Sashe 104
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Badan taso ba shine ta canza da Atamfar dukda itan ma Turai tace ba tayi ba, gafa kayan nan a jibge amma ta bari ta zaɓa mata ma tace Aa, da babu gara babu daɗi Atamfar Ɗinkin doguwar rigane an mata Bead work a wuya da bakin hannun, Sarƙar ce dai tace ba zata cire ba, tilas Turai ta barta, a neman mayafi kuma aka tafka abin kunya dan Hajiya dai bata da Mayafin fita Taro, ƙarshe se a gurin Momy Turai taje da kanta ta Aro mata Jaka da Takalmi kuma aka samu a gurin Hajiya ƙarama.
"Wlh Binta ki canza hali, wannan tsumulmula har ina? Kuɗi kina dasu kamar su kasheki amma ace ko jikinki ba zaki iya kashewa ba wannan wace irin rayuwa ce? Yanzu tsabagen zubar da ƙima Gyalen da zaki saka ki fita kunyar Ɗanki ma baki dashi se an aro a gurin kishiya wannan abin takaici har ina?"
Turai ta dasa mata mita, Binta dake kiciniyar Rataya Jaka a hammata ta buɗe baki zata bata amsa suka jiyo ihun Yara ana oyoyo Uncle Jay, Hajiya ta zabura tayi waje dan ta tabbatar da abinda take jiyowa, Jafar ɗin da ta gama haɗa jama'a da motoci zasu tafi tarowa ko kuwa wani daban suke nufi????
*ALBISHIRINKU MATA YAN UWANA YAN KWALISA NAZO MUKU DA WANI DADDADAN LABARI!!!.*
*NASAN KUNDADE KUNA NEMAN FITACCEN GURIN DAZAKUJE AMUKU GYARAN GASHINKU DANA JIKINKU CIKI DA WAJENSA,TO YANXU DAI GA DAMA TA SAMU...*
*LABARI NAKE BAKUFA AKAN AFINTY QUEENS SHAHARARREN SHAGONMU NA SALOON DAYA HADA KOMAI DA KOMAI DA KOWACE MACE YAR KWALISA IRINA KE BUKATA,SANNAN MUNADA KWARARRUN MA'AIKATAN DASUKASAN KAN AIKINKINSU,KUZO AFINTY QUEENS KUBIYA KUDI MUKUMA MU BATA LOKACINMU DOMIN TSATSTSAFO DUK WANI KYAWU NA JIKINKU DA ALLAH YAYI MUKU...*
*A AFINTY QUEENS MUNA AYYUKA KAMAR HAKA:*
*- HAIR SALOON*
*-HENNA*
*-SPA*
*-DUKKAN*
*-PEDICURE*
*-MANICURE*
*-SANNAN MUNA DA TURARUKA IRIN NA AMARE YAN MATA DA KUMA MAI KANKAT DAN UWAR GIDA TA TURARA GIDANTA JIKINTA DAMA KAYAN SAWARTA ITA DA YARANTA,,HARMA ZAWARAWA DUK MUN TANADI KOMAI*
*DOMINSU SUMA*
*-MUNADA SHOES AND BAGS SBD ISASSUN MATAN DA SUKA AMSA SUNANSU MATA*😊
*- MAKEUP NA BRIDAL ND CASUAL...*
*IDAN KINSAN KINAJIN LABARIN SHAGON SALOON NA AFINTY QUEENS AMMA BAKI TABBATAR DA YADDA AIKINSU YAKE BA TO YAR UWA GADAMA TASAMU MEZAKI TSAYA JIRA MAZA KEMA KI ZARGAYO SHAGONMU DAZAN JERA MIKI ADDRESS DINSHI A KASA DOMIN KEMA KI TABBATAR DA KALAR IRIN NAMU KWAZON DA MUKA KWARE AKANSHI GURIN GYARAN JIKIN YAN UWANMU MATA KUMA MUKE GABATAR MUSU DA JAKUNKUNA DA TAKALMA HARMA DA TURARUKAN WUTA DANA SHAFAMA JIKINSU DON NISHADIN ZUCIYARSU DANA MAZAJENSU....*
*AFINTY QUEENS DISCOVER BLISS IN BEAUTY 💅💯*
*Address 👇👇:*
*KU ZIYARCE MU A SHOP NO.9&10 SHEMA PLAZA,BEHIND SHEMA FILLING STATION KASUWAN BACCI KADUNA*
*TEL:08133379628.*
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*BOOK 2*
*PAGE 7*
"Jafaru, ni uwarka ka yaudara wannan karon ma kace mun biyar na yamma jirginku ze sauka seda na gama tattara jama'a zamu tafi taronka mu nunawa Duniya gatanka shine zaka tozartani Ko La'asar bata rufa ba ka diro a gidannan wato ka sanar da Amadu shi da yake ƙanin ubanka yaje ya dauko ka ko?" Hajiya ta faɗa tana zarewa Jafar idanu. Sakin Yaran Yayyensa da suka ruƙunƙumeshi suna masa oyoyo yayi ya nufeta fuska ɗauke da murmushi cikin shagwaɓa yana cewa
"Haba Hajiyata, dawowana lafiya ai shine komai yanzu, maimakon ki tareni da warm hug se ki farayi mun faɗa kuma?"
