Sashe 67
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Barka barka, baqi mukayi a gidan? Daga ina?" Lantana ta fada tana miqewa sanda su Bara'atu suka shigo da ubannin buhubhuna da suka lodo su kwalla da Samiru. Mairo ma tayi musu sannu da zuwa, ta gane Hadiza a zaman da tayi a gida dukda ta dan qara jiki amma kamanninta basu bace mata ba sannan kuma ga kamannin me gidan a fuskar Bilki hakan ya ankarar da ita cewar daga Bechi suke.
"Bismilla ku shiga tana ciki Hajiyar" ta fada musu bayan data gaidasu a mutunce, kafin suyi magana Lantana tayi tsugul tace
"Ban gane su shiga ba? Ke haka akeyi kawai daga ganin mutane kice su shigar mata daki kina ganinsu yarkace yarkace da wasu uban buhunhuna kamar yan gudun Hijira qilama mabarata masu neman mafaka ko kinga sun miki kalar qawayen Hajiya balle kice su shiga daki kai tsaye?"
"Hayaniyar me akeyi ne haka? Lantana keda su waye?" Binta da subadadin lantana ya farkar da ita ta fada tana leqowa ta tagar uwar dakanta dake cikin tsakar gidan. Tayi sak ganin Bilki wadda suna hada ido ta tamke fuska tam.
"Kune tafe cikin ranar nan? Sannunku da zuwa aiko be sanar mun kuna tafe ba ku shigo" ta fada iyakar dauriyarta a qoqarinta na janyo su a jiki da kirki kamar yanda Turai ta bata shawara Bilki kadai ta sani cikinsu ko kuma ta gane tunda tasan Hadiza sedai sanin babu abinda ze kawota gidan yasa bata ma kawo a ranta ta santa ba. Dankwalinta ta shiga nema dan ta fito falo ta jiyo Bilki na cewa
"Da yake zuwan namu ba naki bane shi yasa be gaya miki ba, bari mu shiga can mun gode da tayi" daga haka suka ja kayansu zuwa dakin Bara'atun. Bi ta tabi bayansu da harara tareda sakin tsaki kafin ta daure kanta ta fito ranta na suya. Tsabar isa da samun guri ne yasa zasu kwaso jiki rabe rabe suzo mata gida kuma be gaya mata ba ko kuwa shima besan zasu zo ba sannan wadannan uban kwanukan da suke tafe dasu na menene ko daga Kasuwa suke? Take tambayar kanta harta fito tsakar gidan Lantana na tsaye guiwa tayi sanyi saboda yanda taji Hajiyar ta musu magana ya nuna mata sudin ba banza bane kamar yanda ta tsammata.
"Ashe baqinki ne Hajiya" ta fada tana sosa kai, Binta ta wuceta tana cewa
"Qannen megidan ne"
Seko ta dafe qirji ta zare ido, amma data tuna suda banza a gun Binta duk daya se ta dan saki ranta sedai mamaki ya kamata da har Binta tayi musu tayin shiga dakinta, to shiri suka fara haka ko kuwa duk cikin wasan kwaiwayon data fara ne?
Binta kitchen din tsakar gidan ta shiga ta tarar da Mairo na kwashe Shinkafar data gama dafawa Miyar na kan wuta tana idasa soyuwa.
"Idan kin gama akai musu abinci kafin nan a hada ruwa da lemo idan da Alkaki ki hada musu" ta bata unarni ita kuma ta amsa da
"Toh Hajiya".
Dakin da suka shigan ta wuce, sun shimfida tabarma cikin kayan da sukazo dasu Mata biyu na zaune Bilki na tsaye taba duban dakin daya qara kyau dalilin sabon fenti da qofofi harda Abun sak kwan lantarki duk aka canza se gurin ya qara haske da kyau.
Daga bakin qofar ta tsaya ta aika musu gaisuwa rai babu dadi kamar an mata dole suka amsa banda Bilki data shige daya daga cikin dakunan gurin, Binta tayi kyacci a ranta tana ayyana yanda zataci kan uwarta kafin ta kalli yar dattijuwar da ta fisu shekaru Qanwar Inna Hajara ce tace
"Bari a kawo musu ruwa, bamu san da zuwanku ba ai da an muku shiri me kyau"
"Ba komai yar nan hakan ma mungode" matar ta fada a ranta tana mamakin rashin kirkin Bintan da ake fada ita dai bata gani ba.
