Sashe 6
Furucina Ne Part 2 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"A a my hubby daina cewa haka yanzu haka ina ɗauke da jinin ka na watanni 2 da sati biyu naso nayi surprise dinka ne." Dr
Are you sure?"
"Very sure my heart".
"Dr Dan Allah ki cire maganan wasa"
Murmushi tayi tace shekara bakwai ka taɓa jin irin wannan wasan a baki na duk yanda kake nuna son kaga mun samu ka manta nakai maka ziyara a China, wata biyu kawuce paris ni nazo gida idan kayi lisafi dai_dai da lokacin cikin zai nuna maka wllh tun a chana na gane amma nayi shiru dan nayi surprise ɗin ku gabaɗaya".
A hankali ya sunkuyo ya manne ta a jikin sa yace" fatima batul kin bani farin ciki tabbas ke ɗin haske ce a rayuwata dole nayiwa Allah godiya. a gobe dayawan ma buƙatan da suke cikin garin kano zasu kwana da farin cikin Alhamdulillah! Allah yamin komai Allah yabani matar da nafi so a rayuwata wanda tun ina yaro nake kwatanta irinta a Raina, yabani dukiyar da ban san iyakar taba yanzu kuma yara Alhamdulillah! ni kam ba dan kar nayi sabo ba da sai nace ina ma ba a wajif ta mutuwa ba dan nikam Allah ya shimfidamin rayuwa a duniya kamar bazan mutu ba amma nasan hakan saɓo ne yarabbi ka Gina min lakhirata fiye da duniya ta. Ya rabbi ka dora ni kan hanya madai daiciya, dukiyar da na tara kasa yazama silar ciyo na zuwa aljana ba ya kai ni ga wuta ba. Allah yasa yara na da zan bari su tafiyar dashi ta hanya madaidaiciya."
"Ameen tace tare da ɗaura hannuta kan nasa da yake yawo a cikin ta
ta ce "my Son yana wajen Hajja nasan kuma bazai yarda ya kwana a can ba duk hankali na yana can".
Murmushi yayi yana shafa cikinta
yace"niko hankalina yana nan."
da sauri ta ɗago kai tana kallon sa da alaman ɓaccin rai, harshin sa ya kai kunneta yana lasa yace "kina yaudaran kanki fuskan ki fa baya nuna ɓacin rai ko damuwa a kullum cikin annurin take".
In dai zaka taɓa my Son to sai na fasa kawo maka ɗan adawar namu".
dariya yayi ya ce" faɗan Allah ne ai ba ikon ku bane ai kwara a kawo masa ɗan a dawar ko ya daina taɓara. Wllh taɓaran Nasir dan ganin shi ɗaya ne yanzu Agrif dayake da ƙannai Aiban da Abbaty ai bayayi ga Aisha ma data ɗauko ƴar riko Zahra ai Kamal bayayi, shi ko kullum abin jarirai yakeyi har shekara bakwai sai dai kimasa wanka da kanki kuma baya yarda yan aiki su masa ko wando bai iya sawa ba nasan idan ya samu ƙane zai san ya girma".
A ɓangare hajja kuwa daƙyar ta lallaɓa mutumin ya yarda yayi bacci. Bacci yayi rigimar a kaishi wajen Mommyn sa.
Da safe duk an haɗu a dining za ayi breakfast, su Mommy da Abba sun makara har anfara ci suka karaso cikin raha. Abdulmajid yace" kai Abba amma ko dai jiyan nan....
sai kuma yayi shiru yana dariya.
Abba ma darinyan yayi yana gyarawa mommy kujeran ta yace ƙarasa mana karamin marar kunya."
Duk akayi dariya, mommy ko idonta akan kowa ganin bata ga ɗan taba har tabuɗe baki zatayi magana taji Agrif yace" mommy Abba Ina kwana Ina my bro?".
Mommy amsa gaisuwan tayi tare da kallon Hajja da alaman tambaya kafin Hajja tayi magana sukaji Nasir yana cewa "to ni ina ruwana da kai naga Mama ce tace kar musake shigowa arabe shine dan na tsaya na gaida baba Yakubu yayi gaba, dan zan maga magan kawai ka saki fitsari shi ne Aiban yacewa Abba wai nayi faɗa dakai ya min duka".
