Sashe 68
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zukudi tayi tana kallonsa tareda sauraron abinda yake cewa,
"Nasan ko a baya bakida matsala da ita, akasi aka samu akan abinda ya faru wanda da bakinki kika furta kin yafe har kika nemi dana dawo da ita kuma nayi matuqar jin dadin hakan, ina fatan zamanku ya canza salo a wannan karom dan zanja mata kunne sosai akan kar a kuma maimaita abinda ya faru a baya".
Murmushi yake yi irin rai fes din nan harya gama maganar, Binta data zama kamar wata hoto se idanu ke motsi suna yawo tsakanin fuskar Audun da bakinsa, so take ta lailayo Ashariya me maiqo sannan ta tambayeshi a gidan kut***r uban wa tace ya maido da Bara'atu sannan dawa yake zaton za'ayi zaman lafiya sedai bakinta ya mata nauyi, bata iya koda motsawa ba seda ya miqe yana mata sallama kan ze koma Kamfani, takun saukarsa daga matakala ne ya farkar da ita daga suman zaunen da tayi ta zabura ta miqe sedai kafin ta kai ga sauka harya fice daga gidan dan tana kaiwa soro taji qarar Motarsa ya bar qofar gidan.
Zaman dabaro tayi ta dora hannu biyu a kai ta zunduma ihu kamar wadda aka aikowa da mutuwar Mahaifinta su Lantana da Mairo suka zaburo dan ganin menene, a dakin Bara'atu ma goggonninta biyu sun niyyaci fita banda Hadiza da Bilki da suka san za'a rina Bilkin ce ta dakatar dasu tana dariya ta cewa Goggo Habi
"Kinga abinda nake gaya miki ko? To yanzu aka fara, Hadiza rufi mana qofar nan dan ba hankali ne da ita ba se ta fado mana be kuma kamata mu biye mata ba dan ko gaban shari'a akaje mu za'a bawa laifi saboda gidanta muka zo"
"Hakane" Hadizan ta fada tana tura qofar ta rufe kamar kuwa sun san nan ta nufo dan zabura tayi kamar zakanya ta durfafi dakin tana kuka tana koro ruwan Ashariya tamkar zararriya ta shiga jijjiqa qofar da niyyar cirera sedai ko Gezau.
"Wallahi tallahi na rantse da girman Allah in baku bude qofar nan ba sena babbake ku a ciki, sena nuna muku ki qananan yan iska ne, ni za'ayiwa haka?" Ta fada cikin qaraji tana cigaba da bubbuga qofa. Dattijai biyun suka tsure, Goggo Habi fadi take
"Me gado a bude qofar nan karta qona mu kinji abinda take cewa"
"Kyaleta Goggo duk kurarin banza ne baki ne da ita babu abinda zata iya a aikace wanda zeyi abu ai baya fada" Hadiza ta bata amsa, Bilki dai bata tanka ba se jera samiru takeyi abinta tana yan waqoqi tamkar ma bata jiyo hauka da Tijarar da Binta takeyi a tsakar gida.
Iyakar masifa, bala'i da duk kalar Ashar wata ma a Bakin Bintan goggonnin Bara'atu suka fara jinta yau seda kamar yanda Hadiza ta fada kurarin banza take dan data gaji da buga qofar gefe ta zube tana kuka kamar me tana maganganu da cin Alwashi kala kala. Mairo data ga abin bana qare bane ta koma kan aikinta ranta duk babu dadi da wannan al'amari, ita kuwa Lantana tana nan tsugunne daga gefenta tun bayan data samu tsarabar hambari a qoqarinta na riqeta ta gwabje mata fuska daga nan ta matsa gefe amma taqi tashi daga gurin se fadi take
"Kiyi haquri Hajiya, ki tashi mu koma can daki kisha ruwan sanyi"
"Se naci "gi***n du***in uwarki Lantana idan kika sake cewa nayi haquri, Allah ya tsinewa haqurin kema Allah ya tsine miki" ta fada dole Lantana taja baki ta kame tana sosa fuska dan inda ta mangaretan har sannan be dena mata zafi ba tsabagen neman gurin zama da iya gulma yasa take zaune a gurin har sannan.
Binta na kuka wiwi kamar Jifa se ga Turai ta shigo gidan ita da wata mata, tun daga qofar gida ake jiyo ihu da kururuwar Bintan dan haka cikin sauri suka shigo dan ganin me yake faruwa.
