← Book details Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 95 OF 126

Sashe 95

Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hankali kwance take jegonta bata da matsalar komai babu abida ke damunta sai kewar mijinta, bayan haihuwartan nan , abin ma saiya daɗa nunkuwà, kullum dashi take kwana take tashi a zuciyarta ji take kamar tayi tsunstuwa ta ganta a agabanshi, ta mika mishi ɗanshi, cikin farin ciki,ta kusa kai matakin da baza ta iya jurewa ba, jira takeyi yaronta yayi kwari, ta lashi takobin zata koma gidan mijinta koda son ransu ko babu, koda tsiya koda tsiya tsiya.

~9ja~

Yau kimanin wata biyar kanen da auren yan matan mummy,kuma har zuwa wannan lokacin cikinsu babu wacce ta taba zuwa gida da sunan ganin gida, kowacce tana gidanta hankali kwance, duk da kuwa cikinsu ba wacce batayi nacin son zuwa gida ba amma mazajen suka hana wannan kuwa umarnin alhaji baba ne.

Soyayya kamal da khadija ba'a magana, tattalin da kulawa suke ba juna na musamman, idan kaga yadda suke gudanàr da rayuwarsu zaka dauka sunyi shekara goma suna soyayya kafin suyi aure, a halin yanzu Khadijah Nada cikin ta dan wata huɗu.

Haka ma Amir da Amira sukam bama a magana, kalar nasu salon soyayya ta dabance, basa jin kunyar uban kowa a gaban kowa nuna ma juna soyayya sukeyi, ƙiri ƙiri mutane suka guji zuwa gidansu, saboda idan kaje indai kana da kunya, ta baza ka iya awa ɗaya a gidan ba,suma dai a kwai cikin ɗan luv, saidai fatan Allah ya raba lafiya.

Su batool ma yanzu komai nomal,babu abinda suke sai shan soyayya da cokali mai yatsu, bangaren yadda sukeji da cikin su kuwa ba'a cewa komai,tunkan a haife shi, shikaran kanshi cikin yasan shi dan gata ne, abinka da masu abin duk sati ake scanning, ta bangaren maah ma ba'a barta a baya ba, duk abinda ta gani indai na jariri ne siya takeyi ta ajiye, abin kwalama kuwa na masu cikin kullum cikin yi takeyi tana aikama batool dashi, bama ci takeyi ba wani bin saidai Dr yaci idan Wanda zai iya cine, ita dai barta da cabbage dinta, yanzu kam an samu ci gaba ta daina cinshi gaya, saidai ta kwada da kulikuli taci, rigima kam yayi sauƙi a gurin batool saidai kunsan ance mai hali baya fasa halinsa, duk da haka duk randa ya tabota haka zata kwana tana masifa, musamman yanzu da wata Dr a gurin aikinsu ta nace tana sonsa, tunda batool ta samu labari ya shiga uku ko minti talatin ya kara akan lokacin da yake dawowa haka zai sameta ta cika tayi fam, komai zai ce mata baza ta yarda ba kawai gurin Dr basira ya tsaya, kishin sa take sosai da sosai ji take da tana da hali da nikab zata saka shi ya dinga sakawa, saukin shi ma yanzu yana da loggonta data fara zai lalubeta ya fara sakar mata zafafan romance daga nan zancen zai mutun sai kuma na gobe.

A bangaren zahra kam, yanzu babu abida zamu ce sai alhmdllh, tsakaninta da miji babu komai sai tsantsar soyayya da kaunar juna, da gasken fa baby take a gurin Barr Adam ji yake da ita kamar Yar jinjira, musamman yanzu data samu ciki, kula yake bata na musamman kamar ya hadiyeta, tsakanin da maryama yanzu kuwa babu komai sai girmama juna da mutunta juna, dama zahra kwata kwata bata da matsala, matsalar daga maryama ne, kuma a halin yanzu gaba daya tayi laushi, bayan dawowarta Barr a gaba ya sakata ya mata nasiha tare da sanar da ita wlh ta gode ma Allah daya haɗa ta da kishiya irin Zahra bata samu mai irin halinta, nan ya sanar da ita cewa zahra ce ta tirsasa shi ya dawo da ita badan haka ba da har yanzu tana cen, take taji wani nadama ya shige ta lallai ta gode ma Allah dabai haɗa ta da mai irin mugun halinta ba don ta Tabbatar inda itace a matsayin zahra,da wlh zahra tabar gidan kenan har a bada asaidai a bita da takardan ta, tayi nadama, ta tuba taubatan nasuha, washe gari kuwa har part ɗin zahra taje ta same ta nemi gafarar abinda ta mata, Allah sarki zahra dama bata riketa a raiba, nan dai tace ta yafe mata, tashi tayi ta rungume ta tana mata godiya, a haka Barr ya samesu, ba karamin dadi yaji a ranshi ba, take ya haɗa su ya nusu nasiha, tare da nuna musu irin tsantsar farin cikin da yake ciki a ranar saboda hada Kansu da sukayi, tun daga ranar kuwa suke zaune lafiya abin su, yara yanzu sun zama yan gata masu uwaye biyu, maryama suna kiranta da mummy zahra kuma suna kiranta da mum, dakinsu nanan a part din zahra data ware musu, lafiyayye Dan yama fi dakinsu na part din maryama haɗuwa, in sunga dama su kwana a gurin mummy insun ga dama su kwana gurin mum, maryama ce ta fara gane zahra nada ciki, aiko dai tayi farin ciki har zuciyar ta, take ta shiga tsokanarta tana kiranta da maman yan biyu, tun zahra na daukar abin da wasa har dai lamarin ya tabbata, saidai muyi fatan Allah ya raba lafiya.

A bangaren su Asmah kam yanzu sun wuje romeo da Juliet, soyayya suke zubawa kamar zasu cinye juna, da'ker da sidin goshi Asmah ta samu Aslam ya koma wajen aiki, shima da yarjejeniyar, yana aiki suna video call, haka dai