Sashe 17
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Audu yayi murmushi yana cewa
"Ayya lamarin qarfen nasara babu tabbas, ku jira bari na shiga cikin gari sena kawo muku Man yanzu indai shine matsalar" yana fadar haka ya juya cikin sassarfa ya tsallake titi ya koma inda su Shamsu suke jiransa. Su ukun suka hau Mashin din suka koma cikin gari. Hankalin mutumin da Driver sa ya tashi, karfa gayya zeje yayo azo ayi musu wani abun? Suka kalli juna kowanne kana iya karantar firgici a fuskarsa, ga mota taqi tashi idan sukace su kwasa da gudu kan suje ko ina su Audun zasu iya cimmasu gaba daya nadamar zuwa Taron daya kawo shi Kano ta kamashi, yana zaman zamansa qungiyarsu ta masu lasisin haqar man futur ta shirya musu taro a Kano kamar baze zo ba ashe Ajaline ya kirashi. Jiki a sabule ya shige motar ya zauna ya hada kai da kujera danya gama saddaqarwa yau kam tasa ta qare, qarar mashin dayaji tasa shi dagowa a firgice sedai ganin Audu tareda Shamsu daya rungumo Qatuwar jarka ga bututu da tiyo a hannunsa yasa shi sakin ajiyar zuciya babu shiri zufar dake keto masa ta fara qafewa har iska na fifitashi.
Fitowa yayi daga motar lokacin har Audu ya bude jarkar yana jiran Direba ya bude gida man a zuba musu shi kuma yana kallon ubangidansa cikin jiran umarni, kai ya gyada masa alamar bada dama ya bude musu, seda ya cika musu tanki taf da mai kafin ya rufe jarkarda dan ragoqar daya rage ciki yana kallon Direban yace
"To ka kunna mu gani"
Direba ya kunna mota se gashi kuwa ta tashi, fuskar Alhajin ta sake washewa yana kallon Audu yace
"Amma a ina ka samo Fetur haka?"
"Ina siyarwa ne anan cikin garinmu" ya bashi amsa. Alhaji ya zura hannu a Aljihu ya zaro kudaden da besan yawansu ba ya miqawa Audu yana cewa
"Nagode kwarai samari"
"Aa ka bar kudinka Alhaji kyaiuta na baku"
"Amma kace siyarwa kakeyi" Alhajin ya fada yana sake miqa masa kudin. Audu yayi murmushi yace
"Eh siyarwa nakeyi amma ku kyautana baku, da zan karbi kudinka tun farko zance maka ina siyarwa ka fadi na nawa za'a zuba maka"
Alhaji ya gyada kai cike da gamsuwa har sannan fuskarsa dauke da murmushi yace
"Hakane, nagode kwarai, yanda ka kaimakeni kaima Allah ya kawo maka wanda zero taimake ka a lokacin da bakayi tsammani ba" suka amsa da Amin. Ya sake saka hannu a Aljihu ya ciro wani dan kati me kyau ya miqawa Audu yace
"Ga katina, idan ka samu dama ka nemeni kaji, Nagode kwarai dagaske Allah ya saka"
Audu ya karbi katin da aka rubuta 'ZAKARIYYA PAKI AND SONS' ya jefa a Aljihu daga nan Alhaji ya shiga mota yana daga musu hannu har suka bar gurin.
Audu da Shamsu suka hau mashin Shamsun nata mita akan me Audu be karbi kudinba yace shi taimakonsu yayi saboda Allah kuma iya addu'ar da yayi masa ma ta ishe shi.
Yanayin garin lokacin sanyi ne dan haka Dada nata fama da mura me zafi wadda daman tanayinta duk sanyi har da daukewar numfashi wani lokacin take samu tun su Audu na qanana haka suka tashi sukaga tana shan wahalar nan duk sanyi shiyasa ya siya mata manyan fulasan ajiye ruwa sannan sanyi na shigowa zasu cire labule me saukin da yake a jikin qofa a saka mata jibgege haka dakin baya rabo da rushi amma dukda haka data fita tsakar gida ta shaqi hazo da sanyi haka zatayita haki tana jan numfashi. Maganin gargajiya take sha tuntuni wannan karon kuma tun zuwan Audu yake fama da ita akan suje Asibiti dan zamansa a Kano yasan cutar Asthma, akwai qanin Hayatu Magashi da yake da ita kuma duk yanayin ciwon nasa haka Dadar take fama sedai taqi yarda suje Asibi balle a dorata akan magani tace tafi gane na gargajiyar da take sha tun tana yarinyarta.
