← Book details Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 131 OF 137

Sashe 131

Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Se ranar Laraba Ahmad ya kaiwa Fatima Ɗinkakkun kaya, Atamfa me kyau da akayiwa ɗinkin zamani amma Modest ɗinki se wani shegen Lace da Anty Sauda tace ya haura dubu ɗari biyu. Kowanne kaya da mahaɗinsa, Takalmi, mayafi, jaka harda Sarƙa da agogo. Zobunan gold guda biyu ya saka mata a ciki ganinsu ya tuna mata da ranar da yace ta nuna masa hannunta kenan measurement ɗin hannun ya ɗauka. Yace mata Atamfar ta Ankon Kamun ce dan ya gaya mata zasuyi biki har Iv ya tura mata Lace kuma kawai ɗinka mata yayi na Dinner.

Tace ba zataje ba Umma ta goya mata baya a cewarta babu tsayayyar magana a tsakaninsu da har zata saka taje musu biki, idan kuma zuwan nata ya janyo wani abu da ba za'a so ba fa? Gara dai da ace anyi magana yan uwansa sun san da zamanta da sauƙi ko cikin yan uwa tana iya samun wata suje tare su dawo. Baffa ma da aka gaya masa cewa yayi Aa. Da kansa ya kira Ahmad yace ba zataje ba, yayi kuma faɗan zobuna har biyu da Umma tace masa zinare ne yace in yazo ya karɓe su ya ajiye idanAllahyasa taje gidansa ya bata ya dai amsa da Toh amma koshi Baffan yasan baze karɓa ba dan yasha ya kawo mata abu yace a mayar yaƙi karɓa sedai ya kalallameshi da magana yace ko babu soyayya tsakaninsu Baffa Babansa ne zeyi mata komai saboda shi. Wannan ya rushe batun zuwanta Biki wanda daman ko da an barta a karan kanta ba zata so taje ba, to wai se taje a matsayinta nawa???

An dai yi biki a gidan Alhajin Bechi lafiya duk kalen bala'in Hajia da yan korarta dole suka kama kansu domin Yan uwan Momy da ƙawayenta wannan karon basu zo da wasa ba. Yanda Hajiyar ta saba musu idan ana biki ba yarta ba amma komai yana hannu ta se abinda tace se yanda ta tsara za'ayi wannan karon basu bari ba. Basu saurari Alhajin ba kansa Ahmad da Sarki sun share mata hawayen komai domin duk halinsa shima wannan karon Ahmad ya shawo kansa sun fitarda mahaifiyarsu kunya ba tareda sunyi jiran kowa ba. Anyi biki lafiya Amare sun tare Hafsatu an tafi Abuja Aslamiyyah na nan Kano se Amaryar Yakubu shima da Allah yayi bana yayi auran tsalle tsalle ya ƙare dukda seda Alhajin yayi masa barazana da ze saukeshi daga Acting Account General dan har yanzu ba'ayi confirming nasa ba kafin ya kawo matar akayi Bikin.

Afeeyah kuwa Rikicewa ta ringayi harta fara zaton WhatsApp ɗinta ya samu matsala saboda status ɗin Ahmad da Jay da suka zama iri ɗaya tunda aka fara bikin har aka gama seta yi tunanin repeating sukeyi taga kamar ana Jay dan komai ma gizon sunansa yake mata yanzu. Ko kusa bata kawo cewar Jay ze iya haɗa wata alaƙa da Ahamd ba shiyasa ma bata tsawaita tunani ko bincike ba ganin kuma komai ya koma normal shikenan ta manta. Ada bata fiya wani duba status ba amma haɗuwarta da Jay kusan kullum seta duba update ɗinsa wanda duk akanta yakeyi. Yace mata yaso yazo Nigeria abinda ya hanashi zuwa contract ɗinsa da Arsenal taje ƙarshe, Clubs da yawa suna zawarcinsa har yanzu kuma beyi finalizing inda ze koma ba yana so se yayi sealing deal ɗin kafin yaje wani guri. Ya tura maata da sabon Field name ɗinsa, a maimakon JAY its going to be AJAY. Yace A for AFEEYAH and JAY remain for the JAFAR bata yarda da gaske yake ba har se ranar da yayi sealing deal da PSG sabuwar rigarsa da AJAY aka bugata.