"Na shiga uku ni Amina, me ya faru? Waya mutu Binta?" Turai ta fada tana nufar qawar tata da ta ke nan zaune kamar kayan wanke ta miqe qafafu kanta ya tuje dan tun fara Tijarar tata dankwali ya cire. Qoqarin kamata ta shigayi danta miqe amma ta kasa saboda yanda ta saki jiki ita aba ba kadab ba ganin Turan kuma yasa ta sake sakin wani kukan me ban takaici kamar wata yarinyar goye tana fadin
"Na shiga uku Turai Audu ya kasheni, wai Bara'atu ya mayar be gaya mun ba"
"Har naji sanyi a raina ashe ba mutuwa akayi ba, dan Allah kama jikinki ki miqe, Zainab zoki tayani mu dagata" Turai ta fada jin abinda Binta tace. Dakuar da sidin goshi bayan sun hadu su uku harda Lantana suka kai Binta daki se sannan ma suka tuna da Yaron da suka baro a daki ya fado daga Kujerar data kwantar dashi yana ta tsala kuka gwanin Tausayi.
"Dauke shi Dan Allah kuje waje ki rarrashe shi" Turai ta fadawa Lantana, ta dauke Nazirun tayi waje dukda ba haka taso ba, so tayi taji komai dukda ta tsinci kan zancen amma zata so ayi komai a gabanta yanda zata fi jin dadin bata labari idan ta fita.
"Yanzu saboda Allah me kikayi haka? Akan wata baquyiyar Bara'atu shine kika kwanta tsakar gida gaban masu aikin ki kina tumami kamar wadda ta kwace daga Turu wani irin abin kunya ne wannan Binta?" Turai ta fada cikin fushi. Binta dake kuka tace
"Ki qyaleni, saboda ba'a taba miki kishiyar nan bane shiyasa duk abinda nayi kike daukarsa shirme ke kinsan zafin abin ne balle ki gane yanda nake ji?"
"Koma menene, kome kikeji be kai ki zauna kina zubarwa da kanki mutunchi ba a samu abin fada akanki, wannan haukan da kikayi wlh Allah yasan inda ze tsaya dan wannan munafukar me aikin naki kina kallonta kinsan nadar rahoto takeyi. Allah na tuba ba Bara'atu ba ko mata uku Audu yace ya daura aure dasu ya kai ki kwanta kina kuka akai balle Bara'atun da ko kashin jikinki ya fita a gurinki, har meye abin tashin hankali a matar da kika san idan kinga dama ko ruwa ba zaki barta tasha da dadi a cikin gidan nan ba.
Kika kara da Zubaida ma kika koreta balle Bara'atu karan kada miya? Dan Allah karki bada ni mana, a gaban Audun kikayi wannan haukar ai kuwa kin kashe kanki kin ruguza duk wani shirinki na baya da wanda ya kamata muyi a gaba wlh murus kin kashe kanko a gurinsa".
A hankali ta fara rage kukan da take tana kallon Turai alamar sonjin qarin bayani, ta yaya ta kashe kanta a gurin Audu ta ruguza shirinta ma baya dana yanzu?"
"Wai ma tukunna, ta ya akayi har ya maida ta baki sani ba?" Turai ta jefa mata tambayar, taja Dankwalinta da aka tsinto mata a Soro ta face majina kafin ta shiga bawa Turai Labarin yanda sukayi kan zancen maido da yara sa dalilinta nayin hakan har zuwa kan zuwansu Bilki da maganar da sukayi dashi dazun.
"Tirqasa, au yanzu suna cikin gidan nan kikayi wannan abin kunyar gaskiya Binta baki haduba kwakwata kin bada ni wlh sauqinta daya be ga wannan qaramin haukan naki ba dan wlh da ace yana nan kikayi shikenan kin gama yawo babu wata fankama da zaki sake yi masa ya yarda" Turan ta sake fada kafin ta muskuta tayi qasa da murya taci gaba da magana.
Se bayan sallar Isha'i su Turai suka bar gidan bayan sun tattauna batutuwa da yawa da Bintan tareda matar da suka zo tare, jan kunne tayi mata sosai akan abinda suka tattauna ta fito ta rakosu zuwa sannan zuciyarta ta danyi sanyi kadan. Ta kalli dakin Bara'atun ta ciji yatsa, ta ci Alwashin seta gwammace mutuwarta da dawowa gidan Audu, zaman da sukayi a baya sharar fage ne yanzu ne zata nuna mata Asalin ita din wacece ta shayar da ita ruwan azabar da ko kallon inda Audu yake aka ce ta yi ba zata yarda ba.
