Sashe 12
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Har gabana ya fadi wlh na dauka gamo nayi" banza ya mata ya miqe ta sake cewa
"Aa, angwayene har aka iya miqewa da farar Asuba? Kaga bayan gudan namune ya fara alamun fadawa shiyasa naji tsoron karna shiga da duhu na rufta kafin a kawo mun agaji ma qila na nutse ina Amaryar, ta tashi ko se an kawo Agaji?"
Tsabar takaici harya tsaya ze bata amsar maganarta ta farko amma qarshen yasa ya wuce ba tareda ya ce mata komai ba, wai a kawo agaji ita dai tana tsufa amma se a hankali. Dakin ya koma lokacin Bara'atu ta fita daga ruwan data ji dadinsa sosai ta daura alwala tana tsaye tana tunanin yanda zatayi da ruwan ya shiga dakin. Kamar dazun ya sake juyewa a Bokiti ya dauraye ya fita dashi ya zubar can bakin rariya ya kife bahon qofar Dada tunda ya gama amfaninsa ya koma dakin, seda yayi Nafila kafin aka kira sallah dan haka ya dauki carbinsa ya fita daidai nan Yakubu ya fito daga bangarensa suka rankaya suka tafi masallacin duk su biyun babu me cewa komai suka zama kamar wasu surukai kowanne fuskar sa cike da annuri irin na sababbi Angwaye.
Bayan an Idar da sallah Abokanan su suka tare su da tsokana, nan suka zauna har gari yayi haske kafin suka doshi gida seda sukaje soro kuma suka tsaya saboda jiyo muryoyin mata alamar kowa ya tashi har an fara hidimar gida. Audu ya kalli Yakubu kamar tababbu suka fashe da dariya lokaci daya harda duqewa kowanne shiyasan dalilin dariyarsa. Yakubu ya kalli Audu yace
"Bazan iya shiga gidan nan ba kunya nakeji"
"Ai gara kai daka sha kunu ka wuce ka sakayo qofa shikenan ka gama abinda zakayi a ciki ka fice ni kuwa komai zanyi akan idon mutane" cewar Audu.
Shigowar Aminu ta sakasu shiga gidan dole yana ta tsokanarsu shima, a dakin Dada suka yada zango suka gaisheta kamar yanda suka saba, bakinta kamar ze yage saboda farin ciki, yau din wata ranace ta musamman a gurinta burinta ya cika na ganin Yakubu da Audu a matsayin magidanta sauran mata Autanta Baballiya da tasan ba lallai tayi tsahon ran da zataga wannan lokacin ba. Seda gari ya gama wayewa tangarau kafin kowanne ya koma dakinsa. Bara'atu na kishingide ya shiga ta miqe ya kalleta da murmushi yana cewa
"Aa yi kwanciyarki Jaruma"
Ta rufe fuska da Hijabin jikinta jin abinda yace wai jaruma, to jarumtar me tayi?"
Muryar Inna Hasiya dake magana ta sakashi fita ya dawo ya kwashi fulasan jiya ya kai mata ya tambayi Bara'atu Qaramin fulas din Shayi ko Jug ta nuna masa inda suke ya dauka ya fita ya kaiwa Innan daga can ya wuce dakin Shafi'u inda yayi ajiyar kaya.
Inna Hasiya tayi sallama Bara'atu ta amsa kafin ta shiga da fara'a Bara'atu ta miqe ta karbi kayan dake hannunta kafin ta duqa har qasa ta gaidata ta amsa tana tambayarta kwanan baqunta ita dai se murmushi take Innan tace mata
"Ga ruwan wanka can a kewaye kije kiyo se ki karya sannu ko" ta fada cikin tausasawa. Kan Bara'atu na qasa tace
"Toh Inna, amma Kwandon wankana yana bangaren Yaya Balaraba a can na barshi jiya"
Cikin jin dadin Yayar da ta kira Balaraba dashi Inna Hasiya ta fita da zummar karbo mata, a hasashe dai Hafastu tayi dacen surukai masu tarbiyya da kuma kunya. Seda ta dauki abin karin su Yakubu wanda Bilki ta ware kafin ta kai musu ta kuma karbowa Bara'atun kayan wankanta. A bandakin ta tarar da Ruwa har bokiti biyu, tayi wanka me kyau ta gasa jikinta dan ruwan da zafinsu kafin ta fito tana sunne kai dan Inna Hasiya da Bilki na tsakar gidan, dab da zata shiga daki Goggo Fadi ta taho tana cewa
"Aa Amarsu wanka akayi?"
