Sashe 1
Matar Mutum Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
*page 1*
"Wallahi Allah shine shaidata bani da masaniya akan yanda akayi kudin nan suka bata. Kowa a nan ya gani ga lissafi nan na duk abinda ya shigo kuma ya fita saga duka companies dinmu tun farkon shekara zuwa yanzu. Idan har duka lissafin da accountants dinmu suka kawo daidai ne tayaya za'ayi ace yanzu an sake lissafi an rasa wasu kudade? Nidai ban ci ba sedai a sake lissafi tun daga qasa ta yuwu a nan aka samu kuskuren lissafi" AMINU BECHI ya fada cikin tsananin tashin hankali. Sati biyu kenan da al'amura suka rikice a BECHI GROUP OF COMPANY lokacin lissafin shekara yayi bayan daya gama hada komai a matsayinsa na AG lissafi yasha banban da abinda aka bashi a rubuce da kuma tsurar kudi da suke a qasa inda aka samu rarar naira na gugan naira har Miliyan dubu biyu da dari biyar (2.5Billion) wadda bayan bashi damar yayi bincike da MD da kuma Chairman sukayi yauce ranar da aka taru duk wani daya isa a company domin jin ta yanda akayi aka haihu a ragaya.
Alhaji ZAKARIYYAH BECHI dake ta jujjuyawa a kujerarsa yana wani miskilin murmushi da babu wanda ya tantance kona menene ya kalle shi yace
"To Aminu kaida kanka kace dukka lissafin da aka gabatar maka daidai suke kuma baka karba ka saka hannu har seka bincika komai ka tabbatar da haka yake. Sannan a iya saninmu ku biyu kuke da access da central account dinmu dakai da Chairman duk wani wanda ze shigar ko fitar da kudi bayan ku biyun seya samu approval a gurinku to tayaya kake zaton zamu yarda idan kudi ya bata kuma kace mana bakada masaniya akai kenan Chairman ne da kanshi ya kwashi kudaden ko kuma me kake nufi?"
Aminu ya kalli Chairman din da tun zamansu bece komai ba ya tallabe haba da hannaye biyu yana bin duk wani da yayi magana a cikin su da kallo, Dattijo ne da a qalla zeyi shekaru 70 zuwa sama, dukda a zaune yake amma kana kallonsa zaka san Zabgegen mutum ne Jindadin rayuwa yasa har yanzun yake da sauran kwarinsa. Aminu ya hadiye yawu muqut saboda yanayin fuskar Chairman daya gani, bashi da yawan fara'a daman amma kuma yanayinsa na yau ya banbanta da kullum kana gani kasan zuciyarsa a kusa take koda yake ai dole, batun kudi akeyi fa, kudin daya qare rayuwarsa yana nemansu ya tara ace lokaci daya wasu su ringayi masa zari daidai dole hankalinsa ya tashi.
Seda ya daidaita nutsuwarsa kafin ya kalli MD dake jiran jin ta bakinsa yace
"Nidai na gama magana, ban ci kudin nan ba ban kuma san wanda ya dauke su ba. Amma dai kamar yanda nace kowanne gida (sector) su sake turo mana da lissafinsu na shekara a qaramun lokaci zan sake bin komai daki daki zan zauna da duka Bank Managers dinmu in Allah ya yarda za'a gano duk ma inda kudin suka shiga" ya qarasa muryarsa na rawa kuma cike da roqo da yaqinin Alhajin ya yarda dashi ya bashi wannan damar. Idan ya rasa besab ina ze dosa ba, abu biyu ne dole daya ya faru, dukda kasancewar Dan Chairman na cikinsa a sabgar Company basa kawo wannan relation din, ya sani kodai yayi Aman kudaden nan tas Miliyan dubu biyu da dari biyar wanda ko an siyar dashi da matarsa da yayansa da abinda ya mallaka baza'a hada wannan kudi ba abu na biyu kuma in wancan be samu ba yasan garqameshi za'a yi a prison still kuma A siyar da duk abinda ya mallaka Company ya rage Asara maganar aikin sa daman tun ranar da kudin sukayi batan dabo ya rubuta resignation letter ya ajiye dan ko be bari ba korar sa za'ayi.