Tana tsaye tsajar gidan bayan ta rakosu Turai Bilki ta fito sukayi wa juna kallon tara saura ta wuce Abinta bakin famfo ta bar Binta da jan qwafa. Kaf setaci uwarsu wlh a sannu zatayi maganinsu. Se yanzu kam taga baiken kanta data kasa riqe kanta tayi shirmen dazu ai su Bilkin zasu qara rainata su tafi da ita a baki amma ta gode Allah da batayi a idon Audun ba. Tana hawa Barander yayi sallama, ji take kamar ta qunduma ashar a maimakon amsa masa amma ta dake iya dakiya ta amsa sedai bata iya ta tsaya ba balle ta juyi ta masa sannu da zuwa ta shige daki tana jiyo shi suna magana da Bilki kusan minti biyar kafin yabi bayanta.
"Uwargida ran gida ko Amarya zance?" Ya tsokaneta yana zama akan kujera tace
"Uhm" kawai tana cirewa Naziru Nafkin.
"Yau sarautar ta motsa kenan?" Ya sake sako mata wasa ta daure ba tareda ta kalleshi ba tace
"To kai ya ka gani?"
"Ras" ya fada kafin ya laluba Aljihunsa ya zaro wata Farar Embelop me dan girma ya miqa mata se sannan ta kalle shi ta saka hannu ta karba tana budewa, Awarwaro ne guda hudu a ciki na zinari, ta hadiye yawu Aljanunta na son abin duniya suka motsa.
"Tukuici ne, ko ince sadakin fadar kishiya ne" Audun ya fada.
Maganar Turai ta dazu ta fado mata da tace
"Ki kwantar da hankali kiyi masa laka laka irin yanda kikayi sanda kika shigo gidan, kina kallon dai wahalar da kikasha lokacin daya Auro Zubaida ta isheki ishara kisan tashin hankali ko masifa ba zata biyar da Audu ba sedai lallashi da kwantar da kai ta hakane zaki moreshi sannan ki samu biyan buqatarki to tabbas ta fara ganin gaskiyar hakan.
"Nasan ko a baya bakida matsala da ita, akasi aka samu akan abinda ya faru wanda da bakinki kika furta kin yafe har kika nemi dana dawo da ita kuma nayi matuqar jin dadin hakan, ina fatan zamanku ya canza salo a wannan karom dan zanja mata kunne sosai akan kar a kuma maimaita abinda ya faru a baya".
Murmushi yake yi irin rai fes din nan harya gama maganar, Binta data zama kamar wata hoto se idanu ke motsi suna yawo tsakanin fuskar Audun da bakinsa, so take ta lailayo Ashariya me maiqo sannan ta tambayeshi a gidan kut***r uban wa tace ya maido da Bara'atu sannan dawa yake zaton za'ayi zaman lafiya sedai bakinta ya mata nauyi, bata iya koda motsawa ba seda ya miqe yana mata sallama kan ze koma Kamfani, takun saukarsa daga matakala ne ya farkar da ita daga suman zaunen da tayi ta zabura ta miqe sedai kafin ta kai ga sauka harya fice daga gidan dan tana kaiwa soro taji qarar Motarsa ya bar qofar gidan.
Zaman dabaro tayi ta dora hannu biyu a kai ta zunduma ihu kamar wadda aka aikowa da mutuwar Mahaifinta su Lantana da Mairo suka zaburo dan ganin menene, a dakin Bara'atu ma goggonninta biyu sun niyyaci fita banda Hadiza da Bilki da suka san za'a rina Bilkin ce ta dakatar dasu tana dariya ta cewa Goggo Habi
"Kinga abinda nake gaya miki ko? To yanzu aka fara, Hadiza rufi mana qofar nan dan ba hankali ne da ita ba se ta fado mana be kuma kamata mu biye mata ba dan ko gaban shari'a akaje mu za'a bawa laifi saboda gidanta muka zo"
"Hakane" Hadizan ta fada tana tura qofar ta rufe kamar kuwa sun san nan ta nufo dan zabura tayi kamar zakanya ta durfafi dakin tana kuka tana koro ruwan Ashariya tamkar zararriya ta shiga jijjiqa qofar da niyyar cirera sedai ko Gezau.