"Munafuka" Bilki ta fada bayan ta juya, matar da ake kira da Inna Habi tace
"Kai Bilkisu, niko banga abinda kuke fada akan matar nan ba. Yanzu wace macece zata tari dangin kishiya sunzo danki haka?"
Mairo ta aje Try data doro su ruwa da Lemo da kayan tabawa, seda ta zabura jin maganar Inna Habin ta kalli Bilki da tayi wata dariyar mugunta tace
"Karkiyi saurin yanke hukunci Inna ki dai jira kiga qarshen wasa dan in akayi wasa babu tabbacin ki fita da qafafunki daga cikin gidan nan muddin ta gano wacece ke".
Mairo ta hade yawu ta miqe tana gasgata zancen Bilkin tabbas Hajiya bata da wannan baqin Labarin, wato shi Alhaji baya gudun rigima ya ringa zuwa yana daura Aure matarsa bata sani ba dadi daya data ji da taga Alamar Bara'atu ce zata dawo dalilin ganin Hadiza.
A can daki kuwa Binta na zaune kan kujera ta harde qafa Lantana na daga qasa suna magana,
"Ku tabbatar da basu buqaci komai ba komai suke so a musu, so nakeyi idan sun koma dukda nasan waccen shegiyar ba zata taba fadar Alherina ba amma saura da yau suka fara zuwa dole dai suce na musu Kirki" Bintan ta fadawa Lantana ta miqe cikin rawar jiki tana cewa
"An gama Hajiya, kin san dama ni indai Ladabin Kule ne nan na fi kauri laka laka zanwa mutum kamar zan kwanta masa idan ina son abu".
Binta ta bita da kallo tana fassara maganarta a zuciyarta kafin taja tsaki a fili tace
"Kar nake kallonki ai karki dauka wawiyace ni kice zaki shammaceni".
Bajewa su Bilki sukayi suka kwashi Abinci abinsu, Hadiza ta tattaro kwanukan da suka gama dasu ta fito dasu waje gurin wanke wanke ta tarar da Lantana na wanke tukwanen da akayi abincin rana Mairo kuma na qoqarin dora na dare ta aje kwanukan hannunta tana musu sannu suka amsa Lantana ta qureta da ido tana si ta tuna inda ta santa bata tuno dinba Hadizan ta juya ciki. Haka taci gaba da wanke wanken tana ta qoqarin gano inda ta santa haka nan kuma ta tsaya mata a rai harta gama tana maida kwanuka ta kasa haqura ta cewa Mairo
"Nikam fuskar matar can batayi miki kalar sani ba?"
"Gaskiya Aa, ke kin santa ne?" Ta mayar mata da tambaya se ta tabe baki tace
"Oho nidai se na ga kamar nasan me kama da ita, qila kama ce to ko kuma a hidimar gidan nan muka taba haduwa da ita"
"Ta yuwu hakan" Mairo ta sake bata amaa tana cigaba da abinda yake gabanta.
Daga soro aka rafka sallama, muryar gardi ce Lantana da bata komai taja Gyalenta ta leqa taga Maza biyu da motar kayan katako a qofar gidan.
"Yauwa, kiyiwa Hajiyar magana kice ga kaya Alhaji yace a Kawo" wanda da alama shine Direba ya fada mata kafin ta bashi amsa Bilki da ta jiyo sallamar itama ta biyo sahu tana ganin kayan kuma ta gane nasu ne dan haka tace
"Ku sauke toh a shigo dasu, ga Almajirai nan su tayaku"
"Toh Hajiya" suka amsa mata kafin su fara kiciniyar kwance Belet din da suka zagaye kayan da ita.
https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*PAGE 26*
"Hajiya wasu Mazane da motar kayan katako, wannan me kama da Alhajin tace su shigo dasu gashi ana kaiwa wancan dakunan" Lantana ta sanarwa da Binta. Mamaki ya kama Bintan, kayan katako kuma na menene? Ta tambayi kanta, to kodai Bilkince zata dawo nan gidan da zama tunda ta samu Labarin a gida take auranta ya mutu? In ko haka ne da anyi tashin hankali da masifa kuwa, ita da gidanta bata san komai ba kawai taga ana shigo mata da kayan gado taqamar tana Qanwar Megida ko? To dashi da itan duk basu isa ba.
