Sashe 13
Furucina Ne Part 2 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Cikin b'acin rai ya ce
"wane magana kika masa idan ke idonki ya rufe da son Nasir ni nawa a bude yake, ko baki fashimci akwai barazana a FURRUCINsa ba? Cewa fa ya yi duk sanda zai ganki kar ya ganki da ita kuma kar ya ganta a babban falo ko hanyar da zai wuce kar a bi da ita wai hakan ne k'adai zai sa ya kasa cutar da ita, ya kafa miki sharud'a kika amsa kin karba kin yi daidai kenan? ko wannan ba damuwa ba ce a gabana fa aka furta 'yar'uwar y'ata tana cikin wani hali Dr har ga Allah ina son NASURUDDEEN din amma FURRUCINSA ya yi ts'auri a kan Nasrim, ba zan iya kwatanta miki yanda nake jin NASRIM a zuciyata ba, ko Kamal shi ne babba ba na jin sa kamar ita ba zan iya jurewa ba idan wani abu ya same ta".
"To dan Allah alk'ali ka yi hakuri ai yaro ne zai dena".
Shiru ya yi yana sauk'e a jiyar zuciya yace" Allah Ya sa, Ya shirya shi. A dawo lafiya".
Cikin shagwaba ta ce
"Haba Abban Nasrim yau ba rakiya"?
Jinjina kai ya yi yana jan bargo yace I love you my wife sai kin dawo".
taku ta fara a hankali da niyar ta k'arasa inda yake ta yi masa kissing
Cikin wata irin murya ya ce "Allah kika kuskure kika k'araso nan bake ba tafiyar nan dan zan b'ata shiri".
Cak ta tsaya tana masa shagwaba
yinkurin tashi ya yi da gudu tayi hanyar fita si ya ce "Da ki tsaya mana ki ga illar tsokana". Sai da ta kai kofa ha hura masa kiss din a hannu ta yi saurin fita dan tasan in ya kamata bakyau.
********
Bayan kwana biyu haka mommy ta zaunar da Maimunatu da Harira tana ce da su
"kuna ji na ko? Nasir ba ya son ganin k'ananan yara jarirai dan haka nake son ku dinga boye Nasrim idan kun gan shi kar ku yarda ya ganta a tak'aice dai ni ma ba na son ku bari ya gan ta, sannan ina neman alfarmarku wannan ya zama sirri tsakanina da ku ka da ku bari wasu su gane ko da Hajja ce".
Maimunatu tace'' in sha Allah ba mai ji wannan maganar"
Ita ma Harira haka ta faɗa wa mommy.
Mommy ta ce
"Yawwa na gode da yanda kuke kiyaye dukkan dokokina ina jin dadin zama da ku sannan ke Maimunatu iyayen Garba sunje garin ku an gama komai sai saka ranan aure kuma na ji dadin yanda suka ce ba sai kin je ba sun bar komai a hannuna su za su zo nan ayi shiyasa na sa a muku gini a nan kusa da part dina ta baya in sha Allah kafin lokacin za a gama ginin".
Cikin kunya myaimunatu ta yi godiya
haka maaikatan nan sukaci gaba da ɓoye Nasrim duk ko yaran da aka samu akasi Agrif ya nace ya dauketa ya ganta to duka da minsini de sai ta sha su a wajen Nasir, Agrif ko ya ce bai yarda ba dan batuwa da Agrif a kanta dan shi duk abin da Nasir yake masa ba ya damunsa amma muddin ya taba masa Nasrim to za suyi fada a ranan ko abinci ba za su ci tare ba, zai ce yayi jagolgolo ta k'azamar yarinya sosai Agrif yake son Nasrim ita ma Nasrim tunda tayi wayo take son sa, amma ba ta son ko da ganin Nasir tana ganin sa za ta sa kuka kaman za ta shide yau ba Harira ta barta a main parlour ta tafi hado mata madaran ta, ta rarrafa ta fito compound shi kuma Nasir yana zaune ya juya bayansa da litafi a hannunsa dan karatu yake tuk'uru sun kusa zana jarabawan fita daga primary ya ji an rike masa k'afa yana juyowa yayi arba da ita bai gane taba dayake baya tsayawa ya kalli fuskanta sosai murmushi yasakar mata ita ko tana d'agawa ta kalleshi ai k'o ta fashe da wani irin kuka da sauri yasa hannu ya dauketa yana cewa am sorry beautiful baby girl". yana kallon ta yana shafa kwantaccen suman kanta yana murmushi ya sake cewa komai naki me kyau ne baby".