Bara'atu ta durqushe tana gaisheta ta amsa fuska washe da fara'a, Inna Hasiya da fuskarta ta hade bayan fitowar Goggo Fadin tace
"Tashi maza kije ki shirya karki bushe".
A dakin bayan ta shafa mai ta ciro wata yaluwar Atamfa me ratsin fari dinkin Tazarce riga ta wuce guiwa an tsagata daga gefe gefe se zani ta saka. Ta bude qaramin kwandon da aka zuba mata kayan kwalliyarta. A qyalle ta zazzaga powder ta shafa ta dakko jagira tana niyyar zanawa se kuma ta dakata. Kwalliyar Balaraba ta jiya ta tuna, daga ita har qaqayenta da sukazo daga ruga babu wadda zakaga dambareriyar kwalliya a fuskarta hoda kawai suka saka se kwalli da man lebe kuma sunyi kyau kodan kasancewar su fararene oho?
Dukda cewar a ruga suke amma sun fita ita da nata qawayen wayewa ta ta'allaqa hakan da cewar garinsu Wailari yafi nasu kusada Birni har wasu daga cikinsu sukan kai tallar Nono cikin Kano qila a can suke gano kwalliya irin ta matan Birni wanda daman Audu yana kwatanta mata sam baya son wannan Jagira dasu jambakin da suke cike fuska dashi amma ita a ganinta idan ba tayi haka ba ba kwalliya tayi ba.
Zuciyarta ta shawarta mata ta gwada simple kwalliya irin ta Balaraban dan haka ta ajiye jagirar, brush ta dauka ta taje girarta da take a cike me kyakykyawan yanayi kamar an zanata fitina take sakata dambara baqin jagira akai ta qarawa fuskarta da bata haske baqi. Bayan ta taje girar ta saka kwalli a dara daran idonta, bazata iya haqura da jambaki ba dan haka ta shafa kadan ta kawo man lebe me kyalli da Audu ya sako mata a kayan fitar biki ta dora akai ita da kanta ta ringa sakin murmushi ganin yanda tayi kyau, fuskarta har qyalli take cike da Annuri irin na Amare. Ta mayar da kayan kwalliyar ta feshe jikinta da turare kafin ta ware dankwari bayan ta gyara zaman ribbon din data tufke jelar Shukun da aka mata. Daurin Maryam Babangida tayi wannan kam gwance ita a gurin kashe dauri, ta ringa juyi a gaban Kwabarta me mudubi daga sama har qasa tana dariyar yarinta dan tayiwa kanta kyau Addu'a take Audu ya shigo ya ganta taji me zece.
Motsin qofa yasa ta nutsu ta shiga neman farin gyalen data fitar tareda kayan. Audu ya shigo da sallama hannunsa riqe da Baqar leda babba kana gani kasan gwangwanaye ne a ciki ya kalli Bara'atu fuskarsa ta sake washewa zuciyarsa tacika da alfaharin kasancewar ta mallakinsa ita kuwa se sunne kai take na kunya. Ya kalli kayan karin da aka ajiye musu alamar bata ci ba yace
"Kar abincin ya huce kizo kici" a kunyace ta zauna qasa, ya fitar da gwangwanin Madara Peak dana milo se sukarime iyali kwali biyu ya ajiye mata ya juya da ragowar yana cewa
"Bari na kaiwa su Yakubu".
Kicibus sukayi da Bilki, ta miqo masa Babban farantin silba da aka dora kwanukan samira guda biyu se ledoji farare da aka qullo Madara, Milo da sugar tace
"Gashi farfesun Inna tace nata ne ita kadai ta ci ta shanye romon" ta fada cike da shaqiyanci tana kallon Bara'atun, ta dago kuwa ta maka mata harara, idon Audu ne yasa bata bata amsa ba tunda su din qawayene daman sun saba da caccakar juna. Audu ya karbi Farantin ya ajiye ya kwashe kayan shayin cikin ledar wanda yasan cikin manyan gwana gwanan da yake siyowa Dada duk sanda ze zo aka debo yace
"Maida su na taho mana da namu mantasu nayi dakin Shafi'i"
"Toh Yaya" Bilkin ta karba ta cigaba da tsayuwa dan so take ya fita ta tsokani qawar tata, karantarta yasa yace mata
"Muje toh" ba yanda ta iya ta fita amma dai ze fita ya barsu a gidan yau kam Bara'atu ta banu a gurinta dan dalilin daya sakata kwana a gidan kenan ma.