To wannan karon ciwon nata yadan ta'azzara dan dalilin daya hanashi komawa Kano kenan kusan satinsa biyu a Bechi se jikin yayi sauqi se kuma ya dawo. A daren ranar ma kwana sukayi zaune saboda yanda ta kasa bacci tana jan numfashi dakyar tun bayan data dafawa su Bara'atu makani hayaqin Karan datayi girkin dashi ya cika mata qirji shikenan numfashi ya fara sama sama washe gari kuwa da sassafe Audu ya kwasheta duk yanda take tirjewa seda sukaje Asibiti. An mata Allura an kuma rubuta mata magunguna ya siya bayan dokoki da sharuddan da likita ya kafa mata akan ta kiyaye duk wani abu daze hadata da qura ko hayaqi suka dawo gida. Wunin ranar zur a dakinta yayi shi haka qannensu da matansu duk suna nan suna hidima da Dadan da gaba daya tayi wani laushi dukda tace taji dadin Allura da maganin data sha abinda take ji a qirjinta ya yaye amma jikinta babu qarfi dama kuma likitan ya gaya musu magungunan akwai me kashe jiki yasa bacci dan haka Audu yace ta kwanta ta huta.
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH*
*HALIN KISHI*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 400 (PROMO PRICE BAYAN KAMMALA FREE PAGES ZE KOMA 500) A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*NAGODE*
*FREE PAGE 8*
Goggo Fadi ta ringa sakin maganganu a tsakar gida wai Lamarin Dada dai ta rasa ma abinda zatace akai wannan rashin kunya har ina ta ringa hawa mashin Yara na goyata sannan danbata da lafiya kamar wata jinjira ta langwabe duk se wani zuruftu yara suke akanta, lokacin da take maganar Dada ta fito Aisha ta rakata kewaye ta fito tana daura Alwala. Seda ta idar ta kalli Goggo Fadin da murmushi tace
"Yaya kenan, indai nice kin kusa ki dena ganina ballantana nayi abinda ze sakaki surutu".
Goggo Fadi ta ce
"Eh ba shakka Hafsatu wato daman naji ance zakuyi qaura Birni yo ni ai haka nake so ku tattara ku tafi ku barmin gidana yanda kuka zo kuka sameni, bari ma wannan yaron yazo kuyiwa gurin naku kudi kawai ya fiddaku shikenan wanda ya hada ya raba"
Har Dadata zura qafarta a daki ta sake waiwayawa tana murmushin da seda gaban Goggo Fadi ya yanke ya fadi haka kawai tace
"Toh ai Malam ba sauri yayi ba Fadi, zan bishi kema kuma komai dadewa zaki biyo bayanmu" daga nan ta shige dakinta tabar Goggo Fadin na sababi ita kadai.
Da dare Audu ya kawo mata Kaza gasashshiya da Madara sabuwar tatsa dan gama tafasata kenan ya karbo ko hucewa batayi ba. Dada na cin naman Baballiya na gefenta yana so yaci Audu ya hanashi Abdullahi daman tuni ya gudu gurin Bara'atu tunda yaga Audun ya shigo da ledoji kuma har Goggo Fadi seda ya miqawa. Dada taci ta qoshi ta turawa Baballiya tana cewa
"Ci ubana kaji haka kawai yabi ya takuramun kai"
"Wlh Dada ke kike dada sangarta yaron nan ya girma amma baze dena sakarci ba a haka kake cewa zakaje aikin Sojan" Audu ya fada, Dada ta kishingide tana sakace tace
"Ze dena ne, aikin Soja kuma nasan indai kana raye seka cika masa burinsa kamar yanda ka dakko hanyar cika na dan uwanka. Ina Alfahari dakai Abdulwahabu ina kuma roqon Allah yaci gaba da hada kanku ya baka ikon ji gaba da jajaircewa akan zumunchinku, ina fatan har yaya da jikoki kuci gaba da hada kanku karku yarda qata baraka ta shiga tsakanin ku, Banida haufi domin kunyo dacen mata na kwarai saboda rayuwar Namiji komai nagartarsa idan yayi kuskuren dace da macen aure anan yake samun tawaya dan haka ina horar ku cewar ko gaba koda ace kunyi sha'awar qara aure kuyi qoqari gurin zabo matar da zata tayaku kuci gaba da hada kan gidanku ba wadda zata tarwatsa muku farin cikin da kuka ginu akai ba. Sannan yan uwanku kuci gaba da haquri dasu kuna jan su a jiki da sannu wata rana zaku koma tamkar baya sanda Malam yana raye".