Agrif yace " to bakai kayimin tsawa ba fisarin yafito ban sani."
dariya duk sukayi ban da Nasir da yaci kunu Ummu tace "Allah sarki NASARA ai dama nasan ba laifinka bane shima Abba dan ba ma zauni bane baisan halinka ba baka fadan rashin gaskiya haka ne kam kamar yanda Mama tace kudun ga shigowa tare ku haɗa kan ku kar a ganku a rarrabe mugayen mutane zasu iya samun nasara akan ku kuji ƴan albarka".
Yes! suka ce
Shi kuma Nasir durƙusawa yayi har ƙasa kamar yanda suka saba yace "Daddy Abu Ina kwanan ku".?
Lafiya suka amsa suna tambayar ya jikinsa bayyi magana ba yaci kunu
yana cewa "Mama ummu ina kwana?
Mama tace "Nasara ko gani kafi mutum NASARA me wuyar ɓatanci ya jikin naka?"
ya sake yamusa fuska yayi bai yi magana ba,
Mommy ganin Nasir ko inda take bai kalla ba yasa cikin sanyi murya tace
"my Son".
ɗagowa yayi ya zuba mata dara-daran idon sa da suka gama cikowa da kwallah yayi
yana juya idon alaman yana son mai da kwallan, bai amsa ba har ya maida kansa ƙasa
ta sake cewa "my Son fushi kake damu".?
girgiza mata kai yayi
tace" to me yasa baka gaida mu ba nida Abba".
miƙewa yayi ya ƙarasa inda take yayi saurin faɗawa jikinta ya saki kukan da yake dannewa tun jiya ya ƙwace masa cikin kuka yace "mommy ba ke bace kika barni kika tafi na kasa bacci, baki min wanka ba, baki min addu'a ba, baki bani tea ba, banyi bacci ba, nayi ta mafarkin ki
Ga ciwon da Abba yajimin sai zafi yakemin kin gani".ya ƙarashe maganan yana ɗaga rigan uniform din sa abinka da farin fata duk birdi yayi jajir wani ma ya fashe".
Alhaji Abdulsamad da sauri ya ɗauke idon sa akan ɗan nasa wani irin tausayin ɗan nasa ne ya ziyarci zuciyar sa amma ya dake mai kawaici ne, sai kawai ya ɗauki pork yafara caccankan dankali.
Mommy itama idon tane ya cicciko tace "sorry my love. Soon zaka warke nima nayi missing naka banyi bacci ba zo kayi breakfast karku makara idan kazo zan shafa maka magani kaji".
Agrif yace" Abba ba muyi fada bafa kalli jikin bro". yayi maganan yana fito da ƙwallan da suka taru a idon sa yana shafa dantsen hannu Nasir cikin tausayi da ƙyar Nasir ya yarda ya dan sha tea Maimunatu me aiki ta haɗo musu wanda zasu tafi dashi suka fita
bayan fitan yaran Alhaji yayi gyaran murya yace " Hajja dama nayiwa Fatima wani kyauta ne nake son sheda muku ke da yan uwa na,
a daren jiya na mallakawa Dr Fanna *Three brothers Rice*
dan haka ina son kusa mata albarka.
Sai Ƴan uwa na kuma
Abdulraham da Abdulmajid na mallaka musu kamfanin *Ashana* ta tanan Kano dan zasu fi jin daɗin aiki dashi kuma naga akwai cigaba a harkan ashanan nan wllh zakuyi mamakin kuɗin da kamfanin ashana take fitar wa a kullum. Hajja sai ke me kike so?".
Numfasawa tayi tace umh! nikam ba abinda nake so illa Allah yahaɗamin kan ku sai de nake ga kamar yautar ƴan uwan ka baiyi yawan na matar ka ba tunda baza'a haɗa shinkafa da ashana ba".
yace "a a hajja shima ashanan ana samu dai-dai gwar gwado kuma ita Fatima bafa babban kamfanin nin rice na Lagos na bata ba, na nan Kano ne su kuma yan uwa na kome suke so acikin dukiyata zan mallaka musu ai kayana nasu ne bani da wanda yafisu. A nan Kano dai a yanzu ba companyn da yawuce na ashanan samu kuma na basu shine saboda su agida suke shi ɗin zaifi musu sauƙin aiki amma ni banƙi ace kowa cikin su ya zabi companyn da yake soba nasha gaya musu ga sunan sai suce ai da ya zauna a guna wai basu da ra'ayin business ne. Idan suna so duk wanda suke so ikon sune ko wani zasu iya bawa kayana ".