"Ka matsoni sena kwasheka da mari wlh, kai kuma me kama da dido dido, sau nawa zan faɗa maka ka fita daga sabgar Jafaru? Shin wai Aisha ta haifamin shine ko Yaya? Nace ka fita daga sabgata data Yayana Amadu amma kaƙi kaji shin ana dolene? To kaji da kunnenka duk bala'i da tuggunku sedai ya ƙare muku amma babu tsafi ko Asirin da zeci Jafaru wlh balle har kuga ya samu nakasu. Ɗaukaka da cigaba a rayuwa yanzu ya fara ganinta duk nasan shirinku da liƙe masan da kakeyi ba wai ban sani ba Asirin da kayi ka lashe masa zuciya ma ina kan karyashi kuma idan na juyo takanka ba zaka ji da daɗi ba"
"Haba Binta wannan wane irin abune kikeyi dan girman Allah? Meye amfanin wannan faɗe faɗen da kikeyi? Jafar dai gashi ya dawo lafiya me kuma kike da buƙata?" Turai ta katse Hajiya daga Hauragiyar da takeyi se kuwa ta zabga mata harara tace
"Babu ruwanki Turai, idan ba zaki tayani ba to kija bakinki kiyi shiru"
"Allah ya sawwaƙa miki, Sannu da zuwa kaji Jafar yi wucewarka can Ɗakinku, idan kuma zaka fara shiga ku gaisa da iyayenka da suka zo tarbarka toh, sannu da hanya" Hajiya Turai da bataji kashedo ba ta faɗa tana nunawa Jafar Palour Binta wanda jama'ar ciki sukayi shiru suna saurar abinda yake faruwa a wajen, Mutan gidan kuwa daman sun san za'a rina dan haka abin bezo musu a bazata ba. Jafar ya kalli Hajiya dake tsaye kamar sojanniya se numfarfashi take tana dannanwa Ahmad da yayi ƙasa da kansa harara, cikin sigar rarrashi Jafar ɗin yace mata
"Please mana Hajiyata, ki saki fuskarki, change of schedule muka samu na flight and na manta ban sanar miki ba. Believe me Yah Ahmad ma be sani ba seda na sauka Kano. You Know i Miss you so much shiyasa ba zan iya jira ba kuzo da yawa ba shiyasa kawai na kirasa nace yazo ya ɗauko ni amma ba laifinsa bane Allah nike da laifi amma kiyi haƙuri bari na koma Abuja kawai gobe sena dawo kizo keda jama'arki ku taroni" ya faɗa bayan daya isa dab da ita. Hararar da takewa Ahmad ta mayar kansa kafin tace
"Billahillazi karka ɗauka kaci banza baka isa ka tozartani a banza Ƙawayena su tafi suna gulmata ba sannan na ƙyakela muje cikin"
"Ai wanan unnecessary drama taki ce zata saka a tafi ana gulmar taki, sabida Allah meye abin tashin hankali a nan? Daman banda ɗaurawa kai ke kika saba taroshi ko yaya? Wlh Yaya Binta bakya gudun abin magana da abin sakawa kai ciwon kai a duniyar nan, duk inda zaman lafiya yake kin ɓauɗe masa" Munira ƙanwarta da batayi niyyar magana ba sedai ganin Abin na Yayartata na neman zarce misali yasa ta fito tana mata maganar. Fuuuu Hajiya ta shige ɗaki Jafar ya kalli Ahmad yace
"I'm sorry Yah Ahmad ni na jawo maka"
"Kaidai jeka kafin Hajiya ta canza maka wannan fuskar taka babu ruwana bari naje wani guri bazan jima ba zan dawo" Ahmad ya bashi amsa yana juyawa ya fice daga gidan.