ita ko sai wani irin kuka take tana neman sauk'a ajikin sa,
Agrif da yake baya shima yana nasa karatun ya ji kukan Nasrim yayi yawa ya juya da niyar ya shiga parlour ya ganta a hannan wanda bai taba zato ba
Nasir yace ''Agrif kaga wata beautiful baby girls gashinta mai kyau komai nata me kyau dan Allah yar wacece mommy tayi bak'uwa ne"?
Wani irin dariya Agrif yasa yana tafa hannu ya ce "Ashe ka san mai kyau ce ashe za ka dauke ta, ba kai ka ce ko hanyar da ta bi ka gani ba zaka sake bi ba? Ashe duk k'arya ne''.
Ya k'arashe maganan yana cigaba da dariya, sai alokacin Nasir ya tuno da wacece a hankali ya sake ta ta yi kasa da sauri Agrif ya yi niyar ɗaukota amma ina! Har ta yi k'asa tif kafin Agrif ya sunkuya ya d'agota har Nasir ya sa kafarsa ya take yatsunta biyu yana wani irin murzawa da takalminsa sawun ciki Agrif yayi-yayi ya d'aga kafar ya kasa ga Nasrim kukan ma ta daina tsabar azaba sai wani irin d'aga ido sama take kamar za ta sume, shiko Nasir sai da yaji k'aran k'ashin alaman yatsun sun karye ya d'aga k'afar a lokacin Harira ta fito wani irin kuka Harira tasa tayi kan Nasrim ta d'agota har tasuma shiko Agrif neman abin da zai bugawa Nasir ya illata shi kawai yake nema jiyake ko bindiga ya samu zai iya harbin sa wani gilas da a kacire a window Hajja ya hango zaran gilas din yayi da wani irin gudu yayi kan Nasir da yajuya baya yana ta fitar da numfashi Baba Yakubu da sauran masu aiki da gudu sukayi kansu amma kafin su k'araso Agrif yasamu nasaran bugawa Nasir a kai
sai de Allah bai sa yai Koda k'ozani ba dan gilas din ba me saurin bashewa bane saide yadanji ciwo juyowa yayi yana kallon Agrif din yace"ni ka bugawa wannan dan wannan banzar ko".
"Eh na buga kuma Wllh bai isaba sai na sake rama mata kuma Nasrim ba banza bace gaka babban banza". yasake yin kansa za k'arfi yanda idan ya buga masa ko bai faahe ba zai illata shi dak'er aka shiga tsakanin su
shiko Nasir ji yayi ya dake tsanan Nasrim dan ba a taba zagin sa haka ba sai yau a kanta har buga masa gilas din ma bai masa zafima irin zagin da Agrif din yake masa yafi masa ciwo da sauri ya sake zaran Nasrim ahannu Harira zai bugata daidai lokacin motar daddy tayi parking daddy bai jira an bude ba yayi sauri ya fito da sauri yayi saurin k'arasawa inda suke Kabiru yana kokarin karban Nasrim a hannun Nasir amma ya hana wani irin mari daddy ya dauke shi dashi zai sake k'aramasa yaji an rike hannu sa yana juyowa yaga Hajja ce cikin b'acin rai,
Ta ce'' Abdulmajid kashe min shi za ka yi a kan wannan yar taka wadda dalilinta na rasa ubansa, tun daga yanzu Nasir zai fara fuskantan maraici akan y'arka za ka dake sa? Yaushe Abdulsamad ya mutu da har za ka fara manta shi waye ka rufe ido har kana dukar masa tilon jininsa ".?
