← Book details Auren Sirri Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 27 OF 149

Sashe 27

Auren Sirri Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

ahankali yakaraso kusa da Ummi ya tsaya yana tmbyrta abinda ke faru sai data ja numfashi sannan ta nuna masa inda zeenat din ke kwance tace zeenat ce ba lfy sai lokacin idanunshi suka kai gareta kwance take akan bed dinshi an lullubeta da bangon rufarsa.
shr yayi tare da zuba mata rikitattun idanunshi.

Daddaden kamshin turarensa tasoma juyowa may matukar sanyi ahankali ta dan lumshe idanunta .

Taku daya zuwa biyu yayi yaja ya sake ya tsaya" sannan ya dubi inda ummi ke tsaye yace me doctor din yace yana damunta?
, doctor din still ya sake mashi bayani kmr dai yadda yayiwa ummi . ahankali ya sake mai idanushin kanta yana cigaba da kallonta wannan shine karo na farko daya tsaya ya Kare mata ,
, sosai kamshin turarensa ke sake kaiwa hancinta farmaki tare da susuta mata duk wata gaba dake jikinta .
.
jikinta da zuciyata suka dauki rawa wani zazzabi mai zafi yayi nasarar sake rufeta sakamakon idanushi dake yawo a gangar jikinta .

Da sauri doctor ya nufo inda take" deeni yasa hannu ya dakatar dashi alamun kada yakarasa gareta" dan wani abu yaji yana taso masa sanda doctor ke masa bayanin abinda ke damunta , tamkar ya auna doctor waje dan takaicin abinda ke cin zuciyarsa.
ganin haka yasa doctor din yace a samo ruwa da towel a goge mata jiki dashi dan tazo daya dubata yaji yadda jikinta ya dau zafi yace zai je ya dauko magani ya dawo cikin sauri ya fice dakin .

A ranta tace doctor dama kayi zamanka dan maganinka kadai ba zai taba min maganin damuwarta ba .

dan ita kadai tasan abinda ke cin ranta .
Wanda tun daga cikin zuciyarta take jin yake taso mata .
tare da haddasa mata tsoro da faduwar gaba.

Tsaye yake har yanzu sai suke hanuwanshi duka da Yayi cikin aljihun wandonsa.

ahankali yasoma takowa zuwa bakin gadon km idanushi akanta.
cikin sanyi ya yaye bargon da aka lullube mata jiki dashi. idanunshi fes akan fuskarta dake lumshe tayi fayu sannan km takara rame sosai ahankali ya daura hannushi saman goshinta .
jin yadda goshinta ya dau zafi da yadda take fidda numfashi sama sama yasanyashi kai hannushi da sauri jikinta.
take yaji abinda ya sake frigitashi .
zafin dake jikinta ya ratsa tafin hannushi" wanda bai san sanda tausayinta ya lullubet shi ba ya dinga jin wani abu na tsigar wa ajikinsa , ya juyo tsaitin Maryam yana harararta yace tsayuwar me kike anan da sauri ta fice daga dakin bata fi minti uku ba Sai gata ta dawo da ruwan ahanunta jikinta na rawa.
azaton zeenat ummi ce ko auntyta zasu goge mata jiki ,amman sai taga DEENi yakarbi robar ruwan a hannu maryam .
Gabadaya suka fita daga dakin har ummi "tare da kulle masu dakin .

Cikin sanyi jiki ya tashi ya dawo gabanta har yanzu sanye yake cikin shadda fara tas sai kamshin turarensa ke tashi a dakin .

ahankali ya cire farar hular shi ya ajiye gefe sannan yasa hannushi duka ya tattarota jikinsa yaja zip din rigar kasa ya zare rigar jikinta ya ajiye gefe ,take jikinta ya sake daukar kirma gabanta yacigaba da faduwa .
tsoro da mamaki suka taru cika zuciyarta. aranta tace wayyo nashiga uku me yaya ke nufi da cire min riga ? yana nufin shi ,zai goge min jiki .
tana ji tana Gani ya cire mata kayan jikinta tsab har bra dinta .
ta rage daga ita sai zani iya cibiya ,sannan ya zauna tare daurata a saman cinyarsa" ya juyo daita suna facing juna taso tasa hannu ta Kare kirjinta amman kasancewar jikinta bbu kwari yasa takasa aiwatar da komai "dan haka ta runtse idanunta gam.
tana jiran taji ruwa ajikinta Amman sai taji shr ahankali ta dan bude idanunta ,DEENi zaune idanunshi kyam akan kirjinta .
da sauri ta maida idanunta ta rufe dan frigice da tsoro ya dauko towel din ya matse sannan yasoma goge mata saman jikinta zuwa kirjinta da fuskarta , ya dimauce da ganin halitatta kirjinta ,hakan yasa yafi goge mata gurin a tare suka dinga sauke ajiyar zuciya .

can yaji ana nouking din dakin yayi sauri ya mayar mata da rigarta sannan yabada izinin shigowa.
doctor ne yashigo da ledar magunguna ahannushi Yace abata abinci taci tukun sannan tasha maganin.
byn tafiyar doctor DEENI yakira ummi Yace akawo tea, en'uwa dayawa suka shigo dakin "ummi da matar uncle din zeenat ,Maryam har ma da shemah . suka dinga jero mata sannu.

byn sun fita ne taji tamkar kar su fita dan bata son abarta daga ita Sai shi.
hakan na sake frigita zuciyarta .
kadan tasha tea din tace takoshi bai wani takurata ba ,ya ballo magani ya Mike mata ba musu tasa hannu ta karba tasha ,dan tasan halinsa ciwonta bazai hana ya jibgeta ba .
Shiya gabadaya a tsorace take dashi.