"Maganar wani lokaci ko a sake bincike duk bata taso ba dan a tsayin faruwar abun zuwa yanzu da da wani abu da zakiyi tuni kayishi, just admit it Aminu kai kaci kudaden nan ka dawo dasu baki alaikum base magana tayi tsayi ba" NAZIRU BECHI ya fada yana wani zazzare masa ido
"Nima dai abinda na gani kenan, idan kuma yayi taurin kai Maigirma Chairman ina ganin a barshi da Legal department suyi aikinsu nasan su zasu sna ta yanda zasu tirsasashi yayi aman kudin ko kuma su miqashi inda ya dace" Alhaji Zakariyya ya qarasa miyar gishiri, cikin Aminu ya kada, ya ringa raba ido tsakanin Alhaji BABANGIDA BECHI da kuma YAKUBU BECHI da yake matsayin mataimakinsa AAG wanda tun fara taqaddamar kamar ma baya gurin wayarsa yake dannawa kunnensa saqale da Bluetooth tabbacin ba jinsu yakeyi ba hakan yasa ya tsayar da idonsa kan Alhaji Babangida cike da roqon ya saka baki amma seyaga ya saukar da kansa qasa bece komai ba.
Dakin ya sake daukan shiru na wani lokaci kafin cikin murya me cike da Izza irin ta wanda suka ci suka tada kai Chairman, Alhaji AUDU BECHI ya fara magana yana cewa
"Duk naji bayanan ku kuma na duba takaddun da aka rigada aka gabatar mun tuntuni. Account general, ina so daga yanzu zuwa qarfe biyu ka gabatar da takaddar barin aikinka da kanka saboda idan muka koreka zamu bata maka career be zama lallai ka sake samun aiki a wani gurin ba, kudi kuma duk wanda ya dauka yaje dan kansa" yana gama fadar haka ya tsuke bakinsa yana kallonsu daidai.
Aminu ya sauke ajiyar zuciya me nauyi tamkar wanda ya hadiyi kunama, jiki da bakinsa suna rawa ya zame daga kan kujerarsa ya durqushe yana cewa
"Nagode Alhaji, Allah ya qara girma nagode nagode".
Naziru da Zakariyya wanda farkon maganar Alhaji yayi musu dadi, sun dana kuma ta kama suka kalli juna tareda yin signa akan idon Alhaji Babangida dake lura da duk wani motsinsu ya girgiza kai kawai. Bazeyi kaffara ba idan ya rantse cewar shirinsu ne saboda sun nuna baqin ciki qarara da kujerar ta Aminu amma baze saka baki a cikin maganar na domin rayuwar gidansu rayuwa ce irin ta kowa tasa ta fishsheshi shida Yan dakinsu. Tunda Aminu ya samu wannan matsayi qarara mutane da yawa a gidan suka nuna qyashi da hassada bayan rasuwar Mr Adekunle Balogun wanda shine AG na BECHI GROUP din tun kafuwarsa Alhajin bisa shawarar Legal Department da sukaga cancantar Aminun aka dorashi, shekaru biyu kenan tun kuma hawansa abubuwan da ba'a saba dasu ba suke faruwa amma wannan al'amari shine mafi girma wanda baze yuwu a dauke kai ba.
Cikin zafin ran dake nuna hassada qarara Alhaji Zakariyya yace
"Ranka ya dade (haka suke kiransa muddin sabgar data shafi aiki ce) naji kace yayi resigning kawai banji maganar dawo da kudi ba ko wani hukunci da za'a dauka akansa?"
"Da alama kunnenka ya soma samun matsala ko? To ka tambayi na kusa da kai su maimaita maka abinda nace, maganar wanda ze maye gurbinsa for now Yakub should take over kafin mu sake zama muga abinda ya dace da ayi ina ganin mun gama abinda ya taramu you can all dismiss" Alhajin ya fada ba tareda ya kalleshi ba. Alhaji Zakariyya ya hadiye yawun takaici ta wani bangare kuma yaji dadin cewar YAKUB BECHI ne zeyi taking over dukda sunso ace anyi confirming nasa ne take as the newa AG amma hakan ma nasarace sunyi nasu Hajiya zata qarasa aikin a gida. Shiya fara miqewa ya kalli Aminu dake harhada takaddun gabansa cikin izgili yace
"Dama anyi gadon farar qafa dole a tsammaci abinda yafi wannan, Allah dai ya sauwaqa ya kuma tsayar iya kanku kar a bata mana sauran iri da halin bera" yana gama fadar hakan ya juya ya fice daga gurin dukkan su kuma sunji abinda ya fada, Da daddaya suka ringa ficewa daga conference room din ya rage Alhaji Audu, Alhaji Abdullahi wanda yake heading bangaren Siminti kuma dane a gurin Alhajin Audun ma'ana dan Yayansa ne da suka hada uba se Mustapha Manzo, shugaban Legal department na rukunin kamfanunuwan Bechi. Alhaji Abdullahi ya kalli Alhaji Audu dayayi shiru da alama yayi nisa a tunani, cikin ladabin da yake masa tun usulan yace
