Sashe 75
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sanda takardar ta shiga hannun Bara'atu ji tayi kamar an mata bushara da gidan Aljanna, da Ajami ya rubuta dan haka ta gane komai abu daya daya dameta a ciki shine cewar da yayi karta tafi masa da Da ko daya, ta yaya zata barwa Binta yaranta? Matar data tsaneta kuma zata iyayin komai akanta da yaranta.
"Karki sakawa ranki damuwa akan yara babu abinda ze same su sannan kina nan a matsayinki na mahaifiyarsu babu abinda ze goge hakan komai daren dadewa kuma zasu nemeki. Ki fuskanci rayuwarki ta gaba, ki tashi kinemi ilimi ki tsaya da qafafunki in sha Allahu ubangiji zeyi miki sakayya a gaba da Mafi Alkhairi kinji" Yakubu ya tausheta.
A ranar suka tafi Bechi gaba daya dan dama can zasuyi sallah. Shiya kaita har gidansu ya kuma yiwa Inna Hajara bayanin komai, bayan tafiyarsa kuwa wuta ce kadai Inna Hajara bata hura ta jefa Bara'atu a ciki ba, ta kasa hango rayuwar da yarta take ciki da ta sa ta haqura da daular da ita hange, damuwarta kadai mutane zasuyi mata dariya, zasu rasa tallafin da suke samu a gurin Audun tunda ya kwace Yayansa, ita da take saka ran idan Bara'atun ta sauke farali Bana badi kuma a sakata a lissafi shine tayi mata baqin ciki shin Bara'atu wace irin yarinya ce ne? An gaya mata da akwai Auran da ake jin dadi dari bisa dari ne a ciki? Wace Macece zata samu Miji kamar Audu daula iya daula tayi wasa da damarta ai se sakarya irin Bara'atun gashi yanzu Auran ya mutu murus babu damar gyarawa.
An cinye watan Shawwal Mahajjata suka fara shirye shiryen tafiya qasa me tsarki, Audu ya rigada ya biyawa Bara'atu, Bilki da Aminu se Balaraba matar Yakubu, a hannun Aminun ya damqa duk wani abu daya kamata na Bara'atun, babu wanda beyi mamaki ba dukda sun san da ita cikin jerin matafiyan amma abinda ya faru yasa suka dauka za'a fasa tafiyar da ita sedai Audun ya basu mamaki. Lokacin tafiya yayi suka shirya sunyi bankwana da yan uwa da Abokanan Arziqi, dalilin su Bilki da Aminu ya saka Audu yi musu rakiya Iyafot dukda qasan ransa badansu yaje ba, haka nan zuciyarsa ta kasa nutsuwa a kwanakin, kullum ya kwanta se yayi mafarkin Bara'atun haka da rana wuni yake da tunaninta a ransa yana jin kamar ta cancanci ya nemi afuwarta koda har yanzun be yarda da cewar ya cutarda ita ba kamar yanda mutane suke fada amma kuma haka nan zuciyarsa take ingizashi ga neman afuwar da besan ta mecece yake da buqata ba.
A iyafot Mahajjata sun hau layin karban tikitin shiga jirgi, yana daga tsaye can gefe dan ya sake zama baqo a cikin danginsa tun da ya rabu da Bara'atu ya sake rasa karsashin sakewa musamman a gaban Yakubu yanzun ma ganinsa tsaye suna sallama da matarsa yasa duk ya kasa sakewa gashi yana so yayi magana da Bara'atu amma shegiyar zuciyarsa me masa hudubar tsiya tana gaya masa girmansa ze zube idan aka ga ya mata magana a nan gurin.
"Be kamatu na tafi muna riqe da juna a zuciya ba, ina roqon da ka yafe mun idanna maka wani laifi a zaman da mukayi da kai, daga bangarena na yafe maka, iyakar wannan Alkhairin da kayi mun ka zama silar da zan ziyarci ma'aiki ya wanke duk wani laifi naka da yake cikin zuciyata sannan idan ka koma gida ka gayawa Matarka in har taji tsoron Allah ta gaya maka gaskiya ta wankeni daga zargin data saka mutane sukemun na kisan kai na yafe mata idan ba haka ba idan harna mutu ko ita ta rigani mutuwa tabbas shari'armu sedai a qarqareta a gaban Allah dan bazan yafe ba bayan raina a ringa aibata Yayana ana jifansu da abinda ban aikata ba" Bara'atu da be san sanda ta dawo gurin ba ta fada tana kuma gama maganar ta koma cikin Ayari tana daga masa hannu, kamar wanda aka matsawa Remote haka shima ya shiga daga mata hannun, zuciyarsa ta ringa tsinkewa wata faduwar gaba da besan dalilinta ba ta saukar masa haka ya tuqa motarsa ya koma gida yana maimaita zancenta na matarsa ta wanketa daga zargin data dora mata.
