Yayan masu kuɗi suna zuwa wannan makarantar kuwa?"
Alhaji Audu na kurɓar baƙin shayi daya sha spices, Girkin Hajiya Rabi ne ita ta dafa masa tana kawowa Hajiya Bintan tazo ta kankane gurin dole ta fita ta bata guri dan har ta fara sakar mata maganganu tana ci mata zarafi shi kuma Gwankin na zaune shirim bece komai ba. Ya gama sauraron Hajiyar kafin yace
"Oh ya samu mata kenan da yake ke zaki nemo masa auran shiyasa ya fara sanar dake?"
"Shi wa? Ummu nace maka ni a suwa Amadu ze faɗamun ya samu Matar Aure Aisha ce ni kowa?" Ta faɗa tana wani taɓe baki. Alhaji ya sake zuba shayinsa yana sha yace
"Shi Ɗan naki nake magana"
"Wai Jafaru? Dama idan be gaya mun ba toh wa kake so yaje ya fara sanarwa ko yana da wata uwar ne bayan ni a duniya?"
"Aa bance ba, shi Ahmad ɗin dake ya ɗaukeni uba ai tun fara neman yarinyar da yakeyi ya sanar dani, kawai inda ya nemo auran ne be gama kwanta mun a rai ba shiyasa ma kika ga an kawo yanzu maganar bata tashi ba amma yafi shekara da sanar dani".
Har wani zullo tayi kamar zata kwanta a gabansa tace
"Ashe maganar ta daɗe? Daman Ummu tace anfi wata shida da zuwan nasu tun kafin lokacin bikin su Hafsatu to ashema ka sani toh naji kace gidan daya nemo auran ne beyi maka ba, da akwai matsala kenan?"
Da zuciya ɗaya yace mata
"Yar wani Bakanike ce yarinyar Malam Hafizu akace sunansa a Alfindiki yake, a binciken da na saka akayimun dai Mahaifin yarinyar nace bashi da matsala mutumin kirki ne toh amma ita yarinyarce surutu yayi yawa akan yanda Samari suke zuwa gurinta wannan yazo wannan ya tafi gashi a matsayin mahaifinta irin rayuwar da akace tanayi ta wadata ya zarce ace shi yakeyi mata, kinsan yaran yanzu, zakiga Iyaye suna iyakacin ƙoƙarinsu gurin tarbiyya amma idan sun fita se abinda hali yayi musamman masu tafiya karatu wasu garuruwan ba gaban Iyayen nasu ba to wannan yasa na dakata kuma shima Ahmad ɗin tun maganar farko da mukayi be sake tayar mun da zancen ba dukda dai ina da labarin suna tare haryanzu kuma ita kaɗai yake kulawa ta yuwu yana jira ta kammala makaranta ne tunda ance shekarar ƙarshe take".