← Book details Auren Sirri Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 72 OF 149

Sashe 72

Auren Sirri Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

DEENI ya hassala dan takaici Dan Allah ni kun dameni da zance wata banza yarinyar ni wlh duk na Raina da ajinku wlh .
" da har kuka tsaya karewa wannan banzar yarinyar kallo " fahad yace idan kai makahone baka gani mu wlh muna Gani ,kuma dole mu yaba baiwar da Allah yayi .

, 'Ahankali ya ture document din dake zube gabansa ,Coffeen da nablah tasoma siyaya a cup, din yasa 'hannu ya dauka yasoma kurba ahankali ahankali tare da lumshe ritattun idanunshi .

Manir da fahad suka bishi da wani irin kallo ganin abinda yayi . yayinda manir ya cika da mamakin deeni .

Fahad yace mekake nufi yanzu da haka sai da hadeye wanda ke bakinshi sannan yace ga abinda nake nufi nan kuwa , kowa ya yakama gabansa.

Manir yayi murmushi sannan yace to munji amman zai siyayyamu coffee to , juyar da fuskasa yayi wani gefen sannan yace ai duk kuna da 'hannu ,idan baku tashi Sha ba ,kubarshi .

murmushin fahad ya sake yi yace da alamun rashin mutunci kawai kake son yimana .

DEENI ya daga kafadunsa, duka a alamun I don't care .
nan dai suka mai da abun wasa atsakaninsu suka cigaba dayin abinda ya kawo su byn sungama ne DEENI ya Mike yace yana zuwa .

Zuwa yayi ya canza kayan jikinsa zuwa kanan kaya sai kamshi mat Hamilton 27 yake zubawa part din ummi yashiga yana kiran sunanta .. first lov.. were are you .

jin shiru bata amsa bane yasashi kutsa kansa cikin bedroom dinta kai tsaye batare da yayi tunanin wani abu .

Ita kuwa dake zaune tana jerawa ummi kayanta da mai wakin yakawo dazu a Waldrop ta zabura ta Mike tsaye da sauri, duk ilaihi jikinta bbu inda Bai dauki rawa ba saboda tsabar tsoron muryar data jiyo.

Sosai kamshin turarensa ke kusanto dakin alamun yana gab da shigowa . gashi bbu komai ajikinta daga ita sai daguwar riga mai 'hannu harmless cikin sauri sauri ta soma neman hijab dinta .
data cire amman tarasa inda ta ,ajiye .

har yashigo dakin , cak ta tsaya ta kasa kwakwarar motse ,jin tsayuwarsa jingine da kofa yasa take kirjinta ya buga yayinda zuciyata tashiga ..
aikin da tasaba a duk sanda , ta kasance tare da DEENI.

shima tsaye cak yana Kare mata kallo tsab wanda in ba lura mutun yayi da kyau ba.

,ba za'ice ita yake bi da wannan mayataccen kallo ba .
shida kansa yasan in yace yarinyar batayi ba , tabbas karya yake km son ranshi ya fada .

ahankali yakaraso dakin sosai yana sake kiran sunna ummi . kainta a sunkuye a kasa yayinda zuciyata ke wani irin bugawa da sauri cikin siririyar muryata mai cike da in inna ... tace ta.. tana.. bathroom ...

Bai ma tsaya wani sararonta ba ballanantana ya nuna alamun yaji abinda tace ba , tunda shima yaji alamun haka.
juya kawai yayi yabar dakin cikin takunsa ,na tsanyaye namiji .

Numfashi ta sauke tana may sa dukka 'hannuna ta dafe kirjinta dashi tare da sauke ajiye zuciya.

wayyo Allah wannan mutumin ba dai frigita mutane ba .
numfashi ta dinga fitarwa 'ahankali 'ahankali har ta dawo normal .km Sai a lokacin taga hijab din ta washe a gefen 'tsabar rudewa ce tasa takasa Gani.

fitar shi bai fi da minti uku ba ummi tafito tanawa nablah sannu da aiki sannan tasamu waje ta zauna, tana dan Jan nabla da hira , itama dai ba laifi takan dan saki jikinta ummi dan tafi zeenat sau dubu har aka kira sallah suna tare da ummi dan dakin tadawo yanxun saboda aikin da za'a yi Wanda ya hada har da dakin nablah.

