Sashe 98
Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Saida ya buɗe mata ta shiga ta zauna sannan shima ya dawo ya bude gefen driver ya shiga suka dauki hanya, suna tafe yana ƙara kwantar mata da hankali, duk da shima karfin hali yakeyi, idan da zai samu dama shima kukan zaiyi sai dai kasancewar shi namiji yasa ya dake yana lallashin ta, ita ko sai ruwan hawaye take zubar wa tana shehseka, sun zo dai dai kofar gida har mai gadi ya wangale get, wayar shi dake hannunta yayi ringing, ko dubawa batayi ta mika mishi, ganin Amir ne me kiran yasa ya daga, daga can bangaren Amir cikin yanayin tsantsar farin ciki yace"broh matata ta haihu, yanzun nan yanzu haka muna standard hospital ko sallaman mu ba'ayi ba." Aslam a ruɗe yace "iyeee kace ta haihu." Ai jin maganar haihuwa yasa ta tsaya da kukan shagwaban da take yi, tare da zazzaro manyan idanunta ta waje gabanta na faduwa tace"honey waye ya haihu" cikin washe baki yace"Amira ce" wani irin zabura tayi ta rungume shi tana faɗin "alhmdllh alhmdllh Allah mun gode maka." Tana cikin murnar kuma yaga tayi tsit, can kuma sai kuka.........
Kwana biyu kun juna shiru wlh nadan samu uziri ne kuyi tamin hakuri dai.
Oum Ummeetarh
07041130088💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu}
Page 121
Ko ba'a faɗa ba yasan kukan me take yi, ta ke yaji gaba ɗaya jikin shi ya ƙara yin sanyi, haka dai ya daure ya shiga rarrashin ta, yana kwantar mata da hankali, ɗago fuskar ta da yayi gaje gaje da hawaye tayi daga jikin shi ta zuba mi shi idanun ta da sukayi jajur tana kallon shi, shima nashi idanun ya zuba a cikin nata, tare da kamo hannayen ta ya riƙe cikin nashi yana murzawa a hankali, a hankali ta buɗe bakin ta tace "ya Aslam sai yaushe ne nima zan haihu, sai yaushe nima zan samu ciki, tsoro nake yi kar ace na kasa cika maka burin ka na samun haihuwa, na San kana son haihuwa sosai kana son kaga gudan jinin ka a duniya, nima kuma ina so domin duk abin da Aslam yake so shi Asmah take so. Inajin tsoran na kasa cika maka wannan burin naka, har hakan ya janyo ka juya min baya wata rana, Wanda duk ranar da hakan ta kasan ce sai dai a kwashi gawar Asmah, domin Asmah baza ta iya rayuwa ba tare da Aslam ba, dan Allah ya Aslam kamin alkawari komai rintsi baza ka juya min baya ba." "Shiii!" Ya faɗa tare da daura dan yatsar shi akan lips ɗinta, girgiza mata kai yayi tare da cewa "kada na sake jin kwatan kwacin irin wadannan maganganun suna fitowa daga bakin ki, Aslam na Asmah ne, ruwa da iska babu abin da zai sa ya juya mata baya, iya wuya muna tare, kuma in-sha Allah zaki samu ciki ki haifa min kyawawan ƴaƴa masu kama dake, zaki shayar dasu kamar kowacce uwa, zaki basu tarbiyya irin Wanda mummy ta baki, kinji my hussy." Gyada kai tayi hawaye naci gaba da kwaran ya daga idanunta ta, sakin hannayen ta yayi, ya jayo fuskarta daf da tashi a hankali ya shiga dauke hawayen dake zubowa a idanun ta da harshen shi, yana gamawa kuma ya haɗe bakin su ya shiga kissing dinta a hankali, sai da yayi ma'ishi ya dago yana kallonta itama shi take kallo yace"oya yi murmushi." Wani murmushi tayi Wanda da gani yasan iya fuska kawai ya tsaya.girgiza kai yayi yace "wannan bai yi ba." Sake wani tayi Wanda babu banbancin dana farko, sake girgiza kai yayi yace "wannan ma bai min ba, bari kiga irin Wanda nake so." Kafin ta Ankara taji ya fara mata cakulkuli, ba shiri ta shiga kwalkwala dariya tare da kokarin zillewa tana buge hannun shi.