Dukda yayi ƙoƙarin danne ɓacin ransa Amma Jafar ɗin seda ya fahimta, ya sani dole kalaman Hajiyar su sosa masa rai shi kansa beji daɗi ba amma yasan idanyace wani abu baya ga kalmar lallaɓi da banbaki a yanzu ƙara tunzurata zeyi tayi musu zazzafar Tijara a gaban mutane.
Jiki a sanyaye ya bi bayan Hajiyar, Yaƙe kawai ya ringayi yana gaisawa da tarin matan dake zaune falon Hajiyar, ya so ya gane wasu amma ya manta sunayensu wasu kuma sababbin fuskane a wajensa dan Hajiya badai tara
ƙawaye ba ga Yayayensu da suka kwaso sekace Biki keyi yanzu da tana nufin waɗannan jama'ar zata kwasa su tafi Ɗaukoshi daga Airport ɗin?.
Abinda ya sake ɓata masa rai yanda Yayan Ƙawayen Hajiyar suketa wani abu kamar masu shafar Jinnu, se ɗaukar hotuna suke da video ana sakoshi a ciki wasu ma yaga kamar Live sukeyi a IG suna faɗin gasu a gidansu Jay sunzo taron shi. Ƙasa Ƙasa yake jan tsaki yana durƙushe tsakiyar Mata kowacce da kalar soki burutsun hirar da take jefa masa da tambayoyi kamar sun aikeshi ya dawo, ba Hajiyar ba ba Ƙawayen nata ba babu wadda tayi tunanin a gajiye yake ko yana da buƙatar yaje ya huta seda Hajiya Turai ta fito daga Kitchen taje tana shirya abincin da za'a rabawa Jama'ar da Hajiya ta tara abin Allah arziƙin Jay yau ba Ƙaramin Better tasa aka shirya a gidan ba harda Rago aka gasa.
"Kana tsugunne Jafar ai se Ƙafafunka su gaji tashi kaje ka huta kaida ka shawo tafiya" Turai ta faɗa, ya saci kallon Hajjaju da ta zauna ta haɗe fuska tana juya ƙafa da gani lissafa yanda zataci ubansu daga shi Har Ahmad ɗin daya rusa mata shiri takeyi.
"Tashi kaje mana kake kallona da wasu idonka irin na Ubanku" ta faɗa tana zaburo masa. Ya miƙe yana shafa kai, daidai nan Faisal Bechi ya shigo yana kwalawa Hajiya kira yana cewa
"An fa gama saita komai har Photographer ya iso Allah dai yasa ma a barku ku shiga Airport ɗin irin wannan gayya se kace masu taro Governor.." Se kuma ya dakata saboda ganin Jay a gabansa, ya buga tsalle kamar yaro ya ɗaneshi yana ihu.
"Get off me my friend, kai baka zaka girma da shirme ba ko?" Jafar ya faɗa yana tureshi. Bakin Faisal kamar ze yage yace
"Welcome brother, ni na sani sedai ba Jafar Bechi ba wlh se kayi disappointing Hajiya amma fa ka kwafsa kai kasan irin Grand welcome da aka shirya maka kuwa yau?"
"Matsa na wuce" Jafar ya tureshi jin yana neman ɓallo masa sabon ruwa Faisal yabi bayansa yana kyalkyala dariyar mugunta yana gaya masa irin shirin da Hajiya tayi. Ɗakin Momy ya wuce, tana zaune kan kujera da waya a hannunta tana dannawa Khadija, Aslamiyya da Maimuna duk suna falon suna kallon Tv duk Drama da aka kwasa suna zaune basu fita ba balle su tanka Jafar ya shiga da sallama suka amsa masa a tare kowannensu fuskarsa na faɗaɗa da murmushi.