Mikewa tayi nablah Tayi tare cewa ummi Ina son naje nayi sallah .

murmushin ummi Tayi haba nablah yanzu sallah ma sai kin tambaya ,ummi girgiza kawai tare da cewa ,jeki kawai kiyi sallahrki kinji ..

MMN SUDAIS CE
[7/12, 7:08 AM] 0mmer Farouk: 💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗

AYSHA A BAGUDO

Page 65

Byn ta idar da sallah magariba,tana zaune akan praymat , tacigaba dayin lazimin daya zame mata jiki .

har sanda taji kiran sallar isha,i daga masallaci dake cikin gidan sannan ta mike ta gabatar da isha'i tayi addu'a sosai .

abinda ke karasa ummi jin kaunar yarinyar nashiga ranta kennan, ita din mai yawan ibada ce ko kadan bata wasa da lokacin sallah.
ahankali nablah ta mike tsaye tana nade praymat . Gaban ya fadi rasssssss sakamakon yiyo sautin muryasa yana yashigowa hade da sallama
yayinda mdm zeenat ke biye dashi tamkar wata bindi.
waje yasamu kusa da umminsa ya zauna yana zuba mata shagwaba tamkar wani karamin yaro .

gabadaya kamshin turarensa yaci koina dakin ummi ta dago idanunta ta kalleshi da kyau tana harararsa wanda kallo daya zakayiwa ummi " ka zagane Hararar tsansar soyayyace irin ta tsakanin uwa da "da" .

Shima kallon umminsa yake yana murmushi tare karyar da kai , ummi ta dubi Zeenat kalli mijinki da kyau sai Naga kmr ya rami yau ko idanuna ne .

Zeenat Tayi murmushi sannan tace bbu wata rama da yayi ,idanunki ne kawai ke ganin hakan.

DEENI ya zabgawa Zeenat harara tare da cewa , rabu daita first love ai bazataga ramar danayi ba , sbd basanin yadda ake kula da miji Tayi ba , amman gabadaya yau a gajiye nike ,ya fadi Haka yaba narke fuska.
abin ma har yaso bawa nablah dariya , Amman ta share kawai saboda ba muhalin yinta bane.

Ummi ta sake duban dan nata da kyau tana murmushin tace kai.. Sam bakasan ka girma ba wlh , kullum shagwaba shagwaba shagwaba tamkar yau aka haifeka ,bazama ka dan rage, ka barwa ya'yanka ba .

,anhakali ya dan dago ya kalli ummi sannan yace haba first love, nasan ko duk duniya nan zan haifa matsayina daban da nasu ,, sai dai kawai zan iya hakura na bar musu sbd mahimmanci su gareni .
, ya karasa fadar hakan ya na murmushi hade da kashewa umminsa idansa daya.
gabadaya sukayi dariya Amman banda nablah dake cigaba da nade abin sallarta.
Cikin sanyi jikin nan nata kmr koda yaushe tabi gefen inda yake zaune wanda dole sai ta wajen zata bi , ta,ajiye abin sallah sannan ta juya zumar basu guri taku daya zuwa biyu Tayi taji muryar zeenat ke.......kalmar da taji kennan cikin isa.. da takama da nunawa nil,adam shi din bakowa bane.

ahankali nablah ta juyo suna fuskartan juna da deeni , batare da ta kalli inda zeenat din take ba .