Haka ta ringa masu nasiha me shige da wasiyya, Baballiya na gama cin kazarsa ya sheme a gurin ita da Audu sukaci gaba da yar hira har ta fara gyangyadi kafin ta hau gadonta yaja mata abin rufa bayan ya shafa mata man zafi a tafin qafarta ta saka safa. Seda ya zubo toka me zafi a babban kaskon da ake ajiyewa a dakin yayi masa mazauni me kyau saboda gudun tsautsayi kafin ya tashi Baballiya ya gyara kwanciyarsa yaja musu qofar ya fita jikinsa a sanyaye saboda maganganun da Dada ta fada masa, yanda take nanata masa hadin kan Iyalinsa kamar wadda take hango wani abu a gaba haka ya shiga dakinsu Bara'atu har tayi bacci ya raba gefenta ya kwanta sedai be jima da kwanciya ba bugun qofar gida ya farkar dashi.
Da mamakin wayake musu bugu cikin dare ya dauki fitila ya fita, seda ya tambayi waye, muryar Yakubu dayaji ta sakashi bude qofar da sauri ya rabe ya shigo ganin yanda yake rawar Dari dan rigar jikinsa bata da nauyi haka nan kansa babu hula ga dare ya tsala dan haka gari yayi sanyi qarara. Yakubun na goye da Jakarsa medan girma kana kallonsa ko baa fada maka ba zaka san yasha wuyar tafiyar da yayiwo ya wuce ciki Audu yabi bayansa zuciyarsa na bugawa abinda ya fara zuwar masa Yakubun ya samu matsala da karatunsa ne. Yana so ya tambayeshi daga ina haka cikin dare ba kuma ya so hayaniyarsu ta tayar da Dada ko Goggo Fadi ta samu abin sharri dan haka yabi Yakubun daya doshi dakin Dada kai tsaya ya tura qofar ya shiga Audu yabi bayansa.
"Ayya lamarin qarfen nasara babu tabbas, ku jira bari na shiga cikin gari sena kawo muku Man yanzu indai shine matsalar" yana fadar haka ya juya cikin sassarfa ya tsallake titi ya koma inda su Shamsu suke jiransa. Su ukun suka hau Mashin din suka koma cikin gari. Hankalin mutumin da Driver sa ya tashi, karfa gayya zeje yayo azo ayi musu wani abun? Suka kalli juna kowanne kana iya karantar firgici a fuskarsa, ga mota taqi tashi idan sukace su kwasa da gudu kan suje ko ina su Audun zasu iya cimmasu gaba daya nadamar zuwa Taron daya kawo shi Kano ta kamashi, yana zaman zamansa qungiyarsu ta masu lasisin haqar man futur ta shirya musu taro a Kano kamar baze zo ba ashe Ajaline ya kirashi. Jiki a sabule ya shige motar ya zauna ya hada kai da kujera danya gama saddaqarwa yau kam tasa ta qare, qarar mashin dayaji tasa shi dagowa a firgice sedai ganin Audu tareda Shamsu daya rungumo Qatuwar jarka ga bututu da tiyo a hannunsa yasa shi sakin ajiyar zuciya babu shiri zufar dake keto masa ta fara qafewa har iska na fifitashi.
Fitowa yayi daga motar lokacin har Audu ya bude jarkar yana jiran Direba ya bude gida man a zuba musu shi kuma yana kallon ubangidansa cikin jiran umarni, kai ya gyada masa alamar bada dama ya bude musu, seda ya cika musu tanki taf da mai kafin ya rufe jarkarda dan ragoqar daya rage ciki yana kallon Direban yace
"To ka kunna mu gani"
Direba ya kunna mota se gashi kuwa ta tashi, fuskar Alhajin ta sake washewa yana kallon Audu yace
"Amma a ina ka samo Fetur haka?"