Ta ringa murmushi kamar wawiya sanda take kallon Interview ɗinsa, an tambayeshi me yasa ya canza suna kuma me A take nufi yace it remains secret lokacin da ze bayyana yana zuwa. Tana jin Yah Malam ɗinsu da Abokinsa Sani da tsabar yanda yake son Jay sunansa ya koma Jay ranar sunata magana. Ance Initial ɗin budurwarsa ne, wasu sunce Initial ɗin Yayansa ne da yake bala'in so kowa dai da abinda yake faɗi. Kamar taje ta gaya musu gaskiya se kuma ta kama bakinta. Anty Sauda tayiwa Umma zancen itama bata bada goyon baya na cewa ma tayi karsu bari Baffa yaji dan ranta ne ze ɓaci. Ya za'ayi tsayin lokacin nan ta dawo tace wani daban ba Ahmad ba itama tasan wasa takeyi. A ranta ko babu gudu babu ja da baya tasan kuma Baffa baze taɓa bin ta tasu ba ya aura mata abinda bata so. Ai da bakinta bata taɓa cewa wani tana son Ahmad ba ko zata aureshi su suke kiɗansu suna rawarsu dan haka babu wata hujja da za'a kafa da zata rabata da wanda take so, badai yace ya kusa zuwa Nigeria ba yana zuwa zata kaishi gidan ayita ta ƙare da haka suka cinye hutun session daya ritsa da Strike kusan watansu uku a gidan kafin suka koma School First semester Four hundred level.
*Assalamu alaikum*
*Ina matan suke, Manyan mata yan kwalisa da suka amsa sunansu na Mata ba muna mata ba Kawayen Binta gumama?*

*SODAH GENERAL ENTERPRISES ce tazo da kanta ba aike ba tana kuma shaida mutu da cewar zafafan kaya sun sauka, kamar yanda kuka sani tana kawo muku suturu na sakawa kama daga kan Atamfa, Laces da dangoginsu*

*Wannan karon ta sake taho muku da tsarabar Supplements ingantattu wato Original bawai copy ba. Ku sani bayan abinci jiki yana da buqatar qarin wasu sinadarai da zasu taimakawa ginuwar jikin da lafiyar kowanne bangare na jikin, SODAH ENTERPRISES tana da General Supplements ma'ana wanda suke tattare da Vitamins da dukkan jiki yake buqata sannan tana da special supplements wanda HQ wato gidan mutunchi yake buqata domin sake tsare qima.*

*Ina wadda take fama da skin nata yaqi dadin azanci? Fata ta bushe tayi dabbara dabbara ta shafa mai duk a banza se qara lalacewa tayi? To maza ki leqa gurin SODAH ENTERPRISES domin tana da sabulu me kyau da inganci me gyara fata tayi kyau ta goge tayi sulbi baya saka Fari asalin kalarki ze sake fiddo miki ya kuna goge duk wasu tabo ko rashes da suke hanaki walwala, sabulunta babu chemical ba kuma na bleaching bane yawwa karki tsammaci da zakiyi haske Aa sedai glowing kalarki ta ainihi ze fitarda.*

*A tuntubeta kai tsaye akan 08137145294*
*Ko ki danna wannan link kai tsaye domin magana da ita*
https://wa.link/wwvjr3
*Location Kano, tana Nation wide delivery*