yadda take kallonsa ta kasan idanunta.
hakan ce takasance dashi domin Shima takasa idanunsa yake satar kallonta, wanda duk nacin mutun bazai taba iya ganewa hakan ba .
zeenat tace kin wani tsaya kina kallona ko nan zan biyoki hade da watsa mata harara sbd yadda taga rana karewa mijinta kallon tsab... cikin sanyi jiki nablah ta hadiye abinda ya tokare mata kirji tare da karaso har inda take , murya a dake tace Gani .... yadda tayi maganar ce tasa zuciyarsa bugawa da sauri , ba zuciyar DEENI kadai ce ta nemi tarwasewa ba har data ummi ,dan sai data tsorata da yadda yarinyar tayi . cike da isa da takama zeenat tayi kwafa tare da aiyana yadda zataci ubanta . tace kije ki hadowa my hrt coffee yanzu ki kawo masa sauran ki bata lokaci da wannan banzar tafiyar take kmr tsutsa .

cikin sanyi murya ta amsa mata da to..... kmr mai shirin zubda kwalla Sannan ta juya ranta a cunkushe ,zuciyarta tamkar zata tarwatse saboda salon da zeenat din ke kokarin son nuna mata .
ko baiwa ce ita iyakarta kennan bata dai kaunar taganta 'tana hutawa .

tafiya kawai take 'tana tuno yan'uwanta da mamanta , batama san sanda hawaye ya wanke mata fuskarta ba .
tasa bayan hannuta tana goge hawayen yayinda wasu ke sake silalowa.
minti biyar tsakani ta sake dawowa dakin hannuta dauke da tire Byn tayi sallama a sanyaye ta janyo wata yar karamar kujerar dake ajiye a gefen ummi gabansa ta ajiye masa wani irin kallon zeenat ke binta dashi may hade da harara harara ne yasa tayi saurin barin dakin zuwa falo .

Bata fi yan mintina da fitowa daga dakin ba shima yafito a natsensa sai kamshin turaren mat Hamilton 27 ke tashi.gabadaya yacika parlour da kashi . da sauri ta dago shanyayun idanunta suka sauka akan fuskarsa wayace manne da kunnensa yana magana cikin sanyi muryar nan tasa tamkar ana busa sarewa .
May dadi da dadin sauraro.

kallon da yabita dashine yasa tasha jinin jikinta hade da dauke idanunta ta sunkuyar da kanta kasa takamo yatsun hannuta tana wasa dasu .
yayinda gafe daya gabanta ke wani irin faduwa har yabar dakin idanunta na kasa batayi kokarin dagowa ba sai data ta kusan minti goma ,ta tabbatar wa kanta yabar gidan gabadaya sannan ahankali ta dago shanyayun idanunta tabi kofar da kallo .

zuciyarta na wani irin dokawa da sauri da sauri a sukwane ta lumshe shanyayun idanunta masu matukar daukar hankali tace kai komai na mutumin nan may kyau ne . Ummi daga inda take zaune ta kwallawa nablah Kira .tashigo batare da ta kalli inda Zeenat ke zaune ba ,itama Zeenat din runtse idanunta tayi tun lokacin dataji ummi takirata .

Nablah tace ummi gani Cike da girmamawa ummi ta zuba mata ido sosai 'tana kallon fuskarta tamkar ba , fuskar dazu ba ,sai Gani tayi yarinyar ta sake canza mata Anya Kuwa bazata fasa hadin nan ba ,karfa tazo tayi datasani . tsawon lokaci nablah najiran ummi kafin daga baya ummi ta nimfasa tace yauwa daman abinda zance miki zaki iya koma dakinki ,dan angama gyaran da za'a yi . nablah tace ta wuce Tare da yiwa ummi sai da safe .'tana shiga dakin sai data frigita daganin yadda yakoma tamkar bashi ba ,komai Na dakin an canza hatta kofar dakin bayi tayi saurin shiga Shima the same tsaki taja kawai 'tana aiyana yadda ake barnar kudi a gidan zuwa gidan an gyara gidan yakai Sau biyu Keenan. Zuciyarta ta kwabeta da Ina ruwanta ,dan Haka ta soma cire kayan jikinta .

11: pm
Chapter 72 · 0% Book details