Tare suka karya da Bara'atun dukda yanda take ta noqewa bayan sun gama ya miqe yana cewa
"Zanje dakin Shafi'i nayi wanka, idan kina buqatar wani abu ki aiko yara su gaya mun"
"A dawo lafiya" ta fada tana miqewa itama bayan ta hada kwanukan da sukaci abinci dasu suka fito a tare bayan ta saka takalmi. Gurin da taga an tara wanke wanke ta ajiye na hannunta Audu kuma ya fita daidai nan Balaraba itama ta fito da nasu kwanukan tasha kwalliya kamar dai Bara'atun, suka sakarwa juna murmushi ta ajiye kayan hannunta kafin suka shiga gaisawa. Dakin Dada suka nufa tare suka tarar suma sun gama karyawa kenan Bilki na tattare guri Baballiya na kwance kamar gawar sababi yana tabara ko kunya bayaji waishi Auta.
Inna Hasiya ta dana masa duka tana cewa
"Dallah tashi ka basu guri su zauna", Dada da bakinta yaqi rufuwa se sannu take musu suka zauna kowacce na sunne kai suka shiga gaishe su. A mutunce suka amsa, tamkar ba surukai ba haka Dadan ta ringa jansu da hira suna amsa mata daddaya cike da kunya Inna Hasiya ta fice tsakar gida se Bilki dake tsokanarsu Dada tana tare musu.
"Kuje ki rakasu su gaida Goggonku" Dadan ta fadawa Bilki, ta miqe suka bi bayanta suna fita ta dafa Bara'atu tana cewa
"Qawata ya kikaji Auran?"
Inna Hasiya ta rafka salati tana cewa
"Kin banu Bilki wannan fitsara har ina sirrin Yayan naki kike kiji kome? To bari Audun yazo daidai yake dake".
Bilki ta ringa dariya su Bara'atu dai se murmushi da haka suka qarasa dakin Goggo Fadi sun tarar da ita da Aminu wanda tun Asuba daya shigo gidan yana can kome suke tattaunawa se Allah. Cike da girmamawa suka gaidata ta amsa itama basu jima ba suka basu guri, bayan sun fito Bara'atu ta kalli Balaraba tace
"Muje kiga dakina nima" suka rankaya Bilki ta wuce gurin Inna Hasiya data kirata. A dakin Balaraba ta ringa santin kayan Bara'atu, hira suka shiga tabawa Bilki ta dawo nan ta tasasu gaba da tsokana suka ringa hira gwanin dadi kafin qawayen Bara'atu suka fara zuwa yan kwadayin ragowar kazar Amarya.
"Aa, angwayene har aka iya miqewa da farar Asuba? Kaga bayan gudan namune ya fara alamun fadawa shiyasa naji tsoron karna shiga da duhu na rufta kafin a kawo mun agaji ma qila na nutse ina Amaryar, ta tashi ko se an kawo Agaji?"
Tsabar takaici harya tsaya ze bata amsar maganarta ta farko amma qarshen yasa ya wuce ba tareda ya ce mata komai ba, wai a kawo agaji ita dai tana tsufa amma se a hankali. Dakin ya koma lokacin Bara'atu ta fita daga ruwan data ji dadinsa sosai ta daura alwala tana tsaye tana tunanin yanda zatayi da ruwan ya shiga dakin. Kamar dazun ya sake juyewa a Bokiti ya dauraye ya fita dashi ya zubar can bakin rariya ya kife bahon qofar Dada tunda ya gama amfaninsa ya koma dakin, seda yayi Nafila kafin aka kira sallah dan haka ya dauki carbinsa ya fita daidai nan Yakubu ya fito daga bangarensa suka rankaya suka tafi masallacin duk su biyun babu me cewa komai suka zama kamar wasu surukai kowanne fuskar sa cike da annuri irin na sababbi Angwaye.
Bayan an Idar da sallah Abokanan su suka tare su da tsokana, nan suka zauna har gari yayi haske kafin suka doshi gida seda sukaje soro kuma suka tsaya saboda jiyo muryoyin mata alamar kowa ya tashi har an fara hidimar gida. Audu ya kalli Yakubu kamar tababbu suka fashe da dariya lokaci daya harda duqewa kowanne shiyasan dalilin dariyarsa. Yakubu ya kalli Audu yace
"Bazan iya shiga gidan nan ba kunya nakeji"
"Ai gara kai daka sha kunu ka wuce ka sakayo qofa shikenan ka gama abinda zakayi a ciki ka fice ni kuwa komai zanyi akan idon mutane" cewar Audu.