"Wlh Binta ki canza hali, wannan tsumulmula har ina? Kuɗi kina dasu kamar su kasheki amma ace ko jikinki ba zaki iya kashewa ba wannan wace irin rayuwa ce? Yanzu tsabagen zubar da ƙima Gyalen da zaki saka ki fita kunyar Ɗanki ma baki dashi se an aro a gurin kishiya wannan abin takaici har ina?"
Turai ta dasa mata mita, Binta dake kiciniyar Rataya Jaka a hammata ta buɗe baki zata bata amsa suka jiyo ihun Yara ana oyoyo Uncle Jay, Hajiya ta zabura tayi waje dan ta tabbatar da abinda take jiyowa, Jafar ɗin da ta gama haɗa jama'a da motoci zasu tafi tarowa ko kuwa wani daban suke nufi????
*ALBISHIRINKU MATA YAN UWANA YAN KWALISA NAZO MUKU DA WANI DADDADAN LABARI!!!.*
*NASAN KUNDADE KUNA NEMAN FITACCEN GURIN DAZAKUJE AMUKU GYARAN GASHINKU DANA JIKINKU CIKI DA WAJENSA,TO YANXU DAI GA DAMA TA SAMU...*
*LABARI NAKE BAKUFA AKAN AFINTY QUEENS SHAHARARREN SHAGONMU NA SALOON DAYA HADA KOMAI DA KOMAI DA KOWACE MACE YAR KWALISA IRINA KE BUKATA,SANNAN MUNADA KWARARRUN MA'AIKATAN DASUKASAN KAN AIKINKINSU,KUZO AFINTY QUEENS KUBIYA KUDI MUKUMA MU BATA LOKACINMU DOMIN TSATSTSAFO DUK WANI KYAWU NA JIKINKU DA ALLAH YAYI MUKU...*
*A AFINTY QUEENS MUNA AYYUKA KAMAR HAKA:*
*- HAIR SALOON*
*-HENNA*
*-SPA*
*-DUKKAN*
*-PEDICURE*
*-MANICURE*
*-SANNAN MUNA DA TURARUKA IRIN NA AMARE YAN MATA DA KUMA MAI KANKAT DAN UWAR GIDA TA TURARA GIDANTA JIKINTA DAMA KAYAN SAWARTA ITA DA YARANTA,,HARMA ZAWARAWA DUK MUN TANADI KOMAI*
*DOMINSU SUMA*
*-MUNADA SHOES AND BAGS SBD ISASSUN MATAN DA SUKA AMSA SUNANSU MATA*😊
*- MAKEUP NA BRIDAL ND CASUAL...*
*IDAN KINSAN KINAJIN LABARIN SHAGON SALOON NA AFINTY QUEENS AMMA BAKI TABBATAR DA YADDA AIKINSU YAKE BA TO YAR UWA GADAMA TASAMU MEZAKI TSAYA JIRA MAZA KEMA KI ZARGAYO SHAGONMU DAZAN JERA MIKI ADDRESS DINSHI A KASA DOMIN KEMA KI TABBATAR DA KALAR IRIN NAMU KWAZON DA MUKA KWARE AKANSHI GURIN GYARAN JIKIN YAN UWANMU MATA KUMA MUKE GABATAR MUSU DA JAKUNKUNA DA TAKALMA HARMA DA TURARUKAN WUTA DANA SHAFAMA JIKINSU DON NISHADIN ZUCIYARSU DANA MAZAJENSU....*
*AFINTY QUEENS DISCOVER BLISS IN BEAUTY 💅💯*
*Address 👇👇:*
*KU ZIYARCE MU A SHOP NO.9&10 SHEMA PLAZA,BEHIND SHEMA FILLING STATION KASUWAN BACCI KADUNA*
*TEL:08133379628.*
*MATAR MUTUM*
*NA MARYAM FAROUK (UMMU MAHEER*
*FIKRA WRITERS ASSOCIATION*
*LITTAFIN KUDI NE*
*PAY 500 A ASUSUN*
*7061838488*
*OPAY DIGITAL SERVICES*
*MARYAM FAROUK*
OR
*0709290797*
*ACCESS BANK*
*SE A TURA SHAIDAR BIYA ZUWA GA 07061838488*
*IDAN KATINE A DAUKI HOTONSA A TURA ZUWA LAMBAR SAMA VTU KUMA A TURA A 08142548705*
*Kuyi following dina a Arewabooks @Maryamfarouk01 inda zaku karanta wannan littafin tareda sauran littattafaina*
*NAGODE*
*BOOK 2*
*PAGE 7*
"Jafaru, ni uwarka ka yaudara wannan karon ma kace mun biyar na yamma jirginku ze sauka seda na gama tattara jama'a zamu tafi taronka mu nunawa Duniya gatanka shine zaka tozartani Ko La'asar bata rufa ba ka diro a gidannan wato ka sanar da Amadu shi da yake ƙanin ubanka yaje ya dauko ka ko?" Hajiya ta faɗa tana zarewa Jafar idanu. Sakin Yaran Yayyensa da suka ruƙunƙumeshi suna masa oyoyo yayi ya nufeta fuska ɗauke da murmushi cikin shagwaɓa yana cewa
"Haba Hajiyata, dawowana lafiya ai shine komai yanzu, maimakon ki tareni da warm hug se ki farayi mun faɗa kuma?"