Ganin haka yasa ya kyale ta, shima yana mata dariya, hararan wasa ta watsa mai cikin muryar shagwaɓa tace" Kai ko ya Aslam yanzu dana mutu fa, baka San ance cakulkuli kanin mutuwa bane." Cikin kwaikwayon muryar ta yace"to ba kene kika ki yi min murmushi ba tun dazu sai kuka kikeyi kina ta min asarar hawayen ki masu daraja."dungure mai kai tayi cikin sigar wasa tare da murguɗa baki.
Dariya yayi tare da cewa "bari dai mu karasa ciki, na baki wani labari mai daɗi." Ya karashe maganar yana kokarin tada motar, riƙe hannu shi tayi tace"dan Allah ya Aslam ka kaini naga babyn mu hankali na ya kwanta." Yace"eh to da nima naso hakan, amma yanzu na canja shawara, kimu shiga daga ciki ki ɗan dumama ni sannan mu tafi." Ya kara she maganar yana ɗage mata gira tare da sakar mata wani shu'umin murmushin da ita kaɗai tasan fassarar sa, ba yadda ta iya, tunda ya bukaci hakan tasan idan ba yi yayi ba kuwa baza ta samu sa'ida ba, don haka bata ƙara cewa komai ba ya tada motor suka ƙarasa ciki.
Kasancewar tana son zuwa ganin baby duk rabin hankalin ta nacan yasa ta ringa yin komai sauri sauri, hakan kuwa yamai daidai sakar mata ragamar komai yayi ita ta buga wasan, Bayan sunyi wanka abinci ta girka musu mai sauki sukaci, basu suka bar gidan ba kuwa sai Bayan la'asar.
Koda suka isa asibitin an sallame su, Aslam yace "gida zamu je kenan." Ya faɗa yana karya kan motar ya dauki hanyar zuwa albishir inda gidan Amir yake.
Suna tafe suna hirar su ta masoya Wanda duk rabin hirar akan batun babyn su ne suma, inda musu ya barke Asmah tace namiji take so shi kuma yace mace yake so.
Wayar ta ne ya dauki ringing shuru sukayi duka ta Ciro wayar daga cikin hand bag dinta, ganin me kiran ne ya saka ta sakin murmushi, kallon ta yayi yace"wake kira." Tace "matar Dr." Ya mutsa fuska yayi alamar bai gane ba, kafin ya tambayeta wacece haka har tayi picking call din ta saka a amsa kuwwa sai ji yayi muryar batool ya karaɗe mai kunne tana cewa"yar uwa ina kika shige ne tun a asibiti nake ta zuba idon ganin ta ina zaki bullo, gashi har anyi sallama mun wuce gida shiru shine nace bari dai na kira naji ko lafiya." Murmushi tayi tace"ke dai bari yar uwa tun ɗazu naso zuwa, wani dan uziri ya rike ni, amma gani a kan hanya yanzun nan insha Allah." Dariya batool ta kwashe dashi cikin son ta tsokane ta tace "uzirin oga babba ba ai nasan shi ya rike mana ke, yana nan yana danne mana yar uwa amma in yazo nan mu yai ta wani mazurai, yana ciccin magani, fuskar nan a haɗe kamar wani na Allah, zaki rantse bazai iya kallo mace ba balle yayi eh yane da ita, to munsan komai." Wani iri wawan burki ya taka jin abinda batool ke fadi Asmah kam wani dariya me haɗe da tari ya sarke ta lokaci guda, batool tace "wlh kuwa sister ba batun dariya bane ai da ganin idanun wannan mutumin zaiyi jaraba ba kaɗan ba, dama kinsan ance irin shiru shirun nan sunfi kowa naci a wannan fanni, a fuska kamar in an saka musu yatsa a baki baza su iya cizawa ba." Dariyar da yaci karfin ta yasa ta katse kiran cikin sauri tana kallon Aslam daya kasa rufe baki tsabar mamaki da al'ajabi sai kuwa zazzaro ido yake yi yana muzurai take maganar batool ya fado mata a rai, ta kara kwashe wa da dariya har da riƙe ciki.