Fita tayi dan taji ba'asi, a tsakar gidan taci karo da Audu da batasan shigowarsa ba tana ganinsa tace
"Yawwa gara da kazo, ban fahimci zuwansu Bilki ba ga kuma wasu kaya da akw shigo dasu na menene?"
Fuska a sake ya dubeta bayan daya bawa Direban motar da suka kawo kaya kudi dan har sun gama saukewa yace
"Kayan su Babangida ne"
"Su Babangida? Su din ne aka siyawa kayan daki se kace na Amarya sababbin Gado da kujeru?" Ta tambayeshi fuskarta na nuna mamakin da take ciki.
Tafiya ya farayi zuwa dakin da su Bilkin keta kiciniyar hada kayan yana ce mata
"Amarya ce mana, ko bakya so a kwace miki kambunki?"
"Audu!" Ta kira sunansa a kausashe tana bin bayansa dan zuwa yanzu kanta ya fara qullewa bata fahimtar maganganunsa.
"Ina zuwa, bari mu gaisa dasu Goggo Ramma ki jirani a sama" ya bata amsa daga nan ya shige falon ya barta a tsaye tana saqa da warwara tana jiyoshi da Bilki yana ce mata
"Hajiya Bilki Tijjan Bechi"
"Kace na qulle jakata bana zan sauke farali" Bilkin ta mayar masa tana ajiye tsumman da take goge goge dashi, yayi murmushi yana tsugunnawa dan gaida Su Goggo Habi ya bata amsa da cewa
"Kusan haka, da dai layi za'abi se Yaya Mairo da Amina sunje sannanke amma yanzu kin san ance Albarkacin Kaza qadangare kansha ruwan kasko to kena Albarkacin qawarki bana zaku jera ku tafi tare in Allah ya yarda".
Bilki ta rangada gida wadda ta zama kamar saukar guduma a kwakwalwar Binta cikin karadi tace
"Nagode dan uwana Allah ya ida nufi, harna hangomu nida Bara'atu muna zagaye Ka'aba ya ubangiji ka nuna mun wannan rana" suka amsa matada Amin gaba daya.
A mutunce suka gaisa kafin ya fito ya ganta tsaye a gurin har sannan,
"To muje" ya fada mata se kuwa ta bishi kamar raqumi da akala zuwa saman nasa.
"Bismilla ku shiga tana ciki Hajiyar" ta fada musu bayan data gaidasu a mutunce, kafin suyi magana Lantana tayi tsugul tace
"Ban gane su shiga ba? Ke haka akeyi kawai daga ganin mutane kice su shigar mata daki kina ganinsu yarkace yarkace da wasu uban buhunhuna kamar yan gudun Hijira qilama mabarata masu neman mafaka ko kinga sun miki kalar qawayen Hajiya balle kice su shiga daki kai tsaye?"
"Hayaniyar me akeyi ne haka? Lantana keda su waye?" Binta da subadadin lantana ya farkar da ita ta fada tana leqowa ta tagar uwar dakanta dake cikin tsakar gidan. Tayi sak ganin Bilki wadda suna hada ido ta tamke fuska tam.
"Kune tafe cikin ranar nan? Sannunku da zuwa aiko be sanar mun kuna tafe ba ku shigo" ta fada iyakar dauriyarta a qoqarinta na janyo su a jiki da kirki kamar yanda Turai ta bata shawara Bilki kadai ta sani cikinsu ko kuma ta gane tunda tasan Hadiza sedai sanin babu abinda ze kawota gidan yasa bata ma kawo a ranta ta santa ba. Dankwalinta ta shiga nema dan ta fito falo ta jiyo Bilki na cewa
"Da yake zuwan namu ba naki bane shi yasa be gaya miki ba, bari mu shiga can mun gode da tayi" daga haka suka ja kayansu zuwa dakin Bara'atun. Bi ta tabi bayansu da harara tareda sakin tsaki kafin ta daure kanta ta fito ranta na suya. Tsabar isa da samun guri ne yasa zasu kwaso jiki rabe rabe suzo mata gida kuma be gaya mata ba ko kuwa shima besan zasu zo ba sannan wadannan uban kwanukan da suke tafe dasu na menene ko daga Kasuwa suke? Take tambayar kanta harta fito tsakar gidan Lantana na tsaye guiwa tayi sanyi saboda yanda taji Hajiyar ta musu magana ya nuna mata sudin ba banza bane kamar yanda ta tsammata.