"Ka matsoni sena kwasheka da mari wlh, kai kuma me kama da dido dido, sau nawa zan faɗa maka ka fita daga sabgar Jafaru? Shin wai Aisha ta haifamin shine ko Yaya? Nace ka fita daga sabgata data Yayana Amadu amma kaƙi kaji shin ana dolene? To kaji da kunnenka duk bala'i da tuggunku sedai ya ƙare muku amma babu tsafi ko Asirin da zeci Jafaru wlh balle har kuga ya samu nakasu. Ɗaukaka da cigaba a rayuwa yanzu ya fara ganinta duk nasan shirinku da liƙe masan da kakeyi ba wai ban sani ba Asirin da kayi ka lashe masa zuciya ma ina kan karyashi kuma idan na juyo takanka ba zaka ji da daɗi ba"
"Haba Binta wannan wane irin abune kikeyi dan girman Allah? Meye amfanin wannan faɗe faɗen da kikeyi? Jafar dai gashi ya dawo lafiya me kuma kike da buƙata?" Turai ta katse Hajiya daga Hauragiyar da takeyi se kuwa ta zabga mata harara tace
"Babu ruwanki Turai, idan ba zaki tayani ba to kija bakinki kiyi shiru"
"Allah ya sawwaƙa miki, Sannu da zuwa kaji Jafar yi wucewarka can Ɗakinku, idan kuma zaka fara shiga ku gaisa da iyayenka da suka zo tarbarka toh, sannu da hanya" Hajiya Turai da bataji kashedo ba ta faɗa tana nunawa Jafar Palour Binta wanda jama'ar ciki sukayi shiru suna saurar abinda yake faruwa a wajen, Mutan gidan kuwa daman sun san za'a rina dan haka abin bezo musu a bazata ba. Jafar ya kalli Hajiya dake tsaye kamar sojanniya se numfarfashi take tana dannanwa Ahmad da yayi ƙasa da kansa harara, cikin sigar rarrashi Jafar ɗin yace mata
"Please mana Hajiyata, ki saki fuskarki, change of schedule muka samu na flight and na manta ban sanar miki ba. Believe me Yah Ahmad ma be sani ba seda na sauka Kano. You Know i Miss you so much shiyasa ba zan iya jira ba kuzo da yawa ba shiyasa kawai na kirasa nace yazo ya ɗauko ni amma ba laifinsa bane Allah nike da laifi amma kiyi haƙuri bari na koma Abuja kawai gobe sena dawo kizo keda jama'arki ku taroni" ya faɗa bayan daya isa dab da ita. Hararar da takewa Ahmad ta mayar kansa kafin tace
"Billahillazi karka ɗauka kaci banza baka isa ka tozartani a banza Ƙawayena su tafi suna gulmata ba sannan na ƙyakela muje cikin"
"Ai wanan unnecessary drama taki ce zata saka a tafi ana gulmar taki, sabida Allah meye abin tashin hankali a nan? Daman banda ɗaurawa kai ke kika saba taroshi ko yaya? Wlh Yaya Binta bakya gudun abin magana da abin sakawa kai ciwon kai a duniyar nan, duk inda zaman lafiya yake kin ɓauɗe masa" Munira ƙanwarta da batayi niyyar magana ba sedai ganin Abin na Yayartata na neman zarce misali yasa ta fito tana mata maganar. Fuuuu Hajiya ta shige ɗaki Jafar ya kalli Ahmad yace
"I'm sorry Yah Ahmad ni na jawo maka"
"Kaidai jeka kafin Hajiya ta canza maka wannan fuskar taka babu ruwana bari naje wani guri bazan jima ba zan dawo" Ahmad ya bashi amsa yana juyawa ya fice daga gidan.