Shima dariyar ne ya kama shi ya shiga taya ta, Girgiza kai yayi yace"lallai ma yaran nan haka na zama a wajen su, haka suka raina ni dama, lallai ma yaran nan sunga gadon barcina ." Ya faɗa cikin tsantsar mamaki dan shi abin ya ba'in daure mashi kai inda wani ya gaya mai wlh baza yarda ba, duk da yasan batool zata aika, indai ita ce daya sani.
Cikin dariya tace "honey kasan batool shakiya ce, babu Wanda ta ragawa, idan abin ta ya motsa har su daddy yi musu take." Yace "aiko dai zata ci kaniyar ta yau a hannu na, sai ta maimaita abinda ta faɗa a gaba na badai zama da wancen ƙara min ɗan iskan ya kara koya mata fitsara ba." Cikin zaro ido tace "kai honey kar kasa naƙudan dole ya taso mata, kasan dai ko giya ta sha baza ta iya maimaita wannan maganar a gaban ka." Yace "ta ko sha mari, ai har yanzu ina nan a Muhammad Aslam ɗina nada da ta sani." Dariya tayi tace "haba dai honey matar wani ce fa." Yace "matar wani ko? To ko mijin nata ne yamin dukan tsiya zan mai balle ita dana ma wanka na goya a baya na." Dariya ta kwashe dashi tare da cewa "Dr din zaka daka." yace "kina mamaki ne ." tace "eh mana." Yace "ki tambaya kiji koda muna yara dukan tsiya nake mai yayi ta kuka hawaye da majina shaɓe shaɓe gashi fa ya fini girma a lokacin"Asmah don dariya harda hawaye ciki dariya tace "dan Allah ya Aslam ka tada motar mu wuce kar kasa cikina ya fashe dan dariya." Dariya yayi tare da ta da motar, har sun far tafiya kiran Amir ya shigo nashi wayar ɗagawa yayi yace "angon ƙarbi angon ƙarni." Amir murya cike da damuwa yace "dan uwa sun kassara ni." Aslam cikin ɗan ta shin hankali yace "su waye kuma." Amir yace "su mummy." Aslam yace "me suka yi." Amir kamar zai fashe da kuka yace"wai bana nan na je gida kwaso wasu kaya, likita ta basu sallama, wai kafin na ƙaraso sun wuce da ita can family hause wai wani acen zata yi wanka sai nan da kwana ar'ba'in zata dawo." Dariyar ƙeta Aslam ya fashe dashi tare da cewa "subhanallahi sannu." Sannan ya ci gaba da kwasar dariya irin mai kara cusa haushin nan, Amir daya gama ƙulewa cikin fushi yace "shege dan iska kawai." Tare da katse kiran ma gaba ɗaya.
Kwana biyu kun juna shiru wlh nadan samu uziri ne kuyi tamin hakuri dai.
Oum Ummeetarh
07041130088💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu}
Page 121
Ko ba'a faɗa ba yasan kukan me take yi, ta ke yaji gaba ɗaya jikin shi ya ƙara yin sanyi, haka dai ya daure ya shiga rarrashin ta, yana kwantar mata da hankali, ɗago fuskar ta da yayi gaje gaje da hawaye tayi daga jikin shi ta zuba mi shi idanun ta da sukayi jajur tana kallon shi, shima nashi idanun ya zuba a cikin nata, tare da kamo hannayen ta ya riƙe cikin nashi yana murzawa a hankali, a hankali ta buɗe bakin ta tace "ya Aslam sai yaushe ne nima zan haihu, sai yaushe nima zan samu ciki, tsoro nake yi kar ace na kasa cika maka burin ka na samun haihuwa, na San kana son haihuwa sosai kana son kaga gudan jinin ka a duniya, nima kuma ina so domin duk abin da Aslam yake so shi Asmah take so. Inajin tsoran na kasa