A karon farko ya tambayi Binta gaskiyar abinda ya faru? Ya akayi tasan Bara'atu ce ta kashe mata Da? Bintan dake cike fam da tafiyar Bara'atun tayi tsaki kawai ta tashi ta bashi guri. Bara'atun nema take ta zame mata qajaga, ta tunkudeta amma ba zata bar zuciyarta ta huta ba kenan? Abu daya ke sanyaya mata rai idan ta tuna aure ya qare tsakaninta da Audu duk Bala'i dole su haqura sannan ga Yayanta nan zube a tsakar gida suna watangaririya iya rabata dasu da tayi tasan zuciyarta ta quntata, jira takeyi Tagwayen Zubaida su shekara biyu suma tasa ya karbo su subi sahun yan uwansu domin tasha Alwashin babu wata mace da zata mori Audu bayan ita, yaya dai da suka haifa sun samu sedai su jira idan ya mutu su yafici abinda suka samu amma badai a yanzu da yake raye ba.
An kammala aikin Hajji lafiya Mahajjata nata lissafin kwanakin daya rage musu su dawo gida haka nan yan gida nata shirye shiryen tarbar yan uwansu, kwanaki biyu ya rage Jirgin su Bara'atu ya sauka, a daren ranar da zasu tafi Jidda inda daga can za'a maido su Nigeria suna shirye shirye dan sun gama daure kayansu cikinta ya fara murdawa, kamar wasa tun tana jinsa kadan kadan har ta kai ga ta kasa zama cikin abinda be gaza Minti talatin ba da fara ciwon cikin rai yayi halinsa Bara'atu ta amsa kiran Mahaliccinta. Mutuwarta ta girgiza yan tawagarsu gaba daya bama su Bilki kadai ba.
Wata mata ce take fadin
"Dazu take cemun tun da muka hau jirgi tayi addu'a idan har ta kammala aikin Hajjinta lafiya kuma ibadarta ta karbu tana fatan ubangiji ya karbi ranta a binneta a qasar Ma'aiki tace tsoro takeji anya kuwa tayi Hajjinta daidai ashe lokaci yana tafe ubangiji ya karbi shahadarki Bara'atu Yarinyar kirki yarinyavme haquri Annabi yasan da zuwanki" haka akayi jana'izar Bara'atu da Asuba a masallacin Harami aka binneta a maqabartar da ba kowa yake samun wannan Alfarma ba se me tsananin rabo shikenan rayuwar ta qare ta tafi ta bar Binta a duniyar da take ganin ba zata qare ba.
Dawoqar Mahajjata a maimakon murna se Al'amari ya juye na koke koke da Jimami, duk wanda yaji mutuwar Bara'atu seya girgiza hatta da Binta da da take ganin idan aka bata wuqa zata iya dabawa Bara'atun se gashi sanda labarin mutuwarta ya rsketa zuciyarta seda ta tsinke ta kuma girgiza.
Munira qanwar Binta da tazo Kano tun Bayan qaramar sallah dalilin takurar da Mama take mata akan ta fitarda Miji bayan kamar wadda aka sakawa hannu Sauro be taba tsaida ita ba bare yaje gidansu da sunan zance shiyasa ta tattaro ta taho gurin Bintan saboda ta samu sauqi kuma qila ta samu Mijin a nan sanda taji zancen mutuwar Bara'atun kuka ta fasa ta dora hannu tana tumami
"Mun shiga uku Yaya Binta matar nan ta mutu bamu nemi yafiyarta ba wlh inaga haqqintane ya kamamu gashi naqi Auruwa Anty Sakina haka siddan aka koreta daga gurin aiki duk irin hanyar Dady da mutanen daya sani ta kasa samun wani aikin ga Mijinta ibtila'in daya fada masa daman da aikin nata suke lallabawa da tallafin da Dady yake bata to ta rasa aikin ita kanta Yaya Salima cikin garari take masifar yau daban ta gobe daban gashi yanzu ta mutu balle mu roqeta ta yafe mana qazafin da muka mata shikenan haka rayuwarmu zata qare a balbalce ni kenan bazan taba yin aure na na shiga uku na lalace wayyo ni Munira kaicona dana biyewa shedan muka laqabawa Baiwar Allah sharrin kisan rai bata ji ba bata gani ba" magana take cikin ihu da kururuwa wanda mutanen da suke tsakar gida Yan Bechi da sukazo tarar su Bilki duk sun Jita, Audu na kan Baranda dan jiri ne yake neman kadashi tun sanda labarin mutuwar ya riskeshi shiyasa ya zauna a gurin ana masa fifita se ga wata sabuwa yana jiyowa daga dakin Binta.