"Ashe baqinki ne Hajiya" ta fada tana sosa kai, Binta ta wuceta tana cewa
"Qannen megidan ne"
Seko ta dafe qirji ta zare ido, amma data tuna suda banza a gun Binta duk daya se ta dan saki ranta sedai mamaki ya kamata da har Binta tayi musu tayin shiga dakinta, to shiri suka fara haka ko kuwa duk cikin wasan kwaiwayon data fara ne?
Binta kitchen din tsakar gidan ta shiga ta tarar da Mairo na kwashe Shinkafar data gama dafawa Miyar na kan wuta tana idasa soyuwa.
"Idan kin gama akai musu abinci kafin nan a hada ruwa da lemo idan da Alkaki ki hada musu" ta bata unarni ita kuma ta amsa da
"Toh Hajiya".
Dakin da suka shigan ta wuce, sun shimfida tabarma cikin kayan da sukazo dasu Mata biyu na zaune Bilki na tsaye taba duban dakin daya qara kyau dalilin sabon fenti da qofofi harda Abun sak kwan lantarki duk aka canza se gurin ya qara haske da kyau.
Daga bakin qofar ta tsaya ta aika musu gaisuwa rai babu dadi kamar an mata dole suka amsa banda Bilki data shige daya daga cikin dakunan gurin, Binta tayi kyacci a ranta tana ayyana yanda zataci kan uwarta kafin ta kalli yar dattijuwar da ta fisu shekaru Qanwar Inna Hajara ce tace
"Bari a kawo musu ruwa, bamu san da zuwanku ba ai da an muku shiri me kyau"
"Ba komai yar nan hakan ma mungode" matar ta fada a ranta tana mamakin rashin kirkin Bintan da ake fada ita dai bata gani ba.
"Munafuka" Bilki ta fada bayan ta juya, matar da ake kira da Inna Habi tace
"Kai Bilkisu, niko banga abinda kuke fada akan matar nan ba. Yanzu wace macece zata tari dangin kishiya sunzo danki haka?"
Mairo ta aje Try data doro su ruwa da Lemo da kayan tabawa, seda ta zabura jin maganar Inna Habin ta kalli Bilki da tayi wata dariyar mugunta tace
"Karkiyi saurin yanke hukunci Inna ki dai jira kiga qarshen wasa dan in akayi wasa babu tabbacin ki fita da qafafunki daga cikin gidan nan muddin ta gano wacece ke".
Mairo ta hade yawu ta miqe tana gasgata zancen Bilkin tabbas Hajiya bata da wannan baqin Labarin, wato shi Alhaji baya gudun rigima ya ringa zuwa yana daura Aure matarsa bata sani ba dadi daya data ji da taga Alamar Bara'atu ce zata dawo dalilin ganin Hadiza.
A can daki kuwa Binta na zaune kan kujera ta harde qafa Lantana na daga qasa suna magana,
"Ku tabbatar da basu buqaci komai ba komai suke so a musu, so nakeyi idan sun koma dukda nasan waccen shegiyar ba zata taba fadar Alherina ba amma saura da yau suka fara zuwa dole dai suce na musu Kirki" Bintan ta fadawa Lantana ta miqe cikin rawar jiki tana cewa
"An gama Hajiya, kin san dama ni indai Ladabin Kule ne nan na fi kauri laka laka zanwa mutum kamar zan kwanta masa idan ina son abu".
Binta ta bita da kallo tana fassara maganarta a zuciyarta kafin taja tsaki a fili tace
"Kar nake kallonki ai karki dauka wawiyace ni kice zaki shammaceni".
Bajewa su Bilki sukayi suka kwashi Abinci abinsu, Hadiza ta tattaro kwanukan da suka gama dasu ta fito dasu waje gurin wanke wanke ta tarar da Lantana na wanke tukwanen da akayi abincin rana Mairo kuma na qoqarin dora na dare ta aje kwanukan hannunta tana musu sannu suka amsa Lantana ta qureta da ido tana si ta tuna inda ta santa bata tuno dinba Hadizan ta juya ciki. Haka taci gaba da wanke wanken tana ta qoqarin gano inda ta santa haka nan kuma ta tsaya mata a rai harta gama tana maida kwanuka ta kasa haqura ta cewa Mairo
"Nikam fuskar matar can batayi miki kalar sani ba?"