cika maka wannan burin naka, har hakan ya janyo ka juya min baya wata rana, Wanda duk ranar da hakan ta kasan ce sai dai a kwashi gawar Asmah, domin Asmah baza ta iya rayuwa ba tare da Aslam ba, dan Allah ya Aslam kamin alkawari komai rintsi baza ka juya min baya ba." "Shiii!" Ya faɗa tare da daura dan yatsar shi akan lips ɗinta, girgiza mata kai yayi tare da cewa "kada na sake jin kwatan kwacin irin wadannan maganganun suna fitowa daga bakin ki, Aslam na Asmah ne, ruwa da iska babu abin da zai sa ya juya mata baya, iya wuya muna tare, kuma in-sha Allah zaki samu ciki ki haifa min kyawawan ƴaƴa masu kama dake, zaki shayar dasu kamar kowacce uwa, zaki basu tarbiyya irin Wanda mummy ta baki, kinji my hussy." Gyada kai tayi hawaye naci gaba da kwaran ya daga idanunta ta, sakin hannayen ta yayi, ya jayo fuskarta daf da tashi a hankali ya shiga dauke hawayen dake zubowa a idanun ta da harshen shi, yana gamawa kuma ya haɗe bakin su ya shiga kissing dinta a hankali, sai da yayi ma'ishi ya dago yana kallonta itama shi take kallo yace"oya yi murmushi." Wani murmushi tayi Wanda da gani yasan iya fuska kawai ya tsaya.girgiza kai yayi yace "wannan bai yi ba." Sake wani tayi Wanda babu banbancin dana farko, sake girgiza kai yayi yace "wannan ma bai min ba, bari kiga irin Wanda nake so." Kafin ta Ankara taji ya fara mata cakulkuli, ba shiri ta shiga kwalkwala dariya tare da kokarin zillewa tana buge hannun shi.
Ganin haka yasa ya kyale ta, shima yana mata dariya, hararan wasa ta watsa mai cikin muryar shagwaɓa tace" Kai ko ya Aslam yanzu dana mutu fa, baka San ance cakulkuli kanin mutuwa bane." Cikin kwaikwayon muryar ta yace"to ba kene kika ki yi min murmushi ba tun dazu sai kuka kikeyi kina ta min asarar hawayen ki masu daraja."dungure mai kai tayi cikin sigar wasa tare da murguɗa baki.
Dariya yayi tare da cewa "bari dai mu karasa ciki, na baki wani labari mai daɗi." Ya karashe maganar yana kokarin tada motar, riƙe hannu shi tayi tace"dan Allah ya Aslam ka kaini naga babyn mu hankali na ya kwanta." Yace"eh to da nima naso hakan, amma yanzu na canja shawara, kimu shiga daga ciki ki ɗan dumama ni sannan mu tafi." Ya kara she maganar yana ɗage mata gira tare da sakar mata wani shu'umin murmushin da ita kaɗai tasan fassarar sa, ba yadda ta iya, tunda ya bukaci hakan tasan idan ba yi yayi ba kuwa baza ta samu sa'ida ba, don haka bata ƙara cewa komai ba ya tada motor suka ƙarasa ciki.
Kasancewar tana son zuwa ganin baby duk rabin hankalin ta nacan yasa ta ringa yin komai sauri sauri, hakan kuwa yamai daidai sakar mata ragamar komai yayi ita ta buga wasan, Bayan sunyi wanka abinci ta girka musu mai sauki sukaci, basu suka bar gidan ba kuwa sai Bayan la'asar.
Koda suka isa asibitin an sallame su, Aslam yace "gida zamu je kenan." Ya faɗa yana karya kan motar ya dauki hanyar zuwa albishir inda gidan Amir yake.
Suna tafe suna hirar su ta masoya Wanda duk rabin hirar akan batun babyn su ne suma, inda musu ya barke Asmah tace namiji take so shi kuma yace mace yake so.