Dukda yayi ƙoƙarin danne ɓacin ransa Amma Jafar ɗin seda ya fahimta, ya sani dole kalaman Hajiyar su sosa masa rai shi kansa beji daɗi ba amma yasan idanyace wani abu baya ga kalmar lallaɓi da banbaki a yanzu ƙara tunzurata zeyi tayi musu zazzafar Tijara a gaban mutane.
Jiki a sanyaye ya bi bayan Hajiyar, Yaƙe kawai ya ringayi yana gaisawa da tarin matan dake zaune falon Hajiyar, ya so ya gane wasu amma ya manta sunayensu wasu kuma sababbin fuskane a wajensa dan Hajiya badai tara
ƙawaye ba ga Yayayensu da suka kwaso sekace Biki keyi yanzu da tana nufin waɗannan jama'ar zata kwasa su tafi Ɗaukoshi daga Airport ɗin?.
Abinda ya sake ɓata masa rai yanda Yayan Ƙawayen Hajiyar suketa wani abu kamar masu shafar Jinnu, se ɗaukar hotuna suke da video ana sakoshi a ciki wasu ma yaga kamar Live sukeyi a IG suna faɗin gasu a gidansu Jay sunzo taron shi. Ƙasa Ƙasa yake jan tsaki yana durƙushe tsakiyar Mata kowacce da kalar soki burutsun hirar da take jefa masa da tambayoyi kamar sun aikeshi ya dawo, ba Hajiyar ba ba Ƙawayen nata ba babu wadda tayi tunanin a gajiye yake ko yana da buƙatar yaje ya huta seda Hajiya Turai ta fito daga Kitchen taje tana shirya abincin da za'a rabawa Jama'ar da Hajiya ta tara abin Allah arziƙin Jay yau ba Ƙaramin Better tasa aka shirya a gidan ba harda Rago aka gasa.
"Kana tsugunne Jafar ai se Ƙafafunka su gaji tashi kaje ka huta kaida ka shawo tafiya" Turai ta faɗa, ya saci kallon Hajjaju da ta zauna ta haɗe fuska tana juya ƙafa da gani lissafa yanda zataci ubansu daga shi Har Ahmad ɗin daya rusa mata shiri takeyi.
"Tashi kaje mana kake kallona da wasu idonka irin na Ubanku" ta faɗa tana zaburo masa. Ya miƙe yana shafa kai, daidai nan Faisal Bechi ya shigo yana kwalawa Hajiya kira yana cewa
"An fa gama saita komai har Photographer ya iso Allah dai yasa ma a barku ku shiga Airport ɗin irin wannan gayya se kace masu taro Governor.." Se kuma ya dakata saboda ganin Jay a gabansa, ya buga tsalle kamar yaro ya ɗaneshi yana ihu.
"Get off me my friend, kai baka zaka girma da shirme ba ko?" Jafar ya faɗa yana tureshi. Bakin Faisal kamar ze yage yace
"Welcome brother, ni na sani sedai ba Jafar Bechi ba wlh se kayi disappointing Hajiya amma fa ka kwafsa kai kasan irin Grand welcome da aka shirya maka kuwa yau?"
"Matsa na wuce" Jafar ya tureshi jin yana neman ɓallo masa sabon ruwa Faisal yabi bayansa yana kyalkyala dariyar mugunta yana gaya masa irin shirin da Hajiya tayi. Ɗakin Momy ya wuce, tana zaune kan kujera da waya a hannunta tana dannawa Khadija, Aslamiyya da Maimuna duk suna falon suna kallon Tv duk Drama da aka kwasa suna zaune basu fita ba balle su tanka Jafar ya shiga da sallama suka amsa masa a tare kowannensu fuskarsa na faɗaɗa da murmushi.