← Book details Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 60 OF 137

Sashe 60

Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Zata iya bada shaidar Audun yana salloli na farilla kuma yana qoqarin yinsu akan lokaci kuma cikin jam'i, a zamansu daya tasamma shekara a watan Azumi kadai zata bada shaidar yana zuwa sallar Tarawi da kuma Qiyamullaili tun bayan daya shude kuma a ranakun girkinta dai bata sake ganin yayi ba bata sani ba ko idan yana dakin Binta. Dama shi bame jurar Ibadar Azumi bane domin Ramadanan ma da qyar yake kaishi, bayan Alqur'ani bata tsammaci ya karanta wani littafi ba bata taba ganinsa dashi ba haka ko a magana ba zatace ga inda ya kawo misali daga cikin Hadisi ko wani littafi na Addini ba. Ba zata manta ba akwai sanda ta taba shawartarsa shiga karatun Asuba da akeyi a masallacin dake cikin layinsu wani baqon babban Malami ne yazo yake bada karatun Fiqhu da Hadisi se Tauhidi take yace mata ai ya gama karatu, seda ya shekara biyar yana qolanta to wane karatu ya rage masa da beyi ba kuma?
Da tace ita zata ringa zuwa gurin matar Malamin da take karantar da Mata a cikin gida harya yarda bata san ya akayi ba ya dawo yace babu maganar ta tambayi dalili kuma yace babu dole ta haqura badan taso ba domin Allah ya sani tana sha'awar ta nemi ilimi shiyasa yanzun data samu wannan damar tayi amfani da ita.

Dada take ja tana biya mata karatun, dayake tasan baqi dan haka karatimu da takardar Alqur'ni be bata wahala sosai ba dukda tafi gane rubutun warshu amma da yake ta saka kanta se gashi tana ganewar in ta biya mata kuma ta ringa nanatawa kenan har seta haddace. Balaraba ce ta sameta akan ta ringa fitowa suna daukar karatun tare bayan da Dada ta sanar mata tana yiwa Inna Zubaidan qarin karatu, daga nan itama ta zama yar Aji ta kuma maida hankali sosai akan abinda ake koya mata. Irin nutsuwar da take tsintar kanta a ciki ta qara tabbatar mata da cewar tabbas akwai banbanci me tarin girma tsakanin rayuwar da akeyinta cikin sani da kuma ta jahilci.

Satinta uku a gidan wata safiya ta tashi da naquda, kafin nan sunje Asibiti har sau biyu Yakubu da kansa ya kaisu tareda Balaraba an dubata an kuma tabbatar da lafiyarta data abinda yake cikinta suka basu kwana goma daya zagayo suka koma kwanaki biyu kenan da zuwan nasu da safiyar ranar Laraba ta tashi da naquda nan da nan suka wuce Asibiti da ita, daman Yakubu yana nan ya jinkirta komawarsa Ikko saboda yana taraddadin ya zasuyi idan haihuwr tazo mata cikin dare gida babu Namiji daga ita se Balaraban dalilin daya saka ya daga tafiyarsa kenan saboda a Asibiti zuwansu na farko sun bashi tabbacin ba zata qara sati biyu nan gaba bata haihu ba gashi kuwa kwanaki goma sha biyu kenan da wanacn zuwan haihuwar tazo.

Cikin taimakon Allah bata dauki lokaci mai tsaho ba ta sauka, ta haifo wasu runtuma runtuman tagwaye wanda ko a Da guda daya aka haifi wannan tabbas se an jinjinawa wadda ta santaloshi se gashi har biyu ubangiji ya bata a sauqaqe cikin Aminci. Lokacin da aka nunawa Yakubu yaran kasa cewa komai yayi se tasbihi daya ringayi a zuciyarsa. Duk wanda yasan Ahalin gidansu baya buqatar a fada masa yaran tsatsonsu ne ze iya cewa ma ba'a taba haifar Jarirai masu kama da Mahaifinsu Malam Tijjani Kwabo da kwabo irin wadannan ba har hasken fatarsa basu bari ba abinda ya banbantasu da Audu kenan saboda shi yana da duhu kadan.