*PROMO PROMO PROMO*
*Nace kina da Labarin MOMMY MOROCCO ME KAYAN MATA KUWA?* *Ko kuwa dai kina nan zaune baki wangale kina fama da masu niqa Kuka da Citta ko su qulla miki Garin Masara da sunan Magani*? *To ki karkade kunnenki Yar uwa ki kuma maza ki dauraye qafarkin nan da tayi furu furu domin MOMMY MOROCCO Ta diro Nigeria kuma tafe take da Abin Arziqi Niqi Niqi*
*Ina mai farin cikin shaida muku Moommy Morocco zatayi BONANZAr kayanta na kwana biyu*.
*Tazo muku da zafafan magungun wanda ya taba amfani dasu ne kadai ze baki labari Ingantattun magunguna na gani na fada ajin farko wanda aka hadasu cikin tsari da kula daga Ganyayyaki da kayan abincinmu masu qara lafiyar jiki da saukarwa Mace Ni'imar da take buqata kayanta babu Algus babu abinda ze cutar dake da yardar Allah*
*1-Da akwai hadin First ladies exclusive VIP package*
*2-Qafarka qafata package*
*3-Kankat package*
*4-Da kuma Mini package*
*Tazo muku da gangariyar maganin SANYI sadidan na Jiki dana Mara wanda In sha Allaahu ba ke ba sanyi kuma za a iya ba wa Yara, Maza ma suna sha*
*Bata tsaya iya nan ba tazo da Turarukan ta na ban mamaki se wanda ya gwada ze bada labari, Kedai kada ki bari de wannan damar ta wuceki domin ta zabtare Farashin kayanta har zuwa kaso 50% discount! Kyaso wannan gara basa ta wuce ki kuwa Indai ba Bintan Audu kike ba* 🥴🥴
*A tuntubeta a WhatsApp:09086233009*
*Ko kiran waya a 08029988065*
*Siyan Nagari Maida kudi gida*
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*PAGE 29*
"Karki sakawa ranki damuwa akan yara babu abinda ze same su sannan kina nan a matsayinki na mahaifiyarsu babu abinda ze goge hakan komai daren dadewa kuma zasu nemeki. Ki fuskanci rayuwarki ta gaba, ki tashi kinemi ilimi ki tsaya da qafafunki in sha Allahu ubangiji zeyi miki sakayya a gaba da Mafi Alkhairi kinji" Yakubu ya tausheta.
A ranar suka tafi Bechi gaba daya dan dama can zasuyi sallah. Shiya kaita har gidansu ya kuma yiwa Inna Hajara bayanin komai, bayan tafiyarsa kuwa wuta ce kadai Inna Hajara bata hura ta jefa Bara'atu a ciki ba, ta kasa hango rayuwar da yarta take ciki da ta sa ta haqura da daular da ita hange, damuwarta kadai mutane zasuyi mata dariya, zasu rasa tallafin da suke samu a gurin Audun tunda ya kwace Yayansa, ita da take saka ran idan Bara'atun ta sauke farali Bana badi kuma a sakata a lissafi shine tayi mata baqin ciki shin Bara'atu wace irin yarinya ce ne? An gaya mata da akwai Auran da ake jin dadi dari bisa dari ne a ciki? Wace Macece zata samu Miji kamar Audu daula iya daula tayi wasa da damarta ai se sakarya irin Bara'atun gashi yanzu Auran ya mutu murus babu damar gyarawa.