Ta k'arashe maganan tana sakin kuka
Daddy ma cikin b'acin rai Hajja ba ta taɓa ganin sa da shi ba ya ce
"Haba! Hajja ba ki ga laifin da yayi ba inda ya jefar ta fa?"
Kafin Hajja ta yi magana Nasir ya ce
" Dan bani da ABBA ba me rama ni shi ne za ka dake ni akan y'arka kuma wllh sai na rama a kanta kashe ta zan yi wllh sai na kashe ta".?
Hajja ta ce "A'a daina wannan FURUCIN, zo mu je na duba ko ka ji ciwo Allah zai saka maka, ai maraici ba siya ka yi ba marici yana kan d'an kowa maraici ba hauka ba ne soyyayata kaɗai ta ishe ka, ni ina son ka kai da ya Abdulsamad ya bar min, kai nake gani a madadinsa ba zan yarda a cutar min kai ba a kan wata banza ba".
Ta idasa maganar haɗe da jan shi suka yi gaba.
Mommy da take tsaye ranta idan ya yi dubu ya ɓaci cikin b'acin rai ta ce
" Yanzu Alk'ali abin har ya kai haka har ta kai ka d'aga hannun ka daura akan Nasir da sunan duka kuma a gaban maaikatansa za ka k'ask'antamin shi ?".
shi ma Abba cikin nasa b'acin ran ya ce "Na daka Dr Fanna ko kin fini iko a kansa ne kina ganin kamar kin fi kowa iko a kansa ko, Dr Fanna na fa gaji da irin wannan halin! Ke wacce irin uwa ce? Idan Nasir amana Halima da Abdulsamad suka bar miki ita Nasrim amana ce kai tsaye daga wajen Allah kina shi Ya ba ki kuma amana Ya ba ki kika rik'e amanan wani bawa amma kin banzatar da amanan Allah Sam.... ".
"wane magana kika masa idan ke idonki ya rufe da son Nasir ni nawa a bude yake, ko baki fashimci akwai barazana a FURRUCINsa ba? Cewa fa ya yi duk sanda zai ganki kar ya ganki da ita kuma kar ya ganta a babban falo ko hanyar da zai wuce kar a bi da ita wai hakan ne k'adai zai sa ya kasa cutar da ita, ya kafa miki sharud'a kika amsa kin karba kin yi daidai kenan? ko wannan ba damuwa ba ce a gabana fa aka furta 'yar'uwar y'ata tana cikin wani hali Dr har ga Allah ina son NASURUDDEEN din amma FURRUCINSA ya yi ts'auri a kan Nasrim, ba zan iya kwatanta miki yanda nake jin NASRIM a zuciyata ba, ko Kamal shi ne babba ba na jin sa kamar ita ba zan iya jurewa ba idan wani abu ya same ta".
"To dan Allah alk'ali ka yi hakuri ai yaro ne zai dena".
Shiru ya yi yana sauk'e a jiyar zuciya yace" Allah Ya sa, Ya shirya shi. A dawo lafiya".
Cikin shagwaba ta ce
"Haba Abban Nasrim yau ba rakiya"?
Jinjina kai ya yi yana jan bargo yace I love you my wife sai kin dawo".
taku ta fara a hankali da niyar ta k'arasa inda yake ta yi masa kissing
Cikin wata irin murya ya ce "Allah kika kuskure kika k'araso nan bake ba tafiyar nan dan zan b'ata shiri".
Cak ta tsaya tana masa shagwaba
yinkurin tashi ya yi da gudu tayi hanyar fita si ya ce "Da ki tsaya mana ki ga illar tsokana". Sai da ta kai kofa ha hura masa kiss din a hannu ta yi saurin fita dan tasan in ya kamata bakyau.