Abdulraham yace "hakane Hajja ba abinda Abdulsamad yaragemu dashi kowane mataki muka taka silar sace"
shima Abdulmajid haka yace sukayi godiya itako mommy wani banbarakwai taji kyautar duk da tun a ɗaki yasanar mata tukuicin surprise ɗin da ta masa sai a gaban hajja amma batayi zaton har tukuicin yakai haka ba.
Tana cikin wannan tunanin taji Abdulmajid yace "Dr congratulations!"
Itama cikin maida masa martanin murmushin sa tace "thanks my love!" Abdulraham ma yace "Dr Allah yasa albarka a ciki, Mama da ummu ma suka mata murmushi tayi cikin jin nauyin ita dai bata so Abdulsamad yayi mata haka ba.
Abdulsamad ya kalli Mama da Ummu yace" Aisha ke kuma daga yau gidan Mai na hanyan kondila naki ne ke ma Amina na yan awaki nakine.
Sannan duk a tara min ma'aikatan gidan nan duk mai buƙata in dai na kuɗine to a masa zan sa MD HOD Accountant su fito da kuɗin da za'a bawa mabuƙata mutum dubu goma a kano da kuma dubu goma a duk jahohin arewa sannan a bawa kwamitin marayu na kowacce jaha kuɗin adadin yanda aka saba badawa a zakka amma ba zakka bane kyauta ce. Dan nuna godiya ta da kyutar da Allah yabani".
Hajja tace"Abdul abin bai yi yawa ba wannan ai sai kasa dukiyar ka ya girgiza".
murmushi yayi yana matsowa kusa da ita ya juyo mata da agogon hannun sa yana nuna mata yace "Hajja kin gani a yanzu da muke maganan nan kuɗin da suka shigo min ya kusa rabin kyautar da nayi kuma gobe ma haka. Kyauta ko sadaka Hajja bazai girgiza dukiyar Three brothers ba sai dai ma yaƙara masa ambaliya".
murmushi tayi tana kallon agogon nasa tace "ina zan gane wannan lissafin Allah yasa albarka cikin dukiyar ka su kuma wanɗan da ka bawa Allah yasa silar arzikin su kenan ".
Amin! suka ce dukkan su Mama da Ummu har ƙasa suka durƙusa suna masa godiya a ranan dai kowa yaga 3brothers yasan yana cikin farin ciki duk wanda Allah yatsaga da rabonsa dai yayi arziƙi duk da bai fito ya faɗa ba yan uwa sa da Hajja sun san yana cikin gagarumin farin ciki.
Are you sure?"
"Very sure my heart".
"Dr Dan Allah ki cire maganan wasa"
Murmushi tayi tace shekara bakwai ka taɓa jin irin wannan wasan a baki na duk yanda kake nuna son kaga mun samu ka manta nakai maka ziyara a China, wata biyu kawuce paris ni nazo gida idan kayi lisafi dai_dai da lokacin cikin zai nuna maka wllh tun a chana na gane amma nayi shiru dan nayi surprise ɗin ku gabaɗaya".
A hankali ya sunkuyo ya manne ta a jikin sa yace" fatima batul kin bani farin ciki tabbas ke ɗin haske ce a rayuwata dole nayiwa Allah godiya. a gobe dayawan ma buƙatan da suke cikin garin kano zasu kwana da farin cikin Alhamdulillah! Allah yamin komai Allah yabani matar da nafi so a rayuwata wanda tun ina yaro nake kwatanta irinta a Raina, yabani dukiyar da ban san iyakar taba yanzu kuma yara Alhamdulillah! ni kam ba dan kar nayi sabo ba da sai nace ina ma ba a wajif ta mutuwa ba dan nikam Allah ya shimfidamin rayuwa a duniya kamar bazan mutu ba amma nasan hakan saɓo ne yarabbi ka Gina min lakhirata fiye da duniya ta. Ya rabbi ka dora ni kan hanya madai daiciya, dukiyar da na tara kasa yazama silar ciyo na zuwa aljana ba ya kai ni ga wuta ba. Allah yasa yara na da zan bari su tafiyar dashi ta hanya madaidaiciya."
"Ameen tace tare da ɗaura hannuta kan nasa da yake yawo a cikin ta
ta ce "my Son yana wajen Hajja nasan kuma bazai yarda ya kwana a can ba duk hankali na yana can".
Murmushi yayi yana shafa cikinta
yace"niko hankalina yana nan."
da sauri ta ɗago kai tana kallon sa da alaman ɓaccin rai, harshin sa ya kai kunneta yana lasa yace "kina yaudaran kanki fuskan ki fa baya nuna ɓacin rai ko damuwa a kullum cikin annurin take".