MMN SUDAIS
💗💗💗💗💗
AUREN SIRRI
💖💖💖
💗💗💗💗💗

AYSHA A BAGUDO

Page 29-30

Byn tasha magani . komawa tayi ta kwanta lomo ajikinsa' tana sakin numfashi sama sama wani iri taji ajikinta lokacin data tsinci kanta kwance kan tattausan jikinsa .
ga kamshin turaren jikinsa gyaraye dana dakin sun buwayi hancinta .
ji take tamkar sukasance haka har abada.
, ahankali tasoma lumshe idanunta har ta rufe su rufff..
bacci ne may nauyi Yayi nasarar daukarta acikin mintina da basu wuce goma ba .

Kyawawan idanushi masu matukar haske da daukar hankali ya zuba mata.
Tare da Kare mata kallo wani zirrrrrrrr ya dinga ji ajikinsa" lokacin daya jita lefe a saman kirjinsa .
da kyar yake jawo numfashin yana fesarwa.
hannushi ya sake kaiwa wuyanta har lokacin jikinta da sauran hucin zafi.
janyota jikinsa ya sake yi .
Tare da ,yasanya hannuwansa duka ya rungume tsam tsam ajikinsa "yana fidda numfashi .
tare da fatan samun saukin zugin da zuciyarsa ke masa wanda shi kansa yarasa dalilin haka.
" Har lokacin bacci take rungume ajikinsa suna musayar numfashin juna mutuwar da jikinsa yayi ne yasashi sake zuba mata rikitattun idanunshi tsawon lokaci yana kallonta
Da kyar yasamu yayo control din kansa cikin sanyi jiki ya zareta daga jikinsa ya kwantar daita ya sake lullube ta da blanket ,sannan ya Mike tsaye yana karkabe jikinsa.

,rigar jikinsa yasoma cirewa ya saura daga shi Sai farar single da wanda shadda.

Wordrob dinsa ya bude ya dauke wasu kayan da zai canza " tare da yashigewa bathroom .

Dakin ya sake dawo byn yagama shirya kansa , cikin farin yadin voyal may matukar taushi da daukar hankali.
Agabanta ya tsaya yana makale links din gaban rigarsa yayinda idanushi ke kanta yana cigaba da kallon fuskarta.

Ahankali ya dinga jin reaction din jikinsa na sauyawa ,yayinda zuciyarsa ke beating tana tsalle tamkar zata bafa masa kirji . wanda shi kansa yarasa dalilin dayasa shi jin haka.
Ahankali ya dauke idanushi a kanta sakamakon
, ji yayi "ana nouking din dakin "yabada umarnin ashigo batare daya tmbyi kowaye ba .
Maryam ce tashigo da sallmarta .
ta gaidashi ya amsa mata a dake .
Cikin sanyi nan nasa
Yakarasa gaban mirrow ya dauki agogon ya daura a tsintsiyar hannushi tare daukar kwalbar turaren ya feshe ilahirin jikinsa ta cikin mirrow din yake wa Maryam magana cikin dakakiyyar " muryasa ki kula daita idan ta farka .idan kika ji zazzabi bai sauka ba ki sanar da first lov ,a tsorace tace ta amsa masa da to...
yana fita ta bi bayansa da kallo cikin ranta tace wayyo zeenat na tausaya miki auren wannan maseefaffe .
,Sai kinyi hakuri da wannan budadden halin na shi .
gefen gadon takoma ta zauna tana sake jin tausayin zeenat din a ranta .

Sosai zeenat tayi bacci baita ta tashi ba.
Sai gaf da magariba.
ji da Maryam tayi jikin zeenat din bbu zafi ko daya .
yasa ta sanarwa da aunty zahra .
Su Aunty zahra suka sata tayi wanka da sallah .
tana zaune akan prayer mat "duk jikinta a mace taji sunce tunda jinkinta da sauki tashiyar akaita tayi sallama da Ummi.

fuskarta cike da tsoro ta dubi aunty zahra tace dan Allah aunty karku kai ni wani guri wlh bani da lfy ..
aunty zahra tace A'a kiyi hakuri yanzu za'a kai ki gidanki kya ji sauki a can.
tana kuka tana komai aka shiryata cikin wata geziner mai ruwan kasa ,Sai kamshi ke tashi ajikinta kai tsaye gurin ummi aka kaita ta mata nasiha mai ratsa jiki ,sannan takara da ce mata takasance may tsananin tsafta da girki domin sune manyan makamai dake kara karfin aure .

Sai km hakuri ,kiyi hakuri kiyi hakuri mamana da duk abinda zaki Gani.gidan aure bbu komai acikknsa Sai hakuri .
Km hakuri shine jigon zaman aure .
duk wata mata da kika ganta zaune gidan mijinta ,hakuri take yi
dan haka ki kula da kyau kinji mamana .
Zuciyar ummi ta tsinke tayi rauni Sai km hawaye shar shar......suka soma zuba , en'uwa ummi da suka zo daga india sukai taba hakuri suma sunyi mata tasu nasiha Sosai .

, ita dai zeenat bbu abinda ummi ta fada wanda bai shiga kunneta ba .
tare da kukan tausayin kanta .
duk sanda ta tuna yau , za'a kaita gidan deeni hankalinta ne ke sake tashi .kuka sosai take har da majina .
ganin irin kukan da zeenat din ke yi yasa ummi kiran deeni a waya .
Chapter 27 · 0% Book details