"Gaskiya Baba a iya fahimtata da kuma binciken da nayi bana zargin cewar Aminu yana da saka hannu a cikin batan kudaden nan"
"Nima dai abinda zan fada kenan, nayi amfani da duk wasu measures da muke using gurin gano me laifi banga wasu alamu na rashin gaskiya a tattare dashi ba. Amma abinda yake bani mamaki shine tabbas kudi sun bata amma babu wata alama da za'a iya tracing a ga inda kudin suka tafi tunda ba transfer akayi ba and we don't deal with huge cash here ballantana ace cash aka debe su. Ni dai what I'm thinking is that kudin nan dama babu su, lissafin bogi aka bashi kawai kuma ina ganin matsalar badaga ko ina aka samota ba se daga Oil Sector. Tunda Naziru ya fara heading gurin nan ake samun runton lissafi Mr Obasaki yana yawan kawo mun qorafin idanna sanar maka Alhaji baka daukan wani mataki na sosai and i don't know your reasons for that. Ire iren wadannan abubuwan ya saka mutane da yawa basa mixing Family with business saboda abinda bare zeyi maka ka dauki mataki idan Jininka ne dole ka daga amsa qafa, amma maganar gaskiya idan ana so a ga daidai se an gyara saboda kowa yasan can ne bangaren dayafi kowanne kawo profit idan aka cigaba da irin wannan tafiyar ina tsoron kar wata rana a wayi gari babu uwar kudi ma balle riba" Mustapha Manzo ya fada, yanda yake maganar duk wanda ya saurareshi dakyau ze fahimci jirwaye yakeyiwa Alhajin me kamar wanka. Kai tsaye baya so ya dora alhakin batan kudin akan Naziru tunda bashi da hujja amma yana so Alhajin ya bincika da kansa ya tabbatar.
Alhaji dake sauraronsu a zahiri yana gyada kai amma a badini kanzil bazece yaji daga abinda suke ta babatu akai ba maganar farar qafa da Zakariyya yayi ce take masa yawo a zuciya wasu shudaddun Al'amura da suka faru a baya suka shiga dawo masa kamar auransa da Mahaifiyar Aminun, abubuwan da suka gidana a tsakani har zuwa rabuwarsu.
"Wallahi Allah shine shaidata bani da masaniya akan yanda akayi kudin nan suka bata. Kowa a nan ya gani ga lissafi nan na duk abinda ya shigo kuma ya fita saga duka companies dinmu tun farkon shekara zuwa yanzu. Idan har duka lissafin da accountants dinmu suka kawo daidai ne tayaya za'ayi ace yanzu an sake lissafi an rasa wasu kudade? Nidai ban ci ba sedai a sake lissafi tun daga qasa ta yuwu a nan aka samu kuskuren lissafi" AMINU BECHI ya fada cikin tsananin tashin hankali. Sati biyu kenan da al'amura suka rikice a BECHI GROUP OF COMPANY lokacin lissafin shekara yayi bayan daya gama hada komai a matsayinsa na AG lissafi yasha banban da abinda aka bashi a rubuce da kuma tsurar kudi da suke a qasa inda aka samu rarar naira na gugan naira har Miliyan dubu biyu da dari biyar (2.5Billion) wadda bayan bashi damar yayi bincike da MD da kuma Chairman sukayi yauce ranar da aka taru duk wani daya isa a company domin jin ta yanda akayi aka haihu a ragaya.
Alhaji ZAKARIYYAH BECHI dake ta jujjuyawa a kujerarsa yana wani miskilin murmushi da babu wanda ya tantance kona menene ya kalle shi yace
"To Aminu kaida kanka kace dukka lissafin da aka gabatar maka daidai suke kuma baka karba ka saka hannu har seka bincika komai ka tabbatar da haka yake. Sannan a iya saninmu ku biyu kuke da access da central account dinmu dakai da Chairman duk wani wanda ze shigar ko fitar da kudi bayan ku biyun seya samu approval a gurinku to tayaya kake zaton zamu yarda idan kudi ya bata kuma kace mana bakada masaniya akai kenan Chairman ne da kanshi ya kwashi kudaden ko kuma me kake nufi?"
