← Book details Auren Sirri Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 61 OF 149

Sashe 61

Auren Sirri Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kallo daya yayi musu tare da dauke idanunshi daga kansu..
ya tabe baki kai tsaye dinning area ya nufa yaci abincinsa hankali kwance . Sannan yacigaba da zamansa yaciro wayarsa yana operating ..
Km duk yana jin abinda zeenat kecewa da yadda Ummi ke rarrashinta da kwantar mata da hankali akan bbu wata kishiya da za'a yo mata ita kadai ce bbu kari ...
, Jin haka Yasa Daga can inda yake zaune yayi gyaran murya.
,Ummi ce ta juyo 'ahankali Tana dubansa ,yatsansa daya ,ya karkada mata alamun a,a harara Ummi ta sakar masa yayinda shi km ya girgiza mata kai kawai yana tabe baki.

Ahankali Ya Mike tsaye ya dawo kusa da Ummi Ya zauna fuskarsa a hade yace ke.....yi excuse dinmu please zata Mike kennan ummin ta maidaita Dan me zaka korar min yarinya tana cikin halin damuwa ?
idan har baka shirya yin magana dani bane tana nan kana iya barin maganar har zuwa wani lokaci dan bbu inda zata ke koma kiyi kwanciyar kinji..
,koma kuwa tayi kwanciyarta kmr yadda Ummi tace amman har lokacin Hawaye bai daina bin kuncinta ba .

Kafadarsa ya sake dagawa alamun bai damu ba da abinda Ummi tace ba ..
Wayarsa ce ta dauki kara sauti mai dadi Mikewa tsaye tare da pic din call din ya manna a kunnenshi tana tafiya .

Hello ..Yaya ganin nan zuwa yanzu sannan yakashe wayar yabar musu gidan gabadaya .

Yana fita Ummi ta dauki wayarta takira hajiya turai bagun farko hjy turai ta dauki wayar da sallamarta " bbu abinda Ummi tasoma tmbyrta sai an km samu kuwa ?

Ummi tayi hakan ne Dan kada zeenat din tadago wani abu dangane da shirinta.

bangaren hjy turai kuwa cewa Tayi eh ansamu amman sai dai guda daya ce km Tanada dan shekara ,Ummi tace kmr shekara nawa gareta ?

eh zata kai kmr 23 haka inji cewar hjy turai ok ki kawota naganta hjy turai tace sai dai kibari zuwa gobe idan Allah Ya kai mu ' latifa zata zo gurina idan zata wuce gida zan bari takaraso miki da yarinya ,Ummi tace ok shikennan sai sun zo din takashe wayarta tare yiwa hjy turai godiya .

Washegari da misalin karfe hudu daidai latifa takawowa Ummi shafa. kallo daya Ummi tayiwa yarinyar taji kwata kwata bata kwanta mata arai ba a ranta tace itama kennan Ina Ga oga DEENI.
tasan ma bazai wank mu,ammultu da yarinyar ba , girgiza kai kawai Tayi byn tasa an kawowa latifa abin motsa baki .

,'ahankali Ummi ta Mike tsaye ta nufi wani kofa tayi warning din glass tare da cewa latifa ta biyo bayanta , latifa ta Mike 'ahankali tabi bayan Ummi .

Wani madaidaici parlour Ummi takai latifa byn sun zauna ne Ummi tace Kira sunan lafita ta amsa kina jina latifa ..yarinyar nan bata min ba km nasan tunda bata min ba da wuya tawa mai gidan Shima kinsa shi da kyankyami tsiya .

dan haka asamo wata kota gurinki ne amman dai zan bar Ita wannan din kafin asamu wata ,dan aikin gida sbd aikin nayiwa laraba yawa ,latifa tace ok babu damuwa ,daman kuwa akwai wata yarinya dake neman aikin gida irin wannan amman kibari zan miki kokari inshallahu .
Ummi tace shikennan latifa Nagode sosai suka yiwa juna sallama sannan latifa ta wuce .

Byn fitar DEENI daga gida kai tsaye gidan yayansa mahamud dake cikin estate din yayi .

zaune suke shida da Yaya Muhamud din babban parlour baki na gidansa .
Shr yabiya baya kafin Yaya Muhamud ya numfasa tukun yasoma magana kmr haka DEENI abinda yasa nace kazo nan ina nemanka ,akwai magana may mahimmanci da nake son muyi akan company,s dinmu.
,kaga dai yanayin danake ciki halin yanzu nima girma ne yake zuwa min yayinda abubuwa ke sake min yawa ni kadai raina nake kokari akan lamuran company,s dinmu na cikin gida da sauran kasashen duniya shine naga yakamata ace kaima , ka'ajiye wannan aikin naka kazo mutaru mu kula da komai Tare.

,kasan mutane wasu basu da amana , amman yaka Gani akan lamarin .. DEENI yayi shr kawai yana sauraransa har yakai karshen zance ,sannan ya dan yi murmushi karfin hali har dimple dinsa ya lotsa ,rasa mezai cewa yayansa yayi dan haka yace shikennan Yaya zan duba nagani idan hakan zai yiwu dan gsky Ina matukar son aikina km banason abinda zai rabani dashi .

,DEENI..yaya Muhamud ya sake kiran sunanshi DEENI ya dago da idanushin yana dubansa dasu , wannan aikin naka yana mahimmanci a rayuwa Shima km talafawa company,s dinmu haka ,amman abinda nake so dakai kaduba din kmr yadda kace ,nan suka bar zance suka shiga hirar duniya har DEENI yake sanar masa da abinda mama ta abuja, tayiwa Ummi akan zeenat , Shima Yaya Muhamud din baiji dadin abinda Tayi ba .