Shigowar Aminu ta sakasu shiga gidan dole yana ta tsokanarsu shima, a dakin Dada suka yada zango suka gaisheta kamar yanda suka saba, bakinta kamar ze yage saboda farin ciki, yau din wata ranace ta musamman a gurinta burinta ya cika na ganin Yakubu da Audu a matsayin magidanta sauran mata Autanta Baballiya da tasan ba lallai tayi tsahon ran da zataga wannan lokacin ba. Seda gari ya gama wayewa tangarau kafin kowanne ya koma dakinsa. Bara'atu na kishingide ya shiga ta miqe ya kalleta da murmushi yana cewa
"Aa yi kwanciyarki Jaruma"
Ta rufe fuska da Hijabin jikinta jin abinda yace wai jaruma, to jarumtar me tayi?"
Muryar Inna Hasiya dake magana ta sakashi fita ya dawo ya kwashi fulasan jiya ya kai mata ya tambayi Bara'atu Qaramin fulas din Shayi ko Jug ta nuna masa inda suke ya dauka ya fita ya kaiwa Innan daga can ya wuce dakin Shafi'u inda yayi ajiyar kaya.
Inna Hasiya tayi sallama Bara'atu ta amsa kafin ta shiga da fara'a Bara'atu ta miqe ta karbi kayan dake hannunta kafin ta duqa har qasa ta gaidata ta amsa tana tambayarta kwanan baqunta ita dai se murmushi take Innan tace mata
"Ga ruwan wanka can a kewaye kije kiyo se ki karya sannu ko" ta fada cikin tausasawa. Kan Bara'atu na qasa tace
"Toh Inna, amma Kwandon wankana yana bangaren Yaya Balaraba a can na barshi jiya"
Cikin jin dadin Yayar da ta kira Balaraba dashi Inna Hasiya ta fita da zummar karbo mata, a hasashe dai Hafastu tayi dacen surukai masu tarbiyya da kuma kunya. Seda ta dauki abin karin su Yakubu wanda Bilki ta ware kafin ta kai musu ta kuma karbowa Bara'atun kayan wankanta. A bandakin ta tarar da Ruwa har bokiti biyu, tayi wanka me kyau ta gasa jikinta dan ruwan da zafinsu kafin ta fito tana sunne kai dan Inna Hasiya da Bilki na tsakar gidan, dab da zata shiga daki Goggo Fadi ta taho tana cewa
"Aa Amarsu wanka akayi?"
Bara'atu ta durqushe tana gaisheta ta amsa fuska washe da fara'a, Inna Hasiya da fuskarta ta hade bayan fitowar Goggo Fadin tace
"Tashi maza kije ki shirya karki bushe".
A dakin bayan ta shafa mai ta ciro wata yaluwar Atamfa me ratsin fari dinkin Tazarce riga ta wuce guiwa an tsagata daga gefe gefe se zani ta saka. Ta bude qaramin kwandon da aka zuba mata kayan kwalliyarta. A qyalle ta zazzaga powder ta shafa ta dakko jagira tana niyyar zanawa se kuma ta dakata. Kwalliyar Balaraba ta jiya ta tuna, daga ita har qaqayenta da sukazo daga ruga babu wadda zakaga dambareriyar kwalliya a fuskarta hoda kawai suka saka se kwalli da man lebe kuma sunyi kyau kodan kasancewar su fararene oho?
Dukda cewar a ruga suke amma sun fita ita da nata qawayen wayewa ta ta'allaqa hakan da cewar garinsu Wailari yafi nasu kusada Birni har wasu daga cikinsu sukan kai tallar Nono cikin Kano qila a can suke gano kwalliya irin ta matan Birni wanda daman Audu yana kwatanta mata sam baya son wannan Jagira dasu jambakin da suke cike fuska dashi amma ita a ganinta idan ba tayi haka ba ba kwalliya tayi ba.
Zuciyarta ta shawarta mata ta gwada simple kwalliya irin ta Balaraban dan haka ta ajiye jagirar, brush ta dauka ta taje girarta da take a cike me kyakykyawan yanayi kamar an zanata fitina take sakata dambara baqin jagira akai ta qarawa fuskarta da bata haske baqi. Bayan ta taje girar ta saka kwalli a dara daran idonta, bazata iya haqura da jambaki ba dan haka ta shafa kadan ta kawo man lebe me kyalli da Audu ya sako mata a kayan fitar biki ta dora akai ita da kanta ta ringa sakin murmushi ganin yanda tayi kyau, fuskarta har qyalli take cike da Annuri irin na Amare. Ta mayar da kayan kwalliyar ta feshe jikinta da turare kafin ta ware dankwari bayan ta gyara zaman ribbon din data tufke jelar Shukun da aka mata. Daurin Maryam Babangida tayi wannan kam gwance ita a gurin kashe dauri, ta ringa juyi a gaban Kwabarta me mudubi daga sama har qasa tana dariyar yarinta dan tayiwa kanta kyau Addu'a take Audu ya shigo ya ganta taji me zece.