"Wallahi tallahi na rantse da girman Allah in baku bude qofar nan ba sena babbake ku a ciki, sena nuna muku ki qananan yan iska ne, ni za'ayiwa haka?" Ta fada cikin qaraji tana cigaba da bubbuga qofa. Dattijai biyun suka tsure, Goggo Habi fadi take
"Me gado a bude qofar nan karta qona mu kinji abinda take cewa"
"Kyaleta Goggo duk kurarin banza ne baki ne da ita babu abinda zata iya a aikace wanda zeyi abu ai baya fada" Hadiza ta bata amsa, Bilki dai bata tanka ba se jera samiru takeyi abinta tana yan waqoqi tamkar ma bata jiyo hauka da Tijarar da Binta takeyi a tsakar gida.
Iyakar masifa, bala'i da duk kalar Ashar wata ma a Bakin Bintan goggonnin Bara'atu suka fara jinta yau seda kamar yanda Hadiza ta fada kurarin banza take dan data gaji da buga qofar gefe ta zube tana kuka kamar me tana maganganu da cin Alwashi kala kala. Mairo data ga abin bana qare bane ta koma kan aikinta ranta duk babu dadi da wannan al'amari, ita kuwa Lantana tana nan tsugunne daga gefenta tun bayan data samu tsarabar hambari a qoqarinta na riqeta ta gwabje mata fuska daga nan ta matsa gefe amma taqi tashi daga gurin se fadi take
"Kiyi haquri Hajiya, ki tashi mu koma can daki kisha ruwan sanyi"
"Se naci "gi***n du***in uwarki Lantana idan kika sake cewa nayi haquri, Allah ya tsinewa haqurin kema Allah ya tsine miki" ta fada dole Lantana taja baki ta kame tana sosa fuska dan inda ta mangaretan har sannan be dena mata zafi ba tsabagen neman gurin zama da iya gulma yasa take zaune a gurin har sannan.
Binta na kuka wiwi kamar Jifa se ga Turai ta shigo gidan ita da wata mata, tun daga qofar gida ake jiyo ihu da kururuwar Bintan dan haka cikin sauri suka shigo dan ganin me yake faruwa.
"Na shiga uku ni Amina, me ya faru? Waya mutu Binta?" Turai ta fada tana nufar qawar tata da ta ke nan zaune kamar kayan wanke ta miqe qafafu kanta ya tuje dan tun fara Tijarar tata dankwali ya cire. Qoqarin kamata ta shigayi danta miqe amma ta kasa saboda yanda ta saki jiki ita aba ba kadab ba ganin Turan kuma yasa ta sake sakin wani kukan me ban takaici kamar wata yarinyar goye tana fadin
"Na shiga uku Turai Audu ya kasheni, wai Bara'atu ya mayar be gaya mun ba"
"Har naji sanyi a raina ashe ba mutuwa akayi ba, dan Allah kama jikinki ki miqe, Zainab zoki tayani mu dagata" Turai ta fada jin abinda Binta tace. Dakuar da sidin goshi bayan sun hadu su uku harda Lantana suka kai Binta daki se sannan ma suka tuna da Yaron da suka baro a daki ya fado daga Kujerar data kwantar dashi yana ta tsala kuka gwanin Tausayi.
"Dauke shi Dan Allah kuje waje ki rarrashe shi" Turai ta fadawa Lantana, ta dauke Nazirun tayi waje dukda ba haka taso ba, so tayi taji komai dukda ta tsinci kan zancen amma zata so ayi komai a gabanta yanda zata fi jin dadin bata labari idan ta fita.
"Yanzu saboda Allah me kikayi haka? Akan wata baquyiyar Bara'atu shine kika kwanta tsakar gida gaban masu aikin ki kina tumami kamar wadda ta kwace daga Turu wani irin abin kunya ne wannan Binta?" Turai ta fada cikin fushi. Binta dake kuka tace
"Ki qyaleni, saboda ba'a taba miki kishiyar nan bane shiyasa duk abinda nayi kike daukarsa shirme ke kinsan zafin abin ne balle ki gane yanda nake ji?"