An cinye watan Shawwal Mahajjata suka fara shirye shiryen tafiya qasa me tsarki, Audu ya rigada ya biyawa Bara'atu, Bilki da Aminu se Balaraba matar Yakubu, a hannun Aminun ya damqa duk wani abu daya kamata na Bara'atun, babu wanda beyi mamaki ba dukda sun san da ita cikin jerin matafiyan amma abinda ya faru yasa suka dauka za'a fasa tafiyar da ita sedai Audun ya basu mamaki. Lokacin tafiya yayi suka shirya sunyi bankwana da yan uwa da Abokanan Arziqi, dalilin su Bilki da Aminu ya saka Audu yi musu rakiya Iyafot dukda qasan ransa badansu yaje ba, haka nan zuciyarsa ta kasa nutsuwa a kwanakin, kullum ya kwanta se yayi mafarkin Bara'atun haka da rana wuni yake da tunaninta a ransa yana jin kamar ta cancanci ya nemi afuwarta koda har yanzun be yarda da cewar ya cutarda ita ba kamar yanda mutane suke fada amma kuma haka nan zuciyarsa take ingizashi ga neman afuwar da besan ta mecece yake da buqata ba.
A iyafot Mahajjata sun hau layin karban tikitin shiga jirgi, yana daga tsaye can gefe dan ya sake zama baqo a cikin danginsa tun da ya rabu da Bara'atu ya sake rasa karsashin sakewa musamman a gaban Yakubu yanzun ma ganinsa tsaye suna sallama da matarsa yasa duk ya kasa sakewa gashi yana so yayi magana da Bara'atu amma shegiyar zuciyarsa me masa hudubar tsiya tana gaya masa girmansa ze zube idan aka ga ya mata magana a nan gurin.
"Be kamatu na tafi muna riqe da juna a zuciya ba, ina roqon da ka yafe mun idanna maka wani laifi a zaman da mukayi da kai, daga bangarena na yafe maka, iyakar wannan Alkhairin da kayi mun ka zama silar da zan ziyarci ma'aiki ya wanke duk wani laifi naka da yake cikin zuciyata sannan idan ka koma gida ka gayawa Matarka in har taji tsoron Allah ta gaya maka gaskiya ta wankeni daga zargin data saka mutane sukemun na kisan kai na yafe mata idan ba haka ba idan harna mutu ko ita ta rigani mutuwa tabbas shari'armu sedai a qarqareta a gaban Allah dan bazan yafe ba bayan raina a ringa aibata Yayana ana jifansu da abinda ban aikata ba" Bara'atu da be san sanda ta dawo gurin ba ta fada tana kuma gama maganar ta koma cikin Ayari tana daga masa hannu, kamar wanda aka matsawa Remote haka shima ya shiga daga mata hannun, zuciyarsa ta ringa tsinkewa wata faduwar gaba da besan dalilinta ba ta saukar masa haka ya tuqa motarsa ya koma gida yana maimaita zancenta na matarsa ta wanketa daga zargin data dora mata.
A karon farko ya tambayi Binta gaskiyar abinda ya faru? Ya akayi tasan Bara'atu ce ta kashe mata Da? Bintan dake cike fam da tafiyar Bara'atun tayi tsaki kawai ta tashi ta bashi guri. Bara'atun nema take ta zame mata qajaga, ta tunkudeta amma ba zata bar zuciyarta ta huta ba kenan? Abu daya ke sanyaya mata rai idan ta tuna aure ya qare tsakaninta da Audu duk Bala'i dole su haqura sannan ga Yayanta nan zube a tsakar gida suna watangaririya iya rabata dasu da tayi tasan zuciyarta ta quntata, jira takeyi Tagwayen Zubaida su shekara biyu suma tasa ya karbo su subi sahun yan uwansu domin tasha Alwashin babu wata mace da zata mori Audu bayan ita, yaya dai da suka haifa sun samu sedai su jira idan ya mutu su yafici abinda suka samu amma badai a yanzu da yake raye ba.
An kammala aikin Hajji lafiya Mahajjata nata lissafin kwanakin daya rage musu su dawo gida haka nan yan gida nata shirye shiryen tarbar yan uwansu, kwanaki biyu ya rage Jirgin su Bara'atu ya sauka, a daren ranar da zasu tafi Jidda inda daga can za'a maido su Nigeria suna shirye shirye dan sun gama daure kayansu cikinta ya fara murdawa, kamar wasa tun tana jinsa kadan kadan har ta kai ga ta kasa zama cikin abinda be gaza Minti talatin ba da fara ciwon cikin rai yayi halinsa Bara'atu ta amsa kiran Mahaliccinta. Mutuwarta ta girgiza yan tawagarsu gaba daya bama su Bilki kadai ba.