In dai zaka taɓa my Son to sai na fasa kawo maka ɗan adawar namu".
dariya yayi ya ce" faɗan Allah ne ai ba ikon ku bane ai kwara a kawo masa ɗan a dawar ko ya daina taɓara. Wllh taɓaran Nasir dan ganin shi ɗaya ne yanzu Agrif dayake da ƙannai Aiban da Abbaty ai bayayi ga Aisha ma data ɗauko ƴar riko Zahra ai Kamal bayayi, shi ko kullum abin jarirai yakeyi har shekara bakwai sai dai kimasa wanka da kanki kuma baya yarda yan aiki su masa ko wando bai iya sawa ba nasan idan ya samu ƙane zai san ya girma".
A ɓangare hajja kuwa daƙyar ta lallaɓa mutumin ya yarda yayi bacci. Bacci yayi rigimar a kaishi wajen Mommyn sa.
Da safe duk an haɗu a dining za ayi breakfast, su Mommy da Abba sun makara har anfara ci suka karaso cikin raha. Abdulmajid yace" kai Abba amma ko dai jiyan nan....
sai kuma yayi shiru yana dariya.
Abba ma darinyan yayi yana gyarawa mommy kujeran ta yace ƙarasa mana karamin marar kunya."
Duk akayi dariya, mommy ko idonta akan kowa ganin bata ga ɗan taba har tabuɗe baki zatayi magana taji Agrif yace" mommy Abba Ina kwana Ina my bro?".
Mommy amsa gaisuwan tayi tare da kallon Hajja da alaman tambaya kafin Hajja tayi magana sukaji Nasir yana cewa "to ni ina ruwana da kai naga Mama ce tace kar musake shigowa arabe shine dan na tsaya na gaida baba Yakubu yayi gaba, dan zan maga magan kawai ka saki fitsari shi ne Aiban yacewa Abba wai nayi faɗa dakai ya min duka".
Agrif yace " to bakai kayimin tsawa ba fisarin yafito ban sani."
dariya duk sukayi ban da Nasir da yaci kunu Ummu tace "Allah sarki NASARA ai dama nasan ba laifinka bane shima Abba dan ba ma zauni bane baisan halinka ba baka fadan rashin gaskiya haka ne kam kamar yanda Mama tace kudun ga shigowa tare ku haɗa kan ku kar a ganku a rarrabe mugayen mutane zasu iya samun nasara akan ku kuji ƴan albarka".
Yes! suka ce
Shi kuma Nasir durƙusawa yayi har ƙasa kamar yanda suka saba yace "Daddy Abu Ina kwanan ku".?
Lafiya suka amsa suna tambayar ya jikinsa bayyi magana ba yaci kunu
yana cewa "Mama ummu ina kwana?
Mama tace "Nasara ko gani kafi mutum NASARA me wuyar ɓatanci ya jikin naka?"
ya sake yamusa fuska yayi bai yi magana ba,
Mommy ganin Nasir ko inda take bai kalla ba yasa cikin sanyi murya tace
"my Son".
ɗagowa yayi ya zuba mata dara-daran idon sa da suka gama cikowa da kwallah yayi
yana juya idon alaman yana son mai da kwallan, bai amsa ba har ya maida kansa ƙasa
ta sake cewa "my Son fushi kake damu".?
girgiza mata kai yayi
tace" to me yasa baka gaida mu ba nida Abba".
miƙewa yayi ya ƙarasa inda take yayi saurin faɗawa jikinta ya saki kukan da yake dannewa tun jiya ya ƙwace masa cikin kuka yace "mommy ba ke bace kika barni kika tafi na kasa bacci, baki min wanka ba, baki min addu'a ba, baki bani tea ba, banyi bacci ba, nayi ta mafarkin ki
Ga ciwon da Abba yajimin sai zafi yakemin kin gani".ya ƙarashe maganan yana ɗaga rigan uniform din sa abinka da farin fata duk birdi yayi jajir wani ma ya fashe".
Alhaji Abdulsamad da sauri ya ɗauke idon sa akan ɗan nasa wani irin tausayin ɗan nasa ne ya ziyarci zuciyar sa amma ya dake mai kawaici ne, sai kawai ya ɗauki pork yafara caccankan dankali.
Mommy itama idon tane ya cicciko tace "sorry my love. Soon zaka warke nima nayi missing naka banyi bacci ba zo kayi breakfast karku makara idan kazo zan shafa maka magani kaji".