Wayar ta ne ya dauki ringing shuru sukayi duka ta Ciro wayar daga cikin hand bag dinta, ganin me kiran ne ya saka ta sakin murmushi, kallon ta yayi yace"wake kira." Tace "matar Dr." Ya mutsa fuska yayi alamar bai gane ba, kafin ya tambayeta wacece haka har tayi picking call din ta saka a amsa kuwwa sai ji yayi muryar batool ya karaɗe mai kunne tana cewa"yar uwa ina kika shige ne tun a asibiti nake ta zuba idon ganin ta ina zaki bullo, gashi har anyi sallama mun wuce gida shiru shine nace bari dai na kira naji ko lafiya." Murmushi tayi tace"ke dai bari yar uwa tun ɗazu naso zuwa, wani dan uziri ya rike ni, amma gani a kan hanya yanzun nan insha Allah." Dariya batool ta kwashe dashi cikin son ta tsokane ta tace "uzirin oga babba ba ai nasan shi ya rike mana ke, yana nan yana danne mana yar uwa amma in yazo nan mu yai ta wani mazurai, yana ciccin magani, fuskar nan a haɗe kamar wani na Allah, zaki rantse bazai iya kallo mace ba balle yayi eh yane da ita, to munsan komai." Wani iri wawan burki ya taka jin abinda batool ke fadi Asmah kam wani dariya me haɗe da tari ya sarke ta lokaci guda, batool tace "wlh kuwa sister ba batun dariya bane ai da ganin idanun wannan mutumin zaiyi jaraba ba kaɗan ba, dama kinsan ance irin shiru shirun nan sunfi kowa naci a wannan fanni, a fuska kamar in an saka musu yatsa a baki baza su iya cizawa ba." Dariyar da yaci karfin ta yasa ta katse kiran cikin sauri tana kallon Aslam daya kasa rufe baki tsabar mamaki da al'ajabi sai kuwa zazzaro ido yake yi yana muzurai take maganar batool ya fado mata a rai, ta kara kwashe wa da dariya har da riƙe ciki.
Shima dariyar ne ya kama shi ya shiga taya ta, Girgiza kai yayi yace"lallai ma yaran nan haka na zama a wajen su, haka suka raina ni dama, lallai ma yaran nan sunga gadon barcina ." Ya faɗa cikin tsantsar mamaki dan shi abin ya ba'in daure mashi kai inda wani ya gaya mai wlh baza yarda ba, duk da yasan batool zata aika, indai ita ce daya sani.
Cikin dariya tace "honey kasan batool shakiya ce, babu Wanda ta ragawa, idan abin ta ya motsa har su daddy yi musu take." Yace "aiko dai zata ci kaniyar ta yau a hannu na, sai ta maimaita abinda ta faɗa a gaba na badai zama da wancen ƙara min ɗan iskan ya kara koya mata fitsara ba." Cikin zaro ido tace "kai honey kar kasa naƙudan dole ya taso mata, kasan dai ko giya ta sha baza ta iya maimaita wannan maganar a gaban ka." Yace "ta ko sha mari, ai har yanzu ina nan a Muhammad Aslam ɗina nada da ta sani." Dariya tayi tace "haba dai honey matar wani ce fa." Yace "matar wani ko? To ko mijin nata ne yamin dukan tsiya zan mai balle ita dana ma wanka na goya a baya na." Dariya ta kwashe dashi tare da cewa "Dr din zaka daka." yace "kina mamaki ne ." tace "eh mana." Yace "ki tambaya kiji koda muna yara dukan tsiya nake mai yayi ta kuka hawaye da majina shaɓe shaɓe gashi fa ya fini girma a lokacin"Asmah don dariya harda hawaye ciki dariya tace "dan Allah ya Aslam ka tada motar mu wuce kar kasa cikina ya fashe dan dariya." Dariya yayi tare da ta da motar, har sun far tafiya kiran Amir ya shigo nashi wayar ɗagawa yayi yace "angon ƙarbi angon ƙarni." Amir murya cike da damuwa yace "dan uwa sun kassara ni." Aslam cikin ɗan ta shin hankali yace "su waye kuma." Amir yace "su mummy." Aslam yace "me suka yi." Amir kamar zai fashe da kuka yace"wai bana nan na je gida kwaso wasu kaya, likita ta basu sallama, wai kafin na ƙaraso sun wuce da ita can family hause wai wani acen zata yi wanka sai nan da kwana ar'ba'in zata dawo." Dariyar ƙeta Aslam ya fashe dashi tare da cewa "subhanallahi sannu." Sannan ya ci gaba da kwasar dariya irin mai kara cusa haushin nan, Amir daya gama ƙulewa cikin fushi yace "shege dan iska kawai." Tare da katse kiran ma gaba ɗaya.