Wata mata ce take fadin
"Dazu take cemun tun da muka hau jirgi tayi addu'a idan har ta kammala aikin Hajjinta lafiya kuma ibadarta ta karbu tana fatan ubangiji ya karbi ranta a binneta a qasar Ma'aiki tace tsoro takeji anya kuwa tayi Hajjinta daidai ashe lokaci yana tafe ubangiji ya karbi shahadarki Bara'atu Yarinyar kirki yarinyavme haquri Annabi yasan da zuwanki" haka akayi jana'izar Bara'atu da Asuba a masallacin Harami aka binneta a maqabartar da ba kowa yake samun wannan Alfarma ba se me tsananin rabo shikenan rayuwar ta qare ta tafi ta bar Binta a duniyar da take ganin ba zata qare ba.
Dawoqar Mahajjata a maimakon murna se Al'amari ya juye na koke koke da Jimami, duk wanda yaji mutuwar Bara'atu seya girgiza hatta da Binta da da take ganin idan aka bata wuqa zata iya dabawa Bara'atun se gashi sanda labarin mutuwarta ya rsketa zuciyarta seda ta tsinke ta kuma girgiza.
Munira qanwar Binta da tazo Kano tun Bayan qaramar sallah dalilin takurar da Mama take mata akan ta fitarda Miji bayan kamar wadda aka sakawa hannu Sauro be taba tsaida ita ba bare yaje gidansu da sunan zance shiyasa ta tattaro ta taho gurin Bintan saboda ta samu sauqi kuma qila ta samu Mijin a nan sanda taji zancen mutuwar Bara'atun kuka ta fasa ta dora hannu tana tumami
"Mun shiga uku Yaya Binta matar nan ta mutu bamu nemi yafiyarta ba wlh inaga haqqintane ya kamamu gashi naqi Auruwa Anty Sakina haka siddan aka koreta daga gurin aiki duk irin hanyar Dady da mutanen daya sani ta kasa samun wani aikin ga Mijinta ibtila'in daya fada masa daman da aikin nata suke lallabawa da tallafin da Dady yake bata to ta rasa aikin ita kanta Yaya Salima cikin garari take masifar yau daban ta gobe daban gashi yanzu ta mutu balle mu roqeta ta yafe mana qazafin da muka mata shikenan haka rayuwarmu zata qare a balbalce ni kenan bazan taba yin aure na na shiga uku na lalace wayyo ni Munira kaicona dana biyewa shedan muka laqabawa Baiwar Allah sharrin kisan rai bata ji ba bata gani ba" magana take cikin ihu da kururuwa wanda mutanen da suke tsakar gida Yan Bechi da sukazo tarar su Bilki duk sun Jita, Audu na kan Baranda dan jiri ne yake neman kadashi tun sanda labarin mutuwar ya riskeshi shiyasa ya zauna a gurin ana masa fifita se ga wata sabuwa yana jiyowa daga dakin Binta.
*PROMO PROMO PROMO*
*Nace kina da Labarin MOMMY MOROCCO ME KAYAN MATA KUWA?* *Ko kuwa dai kina nan zaune baki wangale kina fama da masu niqa Kuka da Citta ko su qulla miki Garin Masara da sunan Magani*? *To ki karkade kunnenki Yar uwa ki kuma maza ki dauraye qafarkin nan da tayi furu furu domin MOMMY MOROCCO Ta diro Nigeria kuma tafe take da Abin Arziqi Niqi Niqi*
*Ina mai farin cikin shaida muku Moommy Morocco zatayi BONANZAr kayanta na kwana biyu*.
*Tazo muku da zafafan magungun wanda ya taba amfani dasu ne kadai ze baki labari Ingantattun magunguna na gani na fada ajin farko wanda aka hadasu cikin tsari da kula daga Ganyayyaki da kayan abincinmu masu qara lafiyar jiki da saukarwa Mace Ni'imar da take buqata kayanta babu Algus babu abinda ze cutar dake da yardar Allah*
*1-Da akwai hadin First ladies exclusive VIP package*
*2-Qafarka qafata package*
*3-Kankat package*
*4-Da kuma Mini package*
*Tazo muku da gangariyar maganin SANYI sadidan na Jiki dana Mara wanda In sha Allaahu ba ke ba sanyi kuma za a iya ba wa Yara, Maza ma suna sha*
*Bata tsaya iya nan ba tazo da Turarukan ta na ban mamaki se wanda ya gwada ze bada labari, Kedai kada ki bari de wannan damar ta wuceki domin ta zabtare Farashin kayanta har zuwa kaso 50% discount! Kyaso wannan gara basa ta wuce ki kuwa Indai ba Bintan Audu kike ba* 🥴🥴
*A tuntubeta a WhatsApp:09086233009*
*Ko kiran waya a 08029988065*
*Siyan Nagari Maida kudi gida*
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*PAGE 29*