Motsin qofa yasa ta nutsu ta shiga neman farin gyalen data fitar tareda kayan. Audu ya shigo da sallama hannunsa riqe da Baqar leda babba kana gani kasan gwangwanaye ne a ciki ya kalli Bara'atu fuskarsa ta sake washewa zuciyarsa tacika da alfaharin kasancewar ta mallakinsa ita kuwa se sunne kai take na kunya. Ya kalli kayan karin da aka ajiye musu alamar bata ci ba yace
"Kar abincin ya huce kizo kici" a kunyace ta zauna qasa, ya fitar da gwangwanin Madara Peak dana milo se sukarime iyali kwali biyu ya ajiye mata ya juya da ragowar yana cewa
"Bari na kaiwa su Yakubu".
Kicibus sukayi da Bilki, ta miqo masa Babban farantin silba da aka dora kwanukan samira guda biyu se ledoji farare da aka qullo Madara, Milo da sugar tace
"Gashi farfesun Inna tace nata ne ita kadai ta ci ta shanye romon" ta fada cike da shaqiyanci tana kallon Bara'atun, ta dago kuwa ta maka mata harara, idon Audu ne yasa bata bata amsa ba tunda su din qawayene daman sun saba da caccakar juna. Audu ya karbi Farantin ya ajiye ya kwashe kayan shayin cikin ledar wanda yasan cikin manyan gwana gwanan da yake siyowa Dada duk sanda ze zo aka debo yace
"Maida su na taho mana da namu mantasu nayi dakin Shafi'i"
"Toh Yaya" Bilkin ta karba ta cigaba da tsayuwa dan so take ya fita ta tsokani qawar tata, karantarta yasa yace mata
"Muje toh" ba yanda ta iya ta fita amma dai ze fita ya barsu a gidan yau kam Bara'atu ta banu a gurinta dan dalilin daya sakata kwana a gidan kenan ma.
Tare suka karya da Bara'atun dukda yanda take ta noqewa bayan sun gama ya miqe yana cewa
"Zanje dakin Shafi'i nayi wanka, idan kina buqatar wani abu ki aiko yara su gaya mun"
"A dawo lafiya" ta fada tana miqewa itama bayan ta hada kwanukan da sukaci abinci dasu suka fito a tare bayan ta saka takalmi. Gurin da taga an tara wanke wanke ta ajiye na hannunta Audu kuma ya fita daidai nan Balaraba itama ta fito da nasu kwanukan tasha kwalliya kamar dai Bara'atun, suka sakarwa juna murmushi ta ajiye kayan hannunta kafin suka shiga gaisawa. Dakin Dada suka nufa tare suka tarar suma sun gama karyawa kenan Bilki na tattare guri Baballiya na kwance kamar gawar sababi yana tabara ko kunya bayaji waishi Auta.
Inna Hasiya ta dana masa duka tana cewa
"Dallah tashi ka basu guri su zauna", Dada da bakinta yaqi rufuwa se sannu take musu suka zauna kowacce na sunne kai suka shiga gaishe su. A mutunce suka amsa, tamkar ba surukai ba haka Dadan ta ringa jansu da hira suna amsa mata daddaya cike da kunya Inna Hasiya ta fice tsakar gida se Bilki dake tsokanarsu Dada tana tare musu.
"Kuje ki rakasu su gaida Goggonku" Dadan ta fadawa Bilki, ta miqe suka bi bayanta suna fita ta dafa Bara'atu tana cewa
"Qawata ya kikaji Auran?"
Inna Hasiya ta rafka salati tana cewa
"Kin banu Bilki wannan fitsara har ina sirrin Yayan naki kike kiji kome? To bari Audun yazo daidai yake dake".
Bilki ta ringa dariya su Bara'atu dai se murmushi da haka suka qarasa dakin Goggo Fadi sun tarar da ita da Aminu wanda tun Asuba daya shigo gidan yana can kome suke tattaunawa se Allah. Cike da girmamawa suka gaidata ta amsa itama basu jima ba suka basu guri, bayan sun fito Bara'atu ta kalli Balaraba tace
"Muje kiga dakina nima" suka rankaya Bilki ta wuce gurin Inna Hasiya data kirata. A dakin Balaraba ta ringa santin kayan Bara'atu, hira suka shiga tabawa Bilki ta dawo nan ta tasasu gaba da tsokana suka ringa hira gwanin dadi kafin qawayen Bara'atu suka fara zuwa yan kwadayin ragowar kazar Amarya.