Sashe 130
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fafur tace Anty Rabi da Momy ba zasuje mata jere ba, Baba Bilki ma da tace ba za'a da ita ba dake har yau na sanyi tayi ba tace ai uban Binta ma yayi kaɗan balle ita ta hanata zuwa gano gidan Yar Audu. Saboda neman suna tace wai Hajiya Balaraba tazo aje da ita tace Aa saje kai Amarya daga ƙarshe dai bisa tursasawar Turai suka tafi da ita da Momy wadda bata so zuwa ba se Hajiya Zainab da Munirah ƙanwar Binta wadda har yau sama da shekaru hamsin kenan tana zaune bata samu Mijin aure ba bayan rasuwar Mamansu ne ta dawo nan Kano da ta fara zama gidan Binta zama yaƙi daɗi se kawai ta siyi gida take zaune abunta tana kasuwancinta tana cigaba da roƙon Allah daya yanke mata dukda ta san cewar ba komai ya janyo mata shiga halin da take ciki ba se haƙƙin baiwar Allah da bataji ba bata gani ba suka laƙa mata sharrin da harta mutu wasu na kallonta dashi. Suka hanata zaman lafiya a gidan auranta harta koma ga Allah.
A can Kaduna suka haɗe da sauran yan uwan Binta akaje akayi jeren wanda babu wani abin arziƙi data siya. Kayan Gado dai a BECHI FURNITURES yace aje a ɗaukar mata duk abinda uba yakeyi saɓanin su Khadija dayake ƙayyade Adadin kuɗi yace a ɗauki kaya na kaza. Su Turai ne sukaje suka zaɓa suka darje kaya na ƙarshen mutunchi a shagon, da Alhaji yaga Invoice ya ringa surfa masifar da bata da Amfani domin dai shiya nada dama kuma sun rigada sun ɗauka har an jera dan a Branch ɗinsa na Abuja suka kwasa ƙarshe abin ya ƙare akan Aslamiyyah yace Gado biyu kujera biyu za'a ɗaukar mata saɓanin Hajiya ƙarama da aka sakawa huɗu, ɗaki biyar ne a gidan da faluka biyu manya se ƙarami ɗaya wanda yake haɗe da Master Bedroom a sama shine na Megidan iyayensa sun gyara masa dan haka hatta ɗakin da me aiki zata zauna Royal aka saka saboda samun guri da nuna akwai.
Kayan Kitchen dai daman yace musu a Al'adar Hausawa uwa ce takeyi to yana kan wannan magana har akan Hajiya be saketa ba dan haka ita tayi kayan kitchen tarkacen banza da wofi wasu matsiyatan kuloli da fulasai ta bakin Turai. Yanda ta ringa zuzuta ta gama siyan komai dan ƙin yarda suje siyayyar tare tayi, haka ta nuna mata kayan taƙi se randa zasu tafi Jere da za'a ɗiba aka tattara kaya ko cika buhu biyu basuyi ba amma faɗi take
"Kinga kaya ko Turai? Dama na gaya miki sena baki mamaki ai bikin Nazira shammatata akayi amma wannan na shirya"
"Billahillazi Binta idan baki fitar da kuɗinki kinci kin morawa kanki ba se kin mutu kina kwance a ƙasa zakiga yayanki na wadaƙa dasu, yanzu wannan kayan kike zuzutu akai? Abinda ko Talaka me zuciya se yayi ninkin abinda kikayi wannan abin kike so akai ace daga gidan Bechi suka fito? Turai ta ringa masifa kamar zata ari baki tana kafa mata hujja da kanta yanda takeyi idan zata aurar da Yayanta da sauran ƙawayensu, ta kawo mata Misalin Momy, auran Khadija da Annah ita da kanta tace har seda suka maido da wasu abubuwan gida dan seda aka kai sukaga an siya an ƙara siya tasan kuma yanzu ma na Aslamiyyah haka zata fitar da kanta kunay.