Aminu ya kalli Chairman din da tun zamansu bece komai ba ya tallabe haba da hannaye biyu yana bin duk wani da yayi magana a cikin su da kallo, Dattijo ne da a qalla zeyi shekaru 70 zuwa sama, dukda a zaune yake amma kana kallonsa zaka san Zabgegen mutum ne Jindadin rayuwa yasa har yanzun yake da sauran kwarinsa. Aminu ya hadiye yawu muqut saboda yanayin fuskar Chairman daya gani, bashi da yawan fara'a daman amma kuma yanayinsa na yau ya banbanta da kullum kana gani kasan zuciyarsa a kusa take koda yake ai dole, batun kudi akeyi fa, kudin daya qare rayuwarsa yana nemansu ya tara ace lokaci daya wasu su ringayi masa zari daidai dole hankalinsa ya tashi.
Seda ya daidaita nutsuwarsa kafin ya kalli MD dake jiran jin ta bakinsa yace
"Nidai na gama magana, ban ci kudin nan ba ban kuma san wanda ya dauke su ba. Amma dai kamar yanda nace kowanne gida (sector) su sake turo mana da lissafinsu na shekara a qaramun lokaci zan sake bin komai daki daki zan zauna da duka Bank Managers dinmu in Allah ya yarda za'a gano duk ma inda kudin suka shiga" ya qarasa muryarsa na rawa kuma cike da roqo da yaqinin Alhajin ya yarda dashi ya bashi wannan damar. Idan ya rasa besab ina ze dosa ba, abu biyu ne dole daya ya faru, dukda kasancewar Dan Chairman na cikinsa a sabgar Company basa kawo wannan relation din, ya sani kodai yayi Aman kudaden nan tas Miliyan dubu biyu da dari biyar wanda ko an siyar dashi da matarsa da yayansa da abinda ya mallaka baza'a hada wannan kudi ba abu na biyu kuma in wancan be samu ba yasan garqameshi za'a yi a prison still kuma A siyar da duk abinda ya mallaka Company ya rage Asara maganar aikin sa daman tun ranar da kudin sukayi batan dabo ya rubuta resignation letter ya ajiye dan ko be bari ba korar sa za'ayi.
"Maganar wani lokaci ko a sake bincike duk bata taso ba dan a tsayin faruwar abun zuwa yanzu da da wani abu da zakiyi tuni kayishi, just admit it Aminu kai kaci kudaden nan ka dawo dasu baki alaikum base magana tayi tsayi ba" NAZIRU BECHI ya fada yana wani zazzare masa ido
"Nima dai abinda na gani kenan, idan kuma yayi taurin kai Maigirma Chairman ina ganin a barshi da Legal department suyi aikinsu nasan su zasu sna ta yanda zasu tirsasashi yayi aman kudin ko kuma su miqashi inda ya dace" Alhaji Zakariyya ya qarasa miyar gishiri, cikin Aminu ya kada, ya ringa raba ido tsakanin Alhaji BABANGIDA BECHI da kuma YAKUBU BECHI da yake matsayin mataimakinsa AAG wanda tun fara taqaddamar kamar ma baya gurin wayarsa yake dannawa kunnensa saqale da Bluetooth tabbacin ba jinsu yakeyi ba hakan yasa ya tsayar da idonsa kan Alhaji Babangida cike da roqon ya saka baki amma seyaga ya saukar da kansa qasa bece komai ba.
Dakin ya sake daukan shiru na wani lokaci kafin cikin murya me cike da Izza irin ta wanda suka ci suka tada kai Chairman, Alhaji AUDU BECHI ya fara magana yana cewa
"Duk naji bayanan ku kuma na duba takaddun da aka rigada aka gabatar mun tuntuni. Account general, ina so daga yanzu zuwa qarfe biyu ka gabatar da takaddar barin aikinka da kanka saboda idan muka koreka zamu bata maka career be zama lallai ka sake samun aiki a wani gurin ba, kudi kuma duk wanda ya dauka yaje dan kansa" yana gama fadar haka ya tsuke bakinsa yana kallonsu daidai.
Aminu ya sauke ajiyar zuciya me nauyi tamkar wanda ya hadiyi kunama, jiki da bakinsa suna rawa ya zame daga kan kujerarsa ya durqushe yana cewa
"Nagode Alhaji, Allah ya qara girma nagode nagode".
Naziru da Zakariyya wanda farkon maganar Alhaji yayi musu dadi, sun dana kuma ta kama suka kalli juna tareda yin signa akan idon Alhaji Babangida dake lura da duk wani motsinsu ya girgiza kai kawai. Bazeyi kaffara ba idan ya rantse cewar shirinsu ne saboda sun nuna baqin ciki qarara da kujerar ta Aminu amma baze saka baki a cikin maganar na domin rayuwar gidansu rayuwa ce irin ta kowa tasa ta fishsheshi shida Yan dakinsu. Tunda Aminu ya samu wannan matsayi qarara mutane da yawa a gidan suka nuna qyashi da hassada bayan rasuwar Mr Adekunle Balogun wanda shine AG na BECHI GROUP din tun kafuwarsa Alhajin bisa shawarar Legal Department da sukaga cancantar Aminun aka dorashi, shekaru biyu kenan tun kuma hawansa abubuwan da ba'a saba dasu ba suke faruwa amma wannan al'amari shine mafi girma wanda baze yuwu a dauke kai ba.