Ya rasa ta ina ze fara ma, Balaraba nata murna ta kasa tsayuwa guri daya shi kuwa tunanin waze fara shaidawa zancen haihuwar yake tayi. Gadai Arziqi Allah ya basu wadannan ne tagwaye na farkoba zuri'ar gidansu amma haihuwar su tazo cikin rudani. Seda ya tabbatar babu abinda ake da buqata a Asibitin kafin yacewa Balaraba zeje ya dawo.

Can kamfanin da Audu yake ginawa inda kuma nan su Musbahu suke zama ya nufa. Yaci sa'ar tarar da Musbahun be tafi gidan Mai ba, bayan sun gaisa yace yazo ya rakashi gidansu Zubaida Amaryar Audu babu musu ya hau mota suka tafi a ransa yana mamakin meyake faruwane domin a kwanakin nan gaba daya sun lura da Baba Audu baya cikin hayyacinsa dukda be fada musu komai da yake damunsa ba amma ko gidan Mai seya kwana biyu be fito ba aikin Kamfanin ma an dakatar dayi kamar yanda ya fada yana cikin wani dan uzuri ne.

Da suka isa gidan a Mota ya bar Musbahu ya qara qofar daya nuna masa a mazaunin ta gidan Malam Hassan. Yayi sallama cikin sa'a Malam din ya fito ya amsa a shirye yake da alama wani gurin zashi, be taba ganin Yakubu ba amma jini da kamannin fuska yasa ya gane dan uwan Audu ne dan haka yayi masa iso cikin gida bayan ya saka Baba Zayya tayi musu shimfida ta kawo masa ruwa a mutunce suka gaisa suna tambayarsa iyali.

Cikin nutsuwa da kuma sanin makamar aiki irin nasa ya warwarewa Malam Hassan duk abinda ake ciki be boye masa komai ba hatta da sakin da Audun yayiwa Zubaida da zamanta a gidansa zuwa yanzun data haihu be rage komai a ciki ba. Malam Hassan yayi shiru cikin tsantsar jimami kafin yace

"Tabbas nayi zargin wani abu ya faru saboda irin zaryar da dan uwanka ya ringayi a gidan nan kuma alamu na rashin gaskiya sun bayyana tattare dashi sedai na kyautata masa zato na cewar koma menene nasan baze cutar mun da Zubaida ba na saka a raina dai wata matsala ce qila da yake jin nauyin sanar dani. Hatta zuwan da zayya tayi ni na turata domin taje ta ga halin da suke ciki qila mu iya gano bakin zare sedai ya tabbatar mata da cewar ya tura Zubaidan can garinku, tabbas wannan maganar ta tayar mana da hankali hat shaidan yaso yayi wasa da zuciyata ya darsa mun zargin wani al'amari na daban amma na yaqe shi da qarfin addu'a ban kuma gusa ba kullum cikin yinta nakeyi ina roqon ubangiji da koma menene yake faruwa ya bayyana mana ya kuma sauqaqa mana.

Na godewa Allah da Jarabawar ta tsaya iyakar haka, na kuma gode maka da kayi mun wannan arziqin na riqe Zubaida a hannunka harta haihu ubangiji ya wanketa daga zargin da dan uwanka yakeyi mata na taje masa gida da Dan da ba nasa ba. Yanzu data haihu a hannunka ze iya tantance kamanceceniyar da take tsakaninsa da abinda aka samu kuma ya iya nutsuwa yayi lissafi na kwarai sabanin idan ana nan ta haihu tunda har ya rigada ya yarda da cewar Boka ko Malamin tsubbu na iya aikata komai la shakka yace itama kamannin dake tsakaninsa da abinda aka haifa qirqirarta akayi".