Duk wanda yaga kayan gadonta da kujeru yasan ubanta ne yayi mata ke za'a zaga ace uwarta bata da zuciya dan wlh ko yar riƙo a gidan nanta wuci akaita da wannan tarkacen. Ƙarshe se Alhaji Zakariyya da Alhaji Naziru harda Yakubu Turan ta kira tace kowa yazo ya bada abinda ya samu, ta tattara ta bazama kasuwa tayo mata siyayyar kayan kichen na fita kunya suka kai ta barwa Binta tsiyarta da tace ta ajiyewa Auta Saratu ta huta ita tasan ba zata raina wannan ɗin ba toh fa tunda suka dawo aka kawo mata Video shikenan ta kasa nutsuwa labari data kai aya zata maimaito tun Alhajin yana ji harya gaji yace mata
"Binta yanda kike nanata mun labarin gidan nan ko zuwa nayi yanzu bazan ɓata ba danna gama gane kowanne lungu da saƙo na gidan, ki bani abincin naci kafin ya huce dan Allah do nakeyi na fita zamu haɗu da Alƙali mu tattauna yanda taro ze kasance kinga lokaci yana ƙaratowa yau Litinin saura kwana huɗu ɗaurin aure".
"Ai toh yi haƙuri wlh santin gidan ne yaƙi ya barni, ai Hajiya dai tayi gida Allah ya tsole idon maƙiya yasa mutu ka raba" ta faɗa tana bashi. Shida ya shiga cin abincin yana jinta dan batayi shiru ba. Ta gyara zama tace
"Dama Alhaji zancen gurin Kamu ne an gama magana da mutanen nan yanzu sun dawo sunce wai kuɗi yayi kaɗan se an ƙara kuma ni nayi ƙarƙaf dubu Ashirin yanzu se nayi da gaske zan fito da ita ai bikin nan dai ya talautani da gaske".
Ya kalleta ta gefen ido a ransa yana mamakinta, wai ta kashe kuɗi kome ta yi se Allah bayan duk abinda ake ciki yana da labari. Zakariyya ya gaya masa su suka bada kuɗin kayan kitchen bayan ta ɗiora musu Alhakin abinda za'aci a gurin Mother's eve data shirya shi kuma nan be san Buhu nawa da galan na mai nawa da sauran kayan abinci data kwashe masa a Store tace za'ayi abincin biki ba. Kaji ɗari biyu ya saka aka bata ita kaɗai banda Sa da za'a yanka na abincin yini. Tunda aka fara zancen bikin nan Aisha bata ce ma ya bata sisin kobo ba, Bilki ce ta nusashsheshi har ya batan dukda be kai ko kwatan abinda Binta ta Ƙwamusa a hannunsa ba. Kayan gado kansu ya banbanta Hajiya Ƙarama cewa yayi su ɗauki wanda ya musu Aslamiyya kuwa dalilin ɓarnar da su Turai suka masa shiya faɗi kalar wanda za'a ɗaukar masa an gaya masa Ahmad da Sarki ne sukayi cikon Kuɗaɗe masu nauyi suka ɗaukar mata irin na Hafsatun kuma duk abinda ya kamata ace yayi wanda Aisha bata tambayeshi ba su sukayi yana kallo aka ringa sauke ruwa da lemo besan katan nawa bane inji Ahmad Jafar kuma shi ya siya Musu Cinema Tv su biyun nan cikin Yaya bila'adadin daya haifa ne suke da zuciyar bashi gudummawar auran ƙannensu dukda sun san yana dashi ba babu ba amma yaji abinhar cikin zuciyarsa.
"Alhaji kayi shiru" Hamshaƙiyar ta girgizashi. Ya aje farantin hannunsa ya miƙe tsaye yana cewa
"Ki karɓo kuɗinki kizo kuyi a nan cikin gidan kamar yanda su Aisha zasuyi ni banida wasu kuɗi da zan sake baki kuma a yanzu nayi iya abinda zan iya"
"Ai shikenan, kana ji Jafaru wai baze zo bikin bako? Gaskiya ka kirashi kayi masa magana ta yaya za'ayi ace baze halarci ɗaurin auran ba? Ta ya mutane wai zasu san Ɗanka ne yafi so ayi ta kallonsa a ba kowa ba ai idanya fito kowa ya san Ɗanka ne darajar sa seta sake linkuwa a ƙasar nan ko ya kace?" Ta sake soko masa wata maganar, ya miƙe yana shiga ɗaki yace
"Duk yanda kika ce Binta, bari na shirya na fita dai na baki guri" ya barta tana cizon yatsa. Daman ba Even centre data kama, tunda taji a gida Momy zatayi Kamunta zata kira masu Decoration taje kakarta ta yanke saƙa bari zatayi ta gama shirya komai se ranar tayi ta kankane ita da mutanenta dan ba zata iya zare Miliyan nawa ta kaiwa masu gurin biki ba, abinci ma da Turai tasa ta kashi kuɗaɗe ta bayar ciwon rai takeyi, so tayi ta bawa masu aikinsu ayi shi nan a cikin gida amma tace gun yan gayu zasu kai, so tayi ya bata kuɗin ta rage asarar wanda tabayar shine yace bashida su yanzu duk kwalliyar nan da tayi ta tashi a banza kenan ai shikenan.