"Koma menene, kome kikeji be kai ki zauna kina zubarwa da kanki mutunchi ba a samu abin fada akanki, wannan haukan da kikayi wlh Allah yasan inda ze tsaya dan wannan munafukar me aikin naki kina kallonta kinsan nadar rahoto takeyi. Allah na tuba ba Bara'atu ba ko mata uku Audu yace ya daura aure dasu ya kai ki kwanta kina kuka akai balle Bara'atun da ko kashin jikinki ya fita a gurinki, har meye abin tashin hankali a matar da kika san idan kinga dama ko ruwa ba zaki barta tasha da dadi a cikin gidan nan ba.
Kika kara da Zubaida ma kika koreta balle Bara'atu karan kada miya? Dan Allah karki bada ni mana, a gaban Audun kikayi wannan haukar ai kuwa kin kashe kanki kin ruguza duk wani shirinki na baya da wanda ya kamata muyi a gaba wlh murus kin kashe kanko a gurinsa".
A hankali ta fara rage kukan da take tana kallon Turai alamar sonjin qarin bayani, ta yaya ta kashe kanta a gurin Audu ta ruguza shirinta ma baya dana yanzu?"
"Wai ma tukunna, ta ya akayi har ya maida ta baki sani ba?" Turai ta jefa mata tambayar, taja Dankwalinta da aka tsinto mata a Soro ta face majina kafin ta shiga bawa Turai Labarin yanda sukayi kan zancen maido da yara sa dalilinta nayin hakan har zuwa kan zuwansu Bilki da maganar da sukayi dashi dazun.
"Tirqasa, au yanzu suna cikin gidan nan kikayi wannan abin kunyar gaskiya Binta baki haduba kwakwata kin bada ni wlh sauqinta daya be ga wannan qaramin haukan naki ba dan wlh da ace yana nan kikayi shikenan kin gama yawo babu wata fankama da zaki sake yi masa ya yarda" Turan ta sake fada kafin ta muskuta tayi qasa da murya taci gaba da magana.
Se bayan sallar Isha'i su Turai suka bar gidan bayan sun tattauna batutuwa da yawa da Bintan tareda matar da suka zo tare, jan kunne tayi mata sosai akan abinda suka tattauna ta fito ta rakosu zuwa sannan zuciyarta ta danyi sanyi kadan. Ta kalli dakin Bara'atun ta ciji yatsa, ta ci Alwashin seta gwammace mutuwarta da dawowa gidan Audu, zaman da sukayi a baya sharar fage ne yanzu ne zata nuna mata Asalin ita din wacece ta shayar da ita ruwan azabar da ko kallon inda Audu yake aka ce ta yi ba zata yarda ba.
Tana tsaye tsajar gidan bayan ta rakosu Turai Bilki ta fito sukayi wa juna kallon tara saura ta wuce Abinta bakin famfo ta bar Binta da jan qwafa. Kaf setaci uwarsu wlh a sannu zatayi maganinsu. Se yanzu kam taga baiken kanta data kasa riqe kanta tayi shirmen dazu ai su Bilkin zasu qara rainata su tafi da ita a baki amma ta gode Allah da batayi a idon Audun ba. Tana hawa Barander yayi sallama, ji take kamar ta qunduma ashar a maimakon amsa masa amma ta dake iya dakiya ta amsa sedai bata iya ta tsaya ba balle ta juyi ta masa sannu da zuwa ta shige daki tana jiyo shi suna magana da Bilki kusan minti biyar kafin yabi bayanta.
"Uwargida ran gida ko Amarya zance?" Ya tsokaneta yana zama akan kujera tace
"Uhm" kawai tana cirewa Naziru Nafkin.
"Yau sarautar ta motsa kenan?" Ya sake sako mata wasa ta daure ba tareda ta kalleshi ba tace
"To kai ya ka gani?"
"Ras" ya fada kafin ya laluba Aljihunsa ya zaro wata Farar Embelop me dan girma ya miqa mata se sannan ta kalle shi ta saka hannu ta karba tana budewa, Awarwaro ne guda hudu a ciki na zinari, ta hadiye yawu Aljanunta na son abin duniya suka motsa.
"Tukuici ne, ko ince sadakin fadar kishiya ne" Audun ya fada.
Maganar Turai ta dazu ta fado mata da tace
"Ki kwantar da hankali kiyi masa laka laka irin yanda kikayi sanda kika shigo gidan, kina kallon dai wahalar da kikasha lokacin daya Auro Zubaida ta isheki ishara kisan tashin hankali ko masifa ba zata biyar da Audu ba sedai lallashi da kwantar da kai ta hakane zaki moreshi sannan ki samu biyan buqatarki to tabbas ta fara ganin gaskiyar hakan.