"Hakane Baba ina kuma qara baku haquri akan abinda ya faru In sha Allahu ma komai ze daidaita base har Zubaida ta dawo gida ba daga can gurina zata sake komawa dakinta da yardar Allah kuma abinda yasa nazo na sanar muku da abinda ake ciki saboda ku mahaifantane kuna da haqqi akanta be kamata kuma ace mun rufeku akan babban Al'amari irin wannan ba" Yakubu ya sake fada. Malam Hassan yayi murmushin daya fi kuka ciwo yace

"Kayya yaro dena wannan magana kuma ai zancen kome babu shi Aure ya qare sedai muyi fatan ubangiji ya musanyawa kowannensu da Mafi Alkhairi a gareshi. Kamar yanda rayuwar data faru a baya ta shude muka yarda da qaddara wannan ma mun dauka, rabon wadannan bayin Allah yayi sanadiyyar wannan Auran, tsakaninmu da Abdullahi kuma har abada babu abinda zamu ce masa sedai fatan Allah ya dubeshi ya saka masa da Alkhairi kwatankwacin wanda yayi mana. Maidomun da Zubaida gida da yayi ya isheni komai a duniya wlh kuma wannan al'amari daya faru baze goge tarin Alkhairinsa na baya a idona ba, wata Jarabaqar ce daga ubangiji kuma idan munyi haquri zamu cinyeta".

Yakubu be ja maganar da nisa ba yayi masa sallama bayan ya roqi Baba Zayya data shirya su tafi Asibiti tare ya kuma sake roqar Malam din da maganar ta zama sirri tsakaninsu. A hanya Baba Zayya ta samu bakin zazzage masa buhun bala'in da bata iyayi gaban Malam Hassan ba kai kace shine Audun, shidai be tanka mata ba domin sunada duk wata dama ta suyi fada dan an bata musu.

*MAMAN MARYAM ONLINE BUSSINESS*

*Ina kuke Mata Yan kwalisa , Ina nufin isassun Mata ,Wai shin Kuna da labarin shahararren company nan namu na GHT wato good healthtreatments*
*Wanda yazo muku da fitattu Kuma* *ingantatattun suppliment ,na dukkan matsalolin ku*❓

*Ina maisan tayi kyau,irin na isassun Mata ya fitar Miki da shef dinki tayi Miki gyara in and out ,nemi royal jelly dinmu na company GHT*
*Wanda aka yishi da xuma ,kundai San amfanin Zuma basai na fada miku ba , hajiya ta kixo ki Yi gyara domin ki kerewa sa,a kije taro ko baki da ko sisi kiji Ana rangada Miki hajiya , saboda yanda Zaki Kara kwarjini ,kina walwali acikin mutane , magungunan ght anti agen ne suna maida tsohuwa* *yarinya ,yarinya Kuma ta koma jaririya*

*Muna da magunguna iri iri*

*NA GYARAN JIKI*
*NA GOGE NANKARWA*
*NA RAGE QIBA*
*NA CIRE TUMBI*
*NA QARIN HIPS*
*NA GIRMAN BREAST*
*NA QARA TSAHON GASHI*

*NA QARIN NI'IMA WANDA ZAI SAUKAR MIKI DA NI'IMA YA QARA MIKI DADI DA ZAQI A GURIN OGA*

*Muna da hadin bita zai zai ,indai kishiyar ki tana Shan magungunan GHT, tohh lallai sunan ki sorry domin kuwa tazarar dake tsakanin ku kamar tazarar sama ne da kasa*

*Muna da Wanda zai matseki ciki da waje Andai na yayin dinki uwargida*,

*Sannan company mu na GHTBai tsaya anan ba*
*Ya kawo muku maganin dukkan matsalolin ku*

*INA MASU HAWAN JINI?*
*INA MASU CIWON ZUCIYA?*
*INA MASU CIWON QODA?*
*INA MASU CIWON HANTA?*
*INA MASU SICKLER?*
*INA MASU HIV?*
*INA MASU CANCER?*
*INA MASU NEMAN HAIHUWA?*

*Tohh Ku matso GHT taxo muku da magungunan matsalolin ku*
*Kuma muna da testimonys da yawa ,na wadanda suka gwada suka da ce*

*Munanan a KANO KUNTAU*
*Kuma muna tura Kaya ko wanne gari cikin aminci da gaskiya , kuma kayan mu muna badashi ne cikin price Mai rahusa ga kyau ga inganci sannan ga Rahusa*
Chapter 60 · 0% Book details