Alhaji ya fito a shirye yana waya, bata san da waye ba abinda taji kawai ya fizgi hankalinta shine
"Babu damuwa nagode, bari mu gama da hayaniyar wannan bikin zanyi magana dashi. Idan son samune ya haƙura da yarinyar ya nemi wata dan sam banji abin ya kwanta mun a rai ba amma bama so na hanashi abinda yake so saboda yaron nada biyayya nasan muddin nace Aa tilas ze haƙura koda ace hakan ze cutar dashi amma yanzu zan samu Alƙali shima da maganar yanda mukayi zakaji".
"Toh fa wane yaro kuma ake magana akai?" Tayi tsalam ta tambaya bayanya kashe wayar. Yana tafiya ze sauka ƙasa tabi bayansa yace
"Ahmad ne, ya samu yarinyar da ze aura. Kiyiwa wancan yaron magana shima ya dakata da shashancin da yakeyi ya fitar da mata dan tare zan haɗu bana son Biki a rarraben nan"
"Yo naji kana cewa yarinyar bata maka ba? Halan kwashe kwashe yayo ko? Ni daman nasan za'a rina Allah yasa dai ba gidan matsiyata ya kwaso auran ba mu shiga uku su ƙara yawa bamu gama data gidan nan ba ya kwaso mana wata" Hajiya ta faɗa shidai be bata amsa ba ya fice daga falon dan Malam Sadi Driver sa yana tsaye harya kunna mota.
Ta wuce ciki inda ta baro ƙawayenta da sukazo ana ta tsara yanda biki ze kasance, Kamu dai rigar na Momy zasu shiga dukda ba haka su Hajiya Zainab suka so ba Turai kuma tace haka ne daidai tunda dai Yaran nan ubansu ɗaya toh ayi Kamun nan a tare idan yaso tunda kowacce gidan Mijinta sun shirya Dinner se suyi abarsu daban ga sauran events da kowacce Amarya zatayi da Ƙawayenta.
"Yanzu kawai sedai mu zama yan kallo mun raɓe raɓe kenan?" Hajiya Sha'awa ta faɗa, Binta ta karkace tace
"Inji wa? Ai biki namune wahala kawai zasu mana su shirya komai. Da kunji ance ina uwar Amarya ku rufa mun baya mu shige, duk wani kira da za'ayi ku shike kuyi kinini karku basu wata ƙofa a gurin" akayi shewa aka tafa.
A can Kaduna suka haɗe da sauran yan uwan Binta akaje akayi jeren wanda babu wani abin arziƙi data siya. Kayan Gado dai a BECHI FURNITURES yace aje a ɗaukar mata duk abinda uba yakeyi saɓanin su Khadija dayake ƙayyade Adadin kuɗi yace a ɗauki kaya na kaza. Su Turai ne sukaje suka zaɓa suka darje kaya na ƙarshen mutunchi a shagon, da Alhaji yaga Invoice ya ringa surfa masifar da bata da Amfani domin dai shiya nada dama kuma sun rigada sun ɗauka har an jera dan a Branch ɗinsa na Abuja suka kwasa ƙarshe abin ya ƙare akan Aslamiyyah yace Gado biyu kujera biyu za'a ɗaukar mata saɓanin Hajiya ƙarama da aka sakawa huɗu, ɗaki biyar ne a gidan da faluka biyu manya se ƙarami ɗaya wanda yake haɗe da Master Bedroom a sama shine na Megidan iyayensa sun gyara masa dan haka hatta ɗakin da me aiki zata zauna Royal aka saka saboda samun guri da nuna akwai.