Bayan wata biyu

Al'amarin duniya fa yasoma damun Zeenat tayi mugun tada hankali kan maganar aunty,n su Ita DEENI gabadaya afrigice take da komai , kawai burinta ahalin yanzu bai wuce kawai ta ganta dauke da ciki ba .

amman kwata kwata hakan yaki samuwa gareta ga lokacin na tafiya , gabadaya hankalinta a tashe yake matuka.

haka ma ta bangaren Ummi itama hankalinta a tashe yake da yadda take ganin yanayin diyar tata.
,shi kuwa gogan sam bbu ruwanshi da wani tashin hankali da suke cikin .
' hakar gabansa kawai yake domin komai yana tafiyar masa yadda yake so daga office har gida .

Sakamakon damuwar da zeenat tasawa ranta ne har hakan yajawo ta Dan rame kadan kallo daya mutun zai mata yagane tana cikin tension .
" Ko school ma sai da wata friend dinta may suna halima ta gane Tana cikin damuwa dan haka tmbyeta ,zeenat bata wani boye mata komai dangane da halin datake ciki ba .

,nan fa halima tace Ina ai baki Ga ta zama ba zeenat kishiya fa ....Ai ni ko sunanta ban kaunar ji ballanantana tashigo min gida gaskiya kitashi tsaye tun wuri , zeenat marairaice murya hali bansa yadda zanyi ba ,bansan koina ba , hospital kawai nasa km muje ,hali tace ok kada ki damu akwai wani mutun danasan yana bada maganin haihuwa ,kibari zan rakaki gurinsa amman a sango ota dake hanyar abe okuta yake ,idai zaki zan rakaki ,zeenat najin haka ta kamo hannunwan halima duka cikin hannuta Tana murna dan Allah hali kitaima min koma Ina ne zani indai zan samu cikin haihuwa nidai banason mijina yayi min kishiya dan bana kaunar zama daita a rayuwata ta duniya km nasan rashin haihuwar nan zai iya bawata shigo min gida .
gara mutuwata danaga zuwan wannan rana.
,hali tace haba kada ki damu zan taimakamiki ai murigada mun zama daya .
Nan fa suka bar zance da zumar gobe zasu tafi songo ota .😭😭😭

Washegari kuwa da wuri zeenat tashirya har Ummi tacewa yana Ga yau kinashiri cikin sauri haka.
Murmushi Tayi kawai Tayi wlh , Ummi lecture gareni da wuri shiyasa kika ganni haka.
Ummi tace ok , koke fa haka nake son ganinki cikin walwala da kazarkazar tattare kwanciyar hankali .
,banason ganinki cikin damuwa zeenat ta sake yin murmushi tare da cewa Ummi sai ta dawo Ummi tayi mata addu'a .

Haka suka je gurin may bada maganin Ita da hali batare da sanin kowa ba .
Bawani abu mutumin yabata ba, baya Ga garin magani baki yace ta da lemun tsami ta dinga da sha da zarar sun gama sex da mijinta har sai maganin yakare har yana sake tabbatar mata maganin bazai kai Ga karewa ba zata samu ciki . Uhmmmm

da murnarta dawo gida km Tayi kmr yadda mutumin yace Tayi.
,tare da zaman jira tsammani , har zuwa lokacin zuwan period dinta, bata Ga jini ba , .

Tacigaba da shan magani ,murna kuwa kmr ta Yaya ,dan duka tunanin ciki gareta amman byn kmr sati daya da shanye maganin sai Ga jini ..
ranar kuwa data Ga jinin zaman dirshan Tayi a bayi "tare da daura hannuta duka bisa kai ta saka kuka a gurin .

,wunin ranar bbu inda taje ko parlour kasa bata keko ba , , Ummi zaune ita da DEENI wanda Bai dade da dawo ba zaune yake kusa da ummi suna hira ,ganin shr shr bata zeenat ba yasata zuwa dakinta , da fari ta dauka ko bacci take ,ganinta kwance tana sheshekar kuka ne yasa gaban Ummi faduwa da sauri takaraso inda take kwance Tana kiran sunanta ke zeenat.. lfy ki kuwa ,kukan me kike haka ?

Aiko zeenat naganin Ummi ta sake rushewa da wani sabon kuka km tashiga gayawa Ummi abinda ya faru amman sai dai ta boye bata gayawa Ummi zance zuwa gurin amso magani ba .

Allah sarki Ummi baiwar Allah haka ta dinga rararshinta Tana kuka itama. jin shr yayi yawa ne yasa DEENI biyo bayan Ummi yaga ko lfy aiko yaga abin mamaki dan zaune ya tadda ummi yayinda zeenat din ke rungume ajikinta suna aikin kuka tamkar wayan,da akayiwa mutuwa mai zafi.
Yana ganin haka yasan iskancin zeenat din ne ya motsa ,dan haka bai wani damu ba ko tada hankalinsa.
" dan yasan zance gizo baya wuce na koki ,sai ma tsawar daya dakawa zeenat din ..Tare da nunata da yatsansa daya ke....... banson wulakancin da rainin hankali fa yazaki zo ki tasa min uwa gaba da kuka?
Ke...duk matsalar ki sai sanya mutane ciki.
Chapter 61 · 0% Book details