← Book details Furucina Ne Part 2 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 100

Sashe 7

Furucina Ne Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Miƙewa yayi Abdulmajid ya kalleshi yace
"to yanzu sai ina ?
"Alƙali zanje zamfara Alhaji Yahaya yasan Hajiya Hauwa ba son kishiya take ba ya tashi ya ɗankara mata yanzu gashi matsalolin suna ta kunnowa ga business yasha gaban sa".
Mommy tace"a a fa my heart ba a yanke hukunci da bangare daya sai an hadu dukkan su ai nima ta gaya min yanzu haka ya sauke igiyar aurensa biyu a kanta saura ɗaya ai ko me ta masa bai kamata ya furta saki ba"
Ya ce "ai shine zanje nayiwa tufkar hanci yanzu haka tana Abuja nace ta biyo jirgi yanzu mu hadu a family house nasu."
Ummu da Hajja atare suka ce "Allah ya tsare."

Mommy ɗan sunkuyawa tayi dai-dai kunne sa yanda ba wanda zaiji tace
" Halimatus Sadiya tana adawo lafiya".
ta ƙarashe maganan tana nuna cikin ta da ido
shima cikin basarwa ya
shafa cikinta yayi ƙasa da murya yace"har kinsa mata Halima kenan ni kuma dana fison asa Hajja a farko amma Halima ma yayi. Yawwa wai ina my Son fushi dai yake ko".?
Murmushi tayi tace"kasan sa da zuciya kuma baka yi lalashi ba".
Tayi magana tana bin bayan sa dan yayi gaba suna fitowa suka hango mutane gidan a compound din Hajja da alaman Abu suka rako dan shima zaiyi tafiya seminar zuwa Egypt kowa yana masa fatan a sauka lafiya
hannu ya bawa Abba sukayi musabaha, Abu yace "sai nan da wata biyu kenan ko, Bro?"
Murmushi Abba yayi yace " a a kai kam zamu hadu a Englan ai ba dan issue ɗin gidan Yahaya ba da tare zamu wuce yanzu kaga Hajja tana ta faɗan na jima banje dardum ba shine na shirya tafiyan a mota zan shiga dardum nayi ziyara
sai na wuce zamfaran insha Allah zuwa Wednesday ina England".
Abu yace "kasan yanda hanyar zamfaran nan take kake cewa zaka tafi a mota"?
Murmushi yayi yace "ba komai bro in ma yan kidnapping ka ke tsoron mota ta bayajin bullet
in kuma accident ne mota na bazai fadi ba koya faɗi akwai matakan kariya wanda ko ƙwarzani ba zai yi ba".
shiru Abdulraham yayi duk da yasan akwai kuskure a *FURUCIN* Ɗan uwan nasa amma yamasa fatan alkairi da cewa
"to Ɗan uwa saduwar alkairi sai mun hadu acan din dan ina ga seminar ɗin zai ɗaukemu kusan few weeks sai kuma idan mungama ina da hutu na 2weeks zamu kasance tare."
Abba yayi murmushi shikuma har zai shiga mota da gudu Nasir ya rungumoshi ta baya yana cewa"Abu na zamuyi missing naka."
Juyowa Abu yayi yace "haka ne my Son amma me kuke son na kawo muku Nasir yace "computer". Abu yajuya yana kallon Agrif da Kamal
yace kuma kun yarda computer kuke so ko?"
ya ƙare maganan yana kallon Kamal da Agrif da Aiban".
Suka ce yes! Abu
''Ok"
Yace yana shafa kan Abbaty da yake hannu ummu yace kai fa cikin gwarancin sa yafadi wani maganan da duk basu gane me yake cewa ba ɗan shikara 3 amma yayi nauyin baki ba agane maganan sa driver sa yabuɗe masa front seat yashiga suma bodyguard dinsa suka shiga yaja drive.
Motan Abu suna fita Nasir ya juya da niyar komawa duk da yasan Abba ma tafiyar zayyi amma yak'i ya tsaya yaga tafiyar sa
Mommy tace "son baka san Abban ku ma tafiyar zaiyi ba"?.
Ko juyowa baiyi ba yashige part ɗin Hajja
Abba har an mude masa kofa zai shiga yajuyo yana kallon hanyar part ɗin Hajja ɗin ji yayi bazai iya tafiya ba sai yanemi sulhu da ɗan nasa yace "sorry ina zuwa".
dariya Hajja tayi tace"ka ce baka ji, wa ya gaya maka karo da nasara akwai riba? ai Nasara goshin girji ne me wuyar karo".
bai juyo ba yana cigaba da tafiya yace"ai Hajja ku kuke ɗaure masa yake abinda yaga dama".
yana shiga yasamu Nasir akan two seat ya daura ɗaya kan ɗaya yasa Laminu mai aiki yana tsiyaya masa ruwa a cup
ya nuna kamar ma bai ga Abban ba Abba ya zauna a gefin sa ya numfasa yace "kana jina NASURUDDEEN?