Kayan Kitchen dai daman yace musu a Al'adar Hausawa uwa ce takeyi to yana kan wannan magana har akan Hajiya be saketa ba dan haka ita tayi kayan kitchen tarkacen banza da wofi wasu matsiyatan kuloli da fulasai ta bakin Turai. Yanda ta ringa zuzuta ta gama siyan komai dan ƙin yarda suje siyayyar tare tayi, haka ta nuna mata kayan taƙi se randa zasu tafi Jere da za'a ɗiba aka tattara kaya ko cika buhu biyu basuyi ba amma faɗi take
"Kinga kaya ko Turai? Dama na gaya miki sena baki mamaki ai bikin Nazira shammatata akayi amma wannan na shirya"
"Billahillazi Binta idan baki fitar da kuɗinki kinci kin morawa kanki ba se kin mutu kina kwance a ƙasa zakiga yayanki na wadaƙa dasu, yanzu wannan kayan kike zuzutu akai? Abinda ko Talaka me zuciya se yayi ninkin abinda kikayi wannan abin kike so akai ace daga gidan Bechi suka fito? Turai ta ringa masifa kamar zata ari baki tana kafa mata hujja da kanta yanda takeyi idan zata aurar da Yayanta da sauran ƙawayensu, ta kawo mata Misalin Momy, auran Khadija da Annah ita da kanta tace har seda suka maido da wasu abubuwan gida dan seda aka kai sukaga an siya an ƙara siya tasan kuma yanzu ma na Aslamiyyah haka zata fitar da kanta kunay.
Duk wanda yaga kayan gadonta da kujeru yasan ubanta ne yayi mata ke za'a zaga ace uwarta bata da zuciya dan wlh ko yar riƙo a gidan nanta wuci akaita da wannan tarkacen. Ƙarshe se Alhaji Zakariyya da Alhaji Naziru harda Yakubu Turan ta kira tace kowa yazo ya bada abinda ya samu, ta tattara ta bazama kasuwa tayo mata siyayyar kayan kichen na fita kunya suka kai ta barwa Binta tsiyarta da tace ta ajiyewa Auta Saratu ta huta ita tasan ba zata raina wannan ɗin ba toh fa tunda suka dawo aka kawo mata Video shikenan ta kasa nutsuwa labari data kai aya zata maimaito tun Alhajin yana ji harya gaji yace mata
"Binta yanda kike nanata mun labarin gidan nan ko zuwa nayi yanzu bazan ɓata ba danna gama gane kowanne lungu da saƙo na gidan, ki bani abincin naci kafin ya huce dan Allah do nakeyi na fita zamu haɗu da Alƙali mu tattauna yanda taro ze kasance kinga lokaci yana ƙaratowa yau Litinin saura kwana huɗu ɗaurin aure".
"Ai toh yi haƙuri wlh santin gidan ne yaƙi ya barni, ai Hajiya dai tayi gida Allah ya tsole idon maƙiya yasa mutu ka raba" ta faɗa tana bashi. Shida ya shiga cin abincin yana jinta dan batayi shiru ba. Ta gyara zama tace
"Dama Alhaji zancen gurin Kamu ne an gama magana da mutanen nan yanzu sun dawo sunce wai kuɗi yayi kaɗan se an ƙara kuma ni nayi ƙarƙaf dubu Ashirin yanzu se nayi da gaske zan fito da ita ai bikin nan dai ya talautani da gaske".
Ya kalleta ta gefen ido a ransa yana mamakinta, wai ta kashe kuɗi kome ta yi se Allah bayan duk abinda ake ciki yana da labari. Zakariyya ya gaya masa su suka bada kuɗin kayan kitchen bayan ta ɗiora musu Alhakin abinda za'aci a gurin Mother's eve data shirya shi kuma nan be san Buhu nawa da galan na mai nawa da sauran kayan abinci data kwashe masa a Store tace za'ayi abincin biki ba. Kaji ɗari biyu ya saka aka bata ita kaɗai banda Sa da za'a yanka na abincin yini. Tunda aka fara zancen bikin nan Aisha bata ce ma ya bata sisin kobo ba, Bilki ce ta nusashsheshi har ya batan dukda be kai ko kwatan abinda Binta ta Ƙwamusa a hannunsa ba. Kayan gado kansu ya banbanta Hajiya Ƙarama cewa yayi su ɗauki wanda ya musu Aslamiyya kuwa dalilin ɓarnar da su Turai suka masa shiya faɗi kalar wanda za'a ɗaukar masa an gaya masa Ahmad da Sarki ne sukayi cikon Kuɗaɗe masu nauyi suka ɗaukar mata irin na Hafsatun kuma duk abinda ya kamata ace yayi wanda Aisha bata tambayeshi ba su sukayi yana kallo aka ringa sauke ruwa da lemo besan katan nawa bane inji Ahmad Jafar kuma shi ya siya Musu Cinema Tv su biyun nan cikin Yaya bila'adadin daya haifa ne suke da zuciyar bashi gudummawar auran ƙannensu dukda sun san yana dashi ba babu ba amma yaji abinhar cikin zuciyarsa.