"Gaskiya Aa, ke kin santa ne?" Ta mayar mata da tambaya se ta tabe baki tace
"Oho nidai se na ga kamar nasan me kama da ita, qila kama ce to ko kuma a hidimar gidan nan muka taba haduwa da ita"
"Ta yuwu hakan" Mairo ta sake bata amaa tana cigaba da abinda yake gabanta.
Daga soro aka rafka sallama, muryar gardi ce Lantana da bata komai taja Gyalenta ta leqa taga Maza biyu da motar kayan katako a qofar gidan.
"Yauwa, kiyiwa Hajiyar magana kice ga kaya Alhaji yace a Kawo" wanda da alama shine Direba ya fada mata kafin ta bashi amsa Bilki da ta jiyo sallamar itama ta biyo sahu tana ganin kayan kuma ta gane nasu ne dan haka tace
"Ku sauke toh a shigo dasu, ga Almajirai nan su tayaku"
"Toh Hajiya" suka amsa mata kafin su fara kiciniyar kwance Belet din da suka zagaye kayan da ita.
https://chat.whatsapp.com/I8xKHGurk7EBf5ZqQdxHKG
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*PAGE 26*
"Hajiya wasu Mazane da motar kayan katako, wannan me kama da Alhajin tace su shigo dasu gashi ana kaiwa wancan dakunan" Lantana ta sanarwa da Binta. Mamaki ya kama Bintan, kayan katako kuma na menene? Ta tambayi kanta, to kodai Bilkince zata dawo nan gidan da zama tunda ta samu Labarin a gida take auranta ya mutu? In ko haka ne da anyi tashin hankali da masifa kuwa, ita da gidanta bata san komai ba kawai taga ana shigo mata da kayan gado taqamar tana Qanwar Megida ko? To dashi da itan duk basu isa ba.
Fita tayi dan taji ba'asi, a tsakar gidan taci karo da Audu da batasan shigowarsa ba tana ganinsa tace
"Yawwa gara da kazo, ban fahimci zuwansu Bilki ba ga kuma wasu kaya da akw shigo dasu na menene?"
Fuska a sake ya dubeta bayan daya bawa Direban motar da suka kawo kaya kudi dan har sun gama saukewa yace
"Kayan su Babangida ne"
"Su Babangida? Su din ne aka siyawa kayan daki se kace na Amarya sababbin Gado da kujeru?" Ta tambayeshi fuskarta na nuna mamakin da take ciki.
Tafiya ya farayi zuwa dakin da su Bilkin keta kiciniyar hada kayan yana ce mata
"Amarya ce mana, ko bakya so a kwace miki kambunki?"
"Audu!" Ta kira sunansa a kausashe tana bin bayansa dan zuwa yanzu kanta ya fara qullewa bata fahimtar maganganunsa.
"Ina zuwa, bari mu gaisa dasu Goggo Ramma ki jirani a sama" ya bata amsa daga nan ya shige falon ya barta a tsaye tana saqa da warwara tana jiyoshi da Bilki yana ce mata
"Hajiya Bilki Tijjan Bechi"
"Kace na qulle jakata bana zan sauke farali" Bilkin ta mayar masa tana ajiye tsumman da take goge goge dashi, yayi murmushi yana tsugunnawa dan gaida Su Goggo Habi ya bata amsa da cewa
"Kusan haka, da dai layi za'abi se Yaya Mairo da Amina sunje sannanke amma yanzu kin san ance Albarkacin Kaza qadangare kansha ruwan kasko to kena Albarkacin qawarki bana zaku jera ku tafi tare in Allah ya yarda".
Bilki ta rangada gida wadda ta zama kamar saukar guduma a kwakwalwar Binta cikin karadi tace
"Nagode dan uwana Allah ya ida nufi, harna hangomu nida Bara'atu muna zagaye Ka'aba ya ubangiji ka nuna mun wannan rana" suka amsa matada Amin gaba daya.
A mutunce suka gaisa kafin ya fito ya ganta tsaye a gurin har sannan,
"To muje" ya fada mata se kuwa ta bishi kamar raqumi da akala zuwa saman nasa.