Agrif yace" Abba ba muyi fada bafa kalli jikin bro". yayi maganan yana fito da ƙwallan da suka taru a idon sa yana shafa dantsen hannu Nasir cikin tausayi da ƙyar Nasir ya yarda ya dan sha tea Maimunatu me aiki ta haɗo musu wanda zasu tafi dashi suka fita
bayan fitan yaran Alhaji yayi gyaran murya yace " Hajja dama nayiwa Fatima wani kyauta ne nake son sheda muku ke da yan uwa na,
a daren jiya na mallakawa Dr Fanna *Three brothers Rice*
dan haka ina son kusa mata albarka.
Sai Ƴan uwa na kuma
Abdulraham da Abdulmajid na mallaka musu kamfanin *Ashana* ta tanan Kano dan zasu fi jin daɗin aiki dashi kuma naga akwai cigaba a harkan ashanan nan wllh zakuyi mamakin kuɗin da kamfanin ashana take fitar wa a kullum. Hajja sai ke me kike so?".
Numfasawa tayi tace umh! nikam ba abinda nake so illa Allah yahaɗamin kan ku sai de nake ga kamar yautar ƴan uwan ka baiyi yawan na matar ka ba tunda baza'a haɗa shinkafa da ashana ba".
yace "a a hajja shima ashanan ana samu dai-dai gwar gwado kuma ita Fatima bafa babban kamfanin nin rice na Lagos na bata ba, na nan Kano ne su kuma yan uwa na kome suke so acikin dukiyata zan mallaka musu ai kayana nasu ne bani da wanda yafisu. A nan Kano dai a yanzu ba companyn da yawuce na ashanan samu kuma na basu shine saboda su agida suke shi ɗin zaifi musu sauƙin aiki amma ni banƙi ace kowa cikin su ya zabi companyn da yake soba nasha gaya musu ga sunan sai suce ai da ya zauna a guna wai basu da ra'ayin business ne. Idan suna so duk wanda suke so ikon sune ko wani zasu iya bawa kayana ".
Abdulraham yace "hakane Hajja ba abinda Abdulsamad yaragemu dashi kowane mataki muka taka silar sace"
shima Abdulmajid haka yace sukayi godiya itako mommy wani banbarakwai taji kyautar duk da tun a ɗaki yasanar mata tukuicin surprise ɗin da ta masa sai a gaban hajja amma batayi zaton har tukuicin yakai haka ba.
Tana cikin wannan tunanin taji Abdulmajid yace "Dr congratulations!"
Itama cikin maida masa martanin murmushin sa tace "thanks my love!" Abdulraham ma yace "Dr Allah yasa albarka a ciki, Mama da ummu ma suka mata murmushi tayi cikin jin nauyin ita dai bata so Abdulsamad yayi mata haka ba.
Abdulsamad ya kalli Mama da Ummu yace" Aisha ke kuma daga yau gidan Mai na hanyan kondila naki ne ke ma Amina na yan awaki nakine.
Sannan duk a tara min ma'aikatan gidan nan duk mai buƙata in dai na kuɗine to a masa zan sa MD HOD Accountant su fito da kuɗin da za'a bawa mabuƙata mutum dubu goma a kano da kuma dubu goma a duk jahohin arewa sannan a bawa kwamitin marayu na kowacce jaha kuɗin adadin yanda aka saba badawa a zakka amma ba zakka bane kyauta ce. Dan nuna godiya ta da kyutar da Allah yabani".
Hajja tace"Abdul abin bai yi yawa ba wannan ai sai kasa dukiyar ka ya girgiza".
murmushi yayi yana matsowa kusa da ita ya juyo mata da agogon hannun sa yana nuna mata yace "Hajja kin gani a yanzu da muke maganan nan kuɗin da suka shigo min ya kusa rabin kyautar da nayi kuma gobe ma haka. Kyauta ko sadaka Hajja bazai girgiza dukiyar Three brothers ba sai dai ma yaƙara masa ambaliya".
murmushi tayi tana kallon agogon nasa tace "ina zan gane wannan lissafin Allah yasa albarka cikin dukiyar ka su kuma wanɗan da ka bawa Allah yasa silar arzikin su kenan ".
Amin! suka ce dukkan su Mama da Ummu har ƙasa suka durƙusa suna masa godiya a ranan dai kowa yaga 3brothers yasan yana cikin farin ciki duk wanda Allah yatsaga da rabonsa dai yayi arziƙi duk da bai fito ya faɗa ba yan uwa sa da Hajja sun san yana cikin gagarumin farin ciki.