********
Bayan kwana biyu haka mommy ta zaunar da Maimunatu da Harira tana ce da su
"kuna ji na ko? Nasir ba ya son ganin k'ananan yara jarirai dan haka nake son ku dinga boye Nasrim idan kun gan shi kar ku yarda ya ganta a tak'aice dai ni ma ba na son ku bari ya gan ta, sannan ina neman alfarmarku wannan ya zama sirri tsakanina da ku ka da ku bari wasu su gane ko da Hajja ce".
Maimunatu tace'' in sha Allah ba mai ji wannan maganar"
Ita ma Harira haka ta faɗa wa mommy.
Mommy ta ce
"Yawwa na gode da yanda kuke kiyaye dukkan dokokina ina jin dadin zama da ku sannan ke Maimunatu iyayen Garba sunje garin ku an gama komai sai saka ranan aure kuma na ji dadin yanda suka ce ba sai kin je ba sun bar komai a hannuna su za su zo nan ayi shiyasa na sa a muku gini a nan kusa da part dina ta baya in sha Allah kafin lokacin za a gama ginin".
Cikin kunya myaimunatu ta yi godiya
haka maaikatan nan sukaci gaba da ɓoye Nasrim duk ko yaran da aka samu akasi Agrif ya nace ya dauketa ya ganta to duka da minsini de sai ta sha su a wajen Nasir, Agrif ko ya ce bai yarda ba dan batuwa da Agrif a kanta dan shi duk abin da Nasir yake masa ba ya damunsa amma muddin ya taba masa Nasrim to za suyi fada a ranan ko abinci ba za su ci tare ba, zai ce yayi jagolgolo ta k'azamar yarinya sosai Agrif yake son Nasrim ita ma Nasrim tunda tayi wayo take son sa, amma ba ta son ko da ganin Nasir tana ganin sa za ta sa kuka kaman za ta shide yau ba Harira ta barta a main parlour ta tafi hado mata madaran ta, ta rarrafa ta fito compound shi kuma Nasir yana zaune ya juya bayansa da litafi a hannunsa dan karatu yake tuk'uru sun kusa zana jarabawan fita daga primary ya ji an rike masa k'afa yana juyowa yayi arba da ita bai gane taba dayake baya tsayawa ya kalli fuskanta sosai murmushi yasakar mata ita ko tana d'agawa ta kalleshi ai k'o ta fashe da wani irin kuka da sauri yasa hannu ya dauketa yana cewa am sorry beautiful baby girl". yana kallon ta yana shafa kwantaccen suman kanta yana murmushi ya sake cewa komai naki me kyau ne baby".
ita ko sai wani irin kuka take tana neman sauk'a ajikin sa,
Agrif da yake baya shima yana nasa karatun ya ji kukan Nasrim yayi yawa ya juya da niyar ya shiga parlour ya ganta a hannan wanda bai taba zato ba
Nasir yace ''Agrif kaga wata beautiful baby girls gashinta mai kyau komai nata me kyau dan Allah yar wacece mommy tayi bak'uwa ne"?
Wani irin dariya Agrif yasa yana tafa hannu ya ce "Ashe ka san mai kyau ce ashe za ka dauke ta, ba kai ka ce ko hanyar da ta bi ka gani ba zaka sake bi ba? Ashe duk k'arya ne''.