*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*

*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*

*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*

*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*

*BOOK 2*
*PAGE 16*

Rayuwa ta shuɗa, soyayyar Afeeyah da Jay tana ƙara ƙarfi inda al'amarinta tsakaninta da Ahmad yake sake taɓaɓarewa. Zywa yanzu ya gama tabbatarwa Fatima bata ta tashi da gaske wani ya masa shigar sauri kuma ya sure Imaninta. Ya sake tsananta Addu'a akan Al'amarin amma mainakon rangwame se sake jinta yakeyi a zuciyarsa kamar ture. Damuwar da yake ciki da ayyuka da suka masa yawa yasa duk ya sake figewa ya fita a hayyacinsa. Kowa a gidan yaro da babba ya shaida Ahmad yana da damuwa hatta Hajiya kuwa seda ranar ta tsare shi tace

"Kai Amadu anya magauta basu danneka ba? Wannan uwar rama haka kamar wanda ake ɗiba ayi miya kullum? Koda yake jarabar neman kuɗi daka saka a ranka ai dole kaƙi abin kirki, ni na rasa ma me kake nema ko kuwa so kake se ka yi gasa da ƙaninka ne? Shidai kasan yan guje guje kawai zeyi a fili ya dirim Miliyoyi sun shiga akawun, shiyasa yake mulla ƙibarsa kai kuwa kana ta fama da dogon wuya kamar tsohon raƙumi takwaran ubanka". A Ƙofar ɗakinta take maganar ga Hajiya bata rage Volume dan haka hatta Momy dake cikin falonta suna magana da Baba Bilki sun jiyota. Baba Bilki ta girgiza kai tace

"Yau rashin mutunchin Binta ya motsa kenan, daɗina da ita bata bar kowa ba, kinji Mijinku ne takwaran tsohon raƙumi. Amma fa maganar gaskiya ki matsa Babana ya gaya miki me yake damunsa da gaske wannan ramar tasa tayi yawa, ni dana tambayesa yace wai aiki ne amma kuma wane aiki ne haka damuwarsa zata nuna har a fuskar mutum? Amadi da ko yaushe fuskarsa take a washe ga barkwanci amma yanzu se a wuni baka ga murmushinsa ba gaskiya ya kamata kiji damuwar yaron nan idan kuma naje Bechi daman zan karɓo masa taimako dan dole mahassada suyi masa caaa irin wannan buɗi da ubangiji yayi masa kiga komai yaro ya taɓa se ya zama kuɗi".

Tana rufe baki ya shiga falon da sallama ƙasa ƙasa, suka bishi da kallo harya zauna kusada ƙafafun Momyn. Murmushin yaƙe yayi ganin yanda suka zuba masa ido yace
"Lafiya dai Innata da Momy kuke kallona haka kamar kunga baƙo?" Inna yake kiran Baba Bilkin Jafar ma ya kama saɓanin sauran da Manyan suce mata Hajiya ragowar Baba.

"Ai dole mu kalleka Ahmad, kana duban kanka a Mirror kuwa? Wannan ƙasumbar da gashin daka tara a kanka na magani da menene?" Momy ta tambaya tana dafa kan nasa. Ya shafa gashin shima yace
"Lokaci ne ban samu naje aski ba amma yanzu idan na fita zanyi"
"Gara dai kayi ko ka koma hayyacinka amma fuska gashi biya biya kuma ba'a kintse ba ai babu kyau" Baba Bilki data miƙe ta sake faɗa yayi murmushi yana tambayarta fita zatayi tace masa Bechi zata tafi kwana biyu bataje ba sati zatayi kafin ta dawo.

"Da bana komai ai da na kaiki"
"Aa yi zamanka, tare zamu tafi da Yaya Yakubu ai can gidan nasa ma zan tafi yanzu"
"Toh Allah ya kiyaye hanya ki gaidasu" sukayi mata bankwana. Bayan fitarta Momy ta fuskance shi dakyau tace
"Karka boyemun komai ka faɗamun gaskiyar abinda yake damunka Ahmad".
Chapter 131 · 0% Book details