"Alhaji kayi shiru" Hamshaƙiyar ta girgizashi. Ya aje farantin hannunsa ya miƙe tsaye yana cewa
"Ki karɓo kuɗinki kizo kuyi a nan cikin gidan kamar yanda su Aisha zasuyi ni banida wasu kuɗi da zan sake baki kuma a yanzu nayi iya abinda zan iya"
"Ai shikenan, kana ji Jafaru wai baze zo bikin bako? Gaskiya ka kirashi kayi masa magana ta yaya za'ayi ace baze halarci ɗaurin auran ba? Ta ya mutane wai zasu san Ɗanka ne yafi so ayi ta kallonsa a ba kowa ba ai idanya fito kowa ya san Ɗanka ne darajar sa seta sake linkuwa a ƙasar nan ko ya kace?" Ta sake soko masa wata maganar, ya miƙe yana shiga ɗaki yace
"Duk yanda kika ce Binta, bari na shirya na fita dai na baki guri" ya barta tana cizon yatsa. Daman ba Even centre data kama, tunda taji a gida Momy zatayi Kamunta zata kira masu Decoration taje kakarta ta yanke saƙa bari zatayi ta gama shirya komai se ranar tayi ta kankane ita da mutanenta dan ba zata iya zare Miliyan nawa ta kaiwa masu gurin biki ba, abinci ma da Turai tasa ta kashi kuɗaɗe ta bayar ciwon rai takeyi, so tayi ta bawa masu aikinsu ayi shi nan a cikin gida amma tace gun yan gayu zasu kai, so tayi ya bata kuɗin ta rage asarar wanda tabayar shine yace bashida su yanzu duk kwalliyar nan da tayi ta tashi a banza kenan ai shikenan.
Alhaji ya fito a shirye yana waya, bata san da waye ba abinda taji kawai ya fizgi hankalinta shine
"Babu damuwa nagode, bari mu gama da hayaniyar wannan bikin zanyi magana dashi. Idan son samune ya haƙura da yarinyar ya nemi wata dan sam banji abin ya kwanta mun a rai ba amma bama so na hanashi abinda yake so saboda yaron nada biyayya nasan muddin nace Aa tilas ze haƙura koda ace hakan ze cutar dashi amma yanzu zan samu Alƙali shima da maganar yanda mukayi zakaji".
"Toh fa wane yaro kuma ake magana akai?" Tayi tsalam ta tambaya bayanya kashe wayar. Yana tafiya ze sauka ƙasa tabi bayansa yace
"Ahmad ne, ya samu yarinyar da ze aura. Kiyiwa wancan yaron magana shima ya dakata da shashancin da yakeyi ya fitar da mata dan tare zan haɗu bana son Biki a rarraben nan"
"Yo naji kana cewa yarinyar bata maka ba? Halan kwashe kwashe yayo ko? Ni daman nasan za'a rina Allah yasa dai ba gidan matsiyata ya kwaso auran ba mu shiga uku su ƙara yawa bamu gama data gidan nan ba ya kwaso mana wata" Hajiya ta faɗa shidai be bata amsa ba ya fice daga falon dan Malam Sadi Driver sa yana tsaye harya kunna mota.
Ta wuce ciki inda ta baro ƙawayenta da sukazo ana ta tsara yanda biki ze kasance, Kamu dai rigar na Momy zasu shiga dukda ba haka su Hajiya Zainab suka so ba Turai kuma tace haka ne daidai tunda dai Yaran nan ubansu ɗaya toh ayi Kamun nan a tare idan yaso tunda kowacce gidan Mijinta sun shirya Dinner se suyi abarsu daban ga sauran events da kowacce Amarya zatayi da Ƙawayenta.
"Yanzu kawai sedai mu zama yan kallo mun raɓe raɓe kenan?" Hajiya Sha'awa ta faɗa, Binta ta karkace tace
"Inji wa? Ai biki namune wahala kawai zasu mana su shirya komai. Da kunji ance ina uwar Amarya ku rufa mun baya mu shige, duk wani kira da za'ayi ku shike kuyi kinini karku basu wata ƙofa a gurin" akayi shewa aka tafa.