"Ina siyarwa ne anan cikin garinmu" ya bashi amsa. Alhaji ya zura hannu a Aljihu ya zaro kudaden da besan yawansu ba ya miqawa Audu yana cewa
"Nagode kwarai samari"
"Aa ka bar kudinka Alhaji kyaiuta na baku"
"Amma kace siyarwa kakeyi" Alhajin ya fada yana sake miqa masa kudin. Audu yayi murmushi yace
"Eh siyarwa nakeyi amma ku kyautana baku, da zan karbi kudinka tun farko zance maka ina siyarwa ka fadi na nawa za'a zuba maka"
Alhaji ya gyada kai cike da gamsuwa har sannan fuskarsa dauke da murmushi yace
"Hakane, nagode kwarai, yanda ka kaimakeni kaima Allah ya kawo maka wanda zero taimake ka a lokacin da bakayi tsammani ba" suka amsa da Amin. Ya sake saka hannu a Aljihu ya ciro wani dan kati me kyau ya miqawa Audu yace
"Ga katina, idan ka samu dama ka nemeni kaji, Nagode kwarai dagaske Allah ya saka"
Audu ya karbi katin da aka rubuta 'ZAKARIYYA PAKI AND SONS' ya jefa a Aljihu daga nan Alhaji ya shiga mota yana daga musu hannu har suka bar gurin.
Audu da Shamsu suka hau mashin Shamsun nata mita akan me Audu be karbi kudinba yace shi taimakonsu yayi saboda Allah kuma iya addu'ar da yayi masa ma ta ishe shi.
Yanayin garin lokacin sanyi ne dan haka Dada nata fama da mura me zafi wadda daman tanayinta duk sanyi har da daukewar numfashi wani lokacin take samu tun su Audu na qanana haka suka tashi sukaga tana shan wahalar nan duk sanyi shiyasa ya siya mata manyan fulasan ajiye ruwa sannan sanyi na shigowa zasu cire labule me saukin da yake a jikin qofa a saka mata jibgege haka dakin baya rabo da rushi amma dukda haka data fita tsakar gida ta shaqi hazo da sanyi haka zatayita haki tana jan numfashi. Maganin gargajiya take sha tuntuni wannan karon kuma tun zuwan Audu yake fama da ita akan suje Asibiti dan zamansa a Kano yasan cutar Asthma, akwai qanin Hayatu Magashi da yake da ita kuma duk yanayin ciwon nasa haka Dadar take fama sedai taqi yarda suje Asibi balle a dorata akan magani tace tafi gane na gargajiyar da take sha tun tana yarinyarta.
To wannan karon ciwon nata yadan ta'azzara dan dalilin daya hanashi komawa Kano kenan kusan satinsa biyu a Bechi se jikin yayi sauqi se kuma ya dawo. A daren ranar ma kwana sukayi zaune saboda yanda ta kasa bacci tana jan numfashi dakyar tun bayan data dafawa su Bara'atu makani hayaqin Karan datayi girkin dashi ya cika mata qirji shikenan numfashi ya fara sama sama washe gari kuwa da sassafe Audu ya kwasheta duk yanda take tirjewa seda sukaje Asibiti. An mata Allura an kuma rubuta mata magunguna ya siya bayan dokoki da sharuddan da likita ya kafa mata akan ta kiyaye duk wani abu daze hadata da qura ko hayaqi suka dawo gida. Wunin ranar zur a dakinta yayi shi haka qannensu da matansu duk suna nan suna hidima da Dadan da gaba daya tayi wani laushi dukda tace taji dadin Allura da maganin data sha abinda take ji a qirjinta ya yaye amma jikinta babu qarfi dama kuma likitan ya gaya musu magungunan akwai me kashe jiki yasa bacci dan haka Audu yace ta kwanta ta huta.
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*MARUBUCIYAR*
*WATA KISHIYAR*
*RUBUTACCIYAR QADDARAH*
*HALIN KISHI*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 400 (PROMO PRICE BAYAN KAMMALA FREE PAGES ZE KOMA 500) A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*NAGODE*
*FREE PAGE 8*
Goggo Fadi ta ringa sakin maganganu a tsakar gida wai Lamarin Dada dai ta rasa ma abinda zatace akai wannan rashin kunya har ina ta ringa hawa mashin Yara na goyata sannan danbata da lafiya kamar wata jinjira ta langwabe duk se wani zuruftu yara suke akanta, lokacin da take maganar Dada ta fito Aisha ta rakata kewaye ta fito tana daura Alwala. Seda ta idar ta kalli Goggo Fadin da murmushi tace
"Yaya kenan, indai nice kin kusa ki dena ganina ballantana nayi abinda ze sakaki surutu".