Turo baki yayi baiyi magana ba Abba yace "me yasa kake haka ne laifi fa kamin amatsayina na mahaifinka na tambayeka me ya haɗa ku da ɗan uwan ka? kamin shiru dan Aiban ƙanin ka ya faɗamin shi ne ka tura masa tea ajiki da yana da zafi da ka konashi. shi ya sana dake ka kai fa yaro ne har yanzu shekarun ka 7 kawai a duniya Nasuru amma ba wanda ya isa dakai meyasa kake haka bana son wannan halin naka kana da zuciya,Saurin fusata,iko,isa gadara ka daina, da Agrif ne yakeyi ko Kamal baza a sama sa ido kamar kai ba. Kai a ido kake duk abinda kayi za ace dan kana ɗanane duk da nasan baka kai matakin da za ace hakan ba amma in ka tashi da wannan ɗabi'ar za ace hakan wataran".
Nasir yace". To Abba me yasa idan Agrif ne ko Kamal baza aga laifin sun ba".?
dafa kafaɗan sa yayi yace"duk da ƙwaƙwalwar ka tayi wa amsa ta nauyi amma
zan baka ya zama dole kasani Nasir kai kana idon mutane ba daya kake da yan uwan ka ba duk abin da kayi za ace dan kana ɗana ne kana taƙama da arziƙi na ne, shi yasa nake son ka gujewa laifi komai ƙanƙantar sa kazama mai biyya ga iyayenka Abdulmajid, Abdulraham da mommy ka sannan inaso kayiwa Mamar ka Halima addu'a kullum idan kayi sallah har nima."
Mommy da ta jima a wajen tayi gyaran murya tace haba Abba wadan nan kalaman sunyi wa son nauyi".
Abba ya furzar da iska yace "ni ma nasan sunyi masa nauyi ban san mesaya nake wasu abubuwan ba Dr dan Allah kamar yanda Halima ta bar miki amana nima na bar miki amanar Nasir da abinda ke cikin ki.....
Nasir ne ya katse shi dacewa "Abba wacece Halima"? Abba da mommy da sauri suka kalli juna tana masa alaman kaga irinta ko kallon agogon hannusa yayi ya miƙe tsaye tare da rike hannu Nasir cikin sanyin murya yace"fatima kawo hannu ki miƙo masa tayi ya haɗa da hannun Nasir yace a karo na biyu amana dan Allah ki bashi duk wata kariya a rayuwa bawai ina gaya miki maganan nan bane da wata manufa ko dan ki tada hankalin ki ina fada ne saboda niba mazauni bane shine dalilin da yasa Halima tace ke tabawa Nasir yarda ce tasa na barmiki amana. Nasir nima
kuma ni nasan yan uwa na basu da matsala ba zasu tada muku hankali akan abinda yazama rabon kuba amma ki musu adalci yanda ya kamata.........
Mommy
cikin ɓacin rai tace "please ya isa".
murmushi yayi yafara tafiya hannusa na saƙale da nasu har inda ake jiran su parking sp ɗin
har an ɗude mota yashiga yafito yana kallon Hajja da daddy yace " Hajja Alƙali a yita haƙuri da halin Nasir insha Allah zai dena Dan Allah ka bashi tarbiyya bisa amana kamar yanda zaka bawa Kamal.....
Hajja tace "kai Abdulsamad nidai zan koma ciki Allah ya tsare ka gaida mutanen daldum sosai. Allah yamaka albarka" tayi ciki
shi ma ya shige mota yana ɗaga musu hannu amma kafin direba ya rufe Nasir yayi wuf yafada jikin sa haka kawai ya saki kuka yana cewa
"Abba kar ka tafi".
murmushi Abba yayi yace" my Son ba dan school ba tare zamu yi tafiyar gobe nefa zan zo jirgin asuba zanbi gobe iyanzu ma muna tare ɗan al'barka".
Ya juya ya kalli Kamal da Agrif da Aiban da Abbaty ya sake fitowa duk sai da ya rungume su shida ba bawa ni damuwa yayi da safgan yaran ba amma yau jiyayi kamar kar ya tafi gani yake idan ya tafi wani abun zai iya samun iyalin nasa musamman da Nasir yace ABBA KAR KA TAFI ɗaya bayan ɗaya yajuya yana kallon su duk sai yaga jikin su yayi sanyi a hankali yashiga motar direba yaja suka fice a harabar gidan idon sa yana kan Fanna da Nasir
duk a sanyaye suka koma gida
Abba har sun kusa fita daga Kano sarkin kasuwa ya kirashi.
ɗaukan wayar yayi yana cewa "Allah yaja zamanin shugaban yan kasuwar duniya".
daga can ban garen Alhaji Nuhu yace "au ranka shi ɗade kama bani na duniyar baki ɗaya kenan".
dariya Abba yayi yace '"eh! mana kano ai duniyace yanzu haka gashi munfi awa mun kasa fita a garin ashe haka fita amota yake da wahala acikin Kano ".
Alh Nuhu yayi saurin cewa
" Sir fita kuma duk fa anshirya kai akejira".
Abba
yace "kai Alhaji Nuhu na wakilta Adamu zai halarci meeting ɗin nan ni bazan samu dama ba".
cikin damuwa Nuhu yace "Adamun yazo amma yallabai dole sunce sai dakai duk akan rage farashin kayan da kayi ne sauran kamfunnnan sunce basu yarda ba kuma suna da gaskiya ragin yayi yawa kaga harda president har ya ƙaraso kai kawai ake jira".
Chapter 7 · 0% Book details