Cikin zafin ran dake nuna hassada qarara Alhaji Zakariyya yace
"Ranka ya dade (haka suke kiransa muddin sabgar data shafi aiki ce) naji kace yayi resigning kawai banji maganar dawo da kudi ba ko wani hukunci da za'a dauka akansa?"
"Da alama kunnenka ya soma samun matsala ko? To ka tambayi na kusa da kai su maimaita maka abinda nace, maganar wanda ze maye gurbinsa for now Yakub should take over kafin mu sake zama muga abinda ya dace da ayi ina ganin mun gama abinda ya taramu you can all dismiss" Alhajin ya fada ba tareda ya kalleshi ba. Alhaji Zakariyya ya hadiye yawun takaici ta wani bangare kuma yaji dadin cewar YAKUB BECHI ne zeyi taking over dukda sunso ace anyi confirming nasa ne take as the newa AG amma hakan ma nasarace sunyi nasu Hajiya zata qarasa aikin a gida. Shiya fara miqewa ya kalli Aminu dake harhada takaddun gabansa cikin izgili yace
"Dama anyi gadon farar qafa dole a tsammaci abinda yafi wannan, Allah dai ya sauwaqa ya kuma tsayar iya kanku kar a bata mana sauran iri da halin bera" yana gama fadar hakan ya juya ya fice daga gurin dukkan su kuma sunji abinda ya fada, Da daddaya suka ringa ficewa daga conference room din ya rage Alhaji Audu, Alhaji Abdullahi wanda yake heading bangaren Siminti kuma dane a gurin Alhajin Audun ma'ana dan Yayansa ne da suka hada uba se Mustapha Manzo, shugaban Legal department na rukunin kamfanunuwan Bechi. Alhaji Abdullahi ya kalli Alhaji Audu dayayi shiru da alama yayi nisa a tunani, cikin ladabin da yake masa tun usulan yace
"Gaskiya Baba a iya fahimtata da kuma binciken da nayi bana zargin cewar Aminu yana da saka hannu a cikin batan kudaden nan"
"Nima dai abinda zan fada kenan, nayi amfani da duk wasu measures da muke using gurin gano me laifi banga wasu alamu na rashin gaskiya a tattare dashi ba. Amma abinda yake bani mamaki shine tabbas kudi sun bata amma babu wata alama da za'a iya tracing a ga inda kudin suka tafi tunda ba transfer akayi ba and we don't deal with huge cash here ballantana ace cash aka debe su. Ni dai what I'm thinking is that kudin nan dama babu su, lissafin bogi aka bashi kawai kuma ina ganin matsalar badaga ko ina aka samota ba se daga Oil Sector. Tunda Naziru ya fara heading gurin nan ake samun runton lissafi Mr Obasaki yana yawan kawo mun qorafin idanna sanar maka Alhaji baka daukan wani mataki na sosai and i don't know your reasons for that. Ire iren wadannan abubuwan ya saka mutane da yawa basa mixing Family with business saboda abinda bare zeyi maka ka dauki mataki idan Jininka ne dole ka daga amsa qafa, amma maganar gaskiya idan ana so a ga daidai se an gyara saboda kowa yasan can ne bangaren dayafi kowanne kawo profit idan aka cigaba da irin wannan tafiyar ina tsoron kar wata rana a wayi gari babu uwar kudi ma balle riba" Mustapha Manzo ya fada, yanda yake maganar duk wanda ya saurareshi dakyau ze fahimci jirwaye yakeyiwa Alhajin me kamar wanka. Kai tsaye baya so ya dora alhakin batan kudin akan Naziru tunda bashi da hujja amma yana so Alhajin ya bincika da kansa ya tabbatar.
Alhaji dake sauraronsu a zahiri yana gyada kai amma a badini kanzil bazece yaji daga abinda suke ta babatu akai ba maganar farar qafa da Zakariyya yayi ce take masa yawo a zuciya wasu shudaddun Al'amura da suka faru a baya suka shiga dawo masa kamar auransa da Mahaifiyar Aminun, abubuwan da suka gidana a tsakani har zuwa rabuwarsu.