Ya k'arashe maganan yana cigaba da dariya, sai alokacin Nasir ya tuno da wacece a hankali ya sake ta ta yi kasa da sauri Agrif ya yi niyar ɗaukota amma ina! Har ta yi k'asa tif kafin Agrif ya sunkuya ya d'agota har Nasir ya sa kafarsa ya take yatsunta biyu yana wani irin murzawa da takalminsa sawun ciki Agrif yayi-yayi ya d'aga kafar ya kasa ga Nasrim kukan ma ta daina tsabar azaba sai wani irin d'aga ido sama take kamar za ta sume, shiko Nasir sai da yaji k'aran k'ashin alaman yatsun sun karye ya d'aga k'afar a lokacin Harira ta fito wani irin kuka Harira tasa tayi kan Nasrim ta d'agota har tasuma shiko Agrif neman abin da zai bugawa Nasir ya illata shi kawai yake nema jiyake ko bindiga ya samu zai iya harbin sa wani gilas da a kacire a window Hajja ya hango zaran gilas din yayi da wani irin gudu yayi kan Nasir da yajuya baya yana ta fitar da numfashi Baba Yakubu da sauran masu aiki da gudu sukayi kansu amma kafin su k'araso Agrif yasamu nasaran bugawa Nasir a kai
sai de Allah bai sa yai Koda k'ozani ba dan gilas din ba me saurin bashewa bane saide yadanji ciwo juyowa yayi yana kallon Agrif din yace"ni ka bugawa wannan dan wannan banzar ko".
"Eh na buga kuma Wllh bai isaba sai na sake rama mata kuma Nasrim ba banza bace gaka babban banza". yasake yin kansa za k'arfi yanda idan ya buga masa ko bai faahe ba zai illata shi dak'er aka shiga tsakanin su
shiko Nasir ji yayi ya dake tsanan Nasrim dan ba a taba zagin sa haka ba sai yau a kanta har buga masa gilas din ma bai masa zafima irin zagin da Agrif din yake masa yafi masa ciwo da sauri ya sake zaran Nasrim ahannu Harira zai bugata daidai lokacin motar daddy tayi parking daddy bai jira an bude ba yayi sauri ya fito da sauri yayi saurin k'arasawa inda suke Kabiru yana kokarin karban Nasrim a hannun Nasir amma ya hana wani irin mari daddy ya dauke shi dashi zai sake k'aramasa yaji an rike hannu sa yana juyowa yaga Hajja ce cikin b'acin rai,
Ta ce'' Abdulmajid kashe min shi za ka yi a kan wannan yar taka wadda dalilinta na rasa ubansa, tun daga yanzu Nasir zai fara fuskantan maraici akan y'arka za ka dake sa? Yaushe Abdulsamad ya mutu da har za ka fara manta shi waye ka rufe ido har kana dukar masa tilon jininsa ".?
Ta k'arashe maganan tana sakin kuka
Daddy ma cikin b'acin rai Hajja ba ta taɓa ganin sa da shi ba ya ce
"Haba! Hajja ba ki ga laifin da yayi ba inda ya jefar ta fa?"
Kafin Hajja ta yi magana Nasir ya ce
" Dan bani da ABBA ba me rama ni shi ne za ka dake ni akan y'arka kuma wllh sai na rama a kanta kashe ta zan yi wllh sai na kashe ta".?
Hajja ta ce "A'a daina wannan FURUCIN, zo mu je na duba ko ka ji ciwo Allah zai saka maka, ai maraici ba siya ka yi ba marici yana kan d'an kowa maraici ba hauka ba ne soyyayata kaɗai ta ishe ka, ni ina son ka kai da ya Abdulsamad ya bar min, kai nake gani a madadinsa ba zan yarda a cutar min kai ba a kan wata banza ba".
Ta idasa maganar haɗe da jan shi suka yi gaba.
Mommy da take tsaye ranta idan ya yi dubu ya ɓaci cikin b'acin rai ta ce
" Yanzu Alk'ali abin har ya kai haka har ta kai ka d'aga hannun ka daura akan Nasir da sunan duka kuma a gaban maaikatansa za ka k'ask'antamin shi ?".
shi ma Abba cikin nasa b'acin ran ya ce "Na daka Dr Fanna ko kin fini iko a kansa ne kina ganin kamar kin fi kowa iko a kansa ko, Dr Fanna na fa gaji da irin wannan halin! Ke wacce irin uwa ce? Idan Nasir amana Halima da Abdulsamad suka bar miki ita Nasrim amana ce kai tsaye daga wajen Allah kina shi Ya ba ki kuma amana Ya ba ki kika rik'e amanan wani bawa amma kin banzatar da amanan Allah Sam.... ".