Goggo Fadi ta ce
"Eh ba shakka Hafsatu wato daman naji ance zakuyi qaura Birni yo ni ai haka nake so ku tattara ku tafi ku barmin gidana yanda kuka zo kuka sameni, bari ma wannan yaron yazo kuyiwa gurin naku kudi kawai ya fiddaku shikenan wanda ya hada ya raba"
Har Dadata zura qafarta a daki ta sake waiwayawa tana murmushin da seda gaban Goggo Fadi ya yanke ya fadi haka kawai tace
"Toh ai Malam ba sauri yayi ba Fadi, zan bishi kema kuma komai dadewa zaki biyo bayanmu" daga nan ta shige dakinta tabar Goggo Fadin na sababi ita kadai.
Da dare Audu ya kawo mata Kaza gasashshiya da Madara sabuwar tatsa dan gama tafasata kenan ya karbo ko hucewa batayi ba. Dada na cin naman Baballiya na gefenta yana so yaci Audu ya hanashi Abdullahi daman tuni ya gudu gurin Bara'atu tunda yaga Audun ya shigo da ledoji kuma har Goggo Fadi seda ya miqawa. Dada taci ta qoshi ta turawa Baballiya tana cewa
"Ci ubana kaji haka kawai yabi ya takuramun kai"
"Wlh Dada ke kike dada sangarta yaron nan ya girma amma baze dena sakarci ba a haka kake cewa zakaje aikin Sojan" Audu ya fada, Dada ta kishingide tana sakace tace
"Ze dena ne, aikin Soja kuma nasan indai kana raye seka cika masa burinsa kamar yanda ka dakko hanyar cika na dan uwanka. Ina Alfahari dakai Abdulwahabu ina kuma roqon Allah yaci gaba da hada kanku ya baka ikon ji gaba da jajaircewa akan zumunchinku, ina fatan har yaya da jikoki kuci gaba da hada kanku karku yarda qata baraka ta shiga tsakanin ku, Banida haufi domin kunyo dacen mata na kwarai saboda rayuwar Namiji komai nagartarsa idan yayi kuskuren dace da macen aure anan yake samun tawaya dan haka ina horar ku cewar ko gaba koda ace kunyi sha'awar qara aure kuyi qoqari gurin zabo matar da zata tayaku kuci gaba da hada kan gidanku ba wadda zata tarwatsa muku farin cikin da kuka ginu akai ba. Sannan yan uwanku kuci gaba da haquri dasu kuna jan su a jiki da sannu wata rana zaku koma tamkar baya sanda Malam yana raye".
Haka ta ringa masu nasiha me shige da wasiyya, Baballiya na gama cin kazarsa ya sheme a gurin ita da Audu sukaci gaba da yar hira har ta fara gyangyadi kafin ta hau gadonta yaja mata abin rufa bayan ya shafa mata man zafi a tafin qafarta ta saka safa. Seda ya zubo toka me zafi a babban kaskon da ake ajiyewa a dakin yayi masa mazauni me kyau saboda gudun tsautsayi kafin ya tashi Baballiya ya gyara kwanciyarsa yaja musu qofar ya fita jikinsa a sanyaye saboda maganganun da Dada ta fada masa, yanda take nanata masa hadin kan Iyalinsa kamar wadda take hango wani abu a gaba haka ya shiga dakinsu Bara'atu har tayi bacci ya raba gefenta ya kwanta sedai be jima da kwanciya ba bugun qofar gida ya farkar dashi.
Da mamakin wayake musu bugu cikin dare ya dauki fitila ya fita, seda ya tambayi waye, muryar Yakubu dayaji ta sakashi bude qofar da sauri ya rabe ya shigo ganin yanda yake rawar Dari dan rigar jikinsa bata da nauyi haka nan kansa babu hula ga dare ya tsala dan haka gari yayi sanyi qarara. Yakubun na goye da Jakarsa medan girma kana kallonsa ko baa fada maka ba zaka san yasha wuyar tafiyar da yayiwo ya wuce ciki Audu yabi bayansa zuciyarsa na bugawa abinda ya fara zuwar masa Yakubun ya samu matsala da karatunsa ne. Yana so ya tambayeshi daga ina haka cikin dare ba kuma ya so hayaniyarsu ta tayar da Dada ko Goggo Fadi ta samu abin sharri dan haka yabi Yakubun daya doshi dakin Dada kai tsaya ya tura qofar ya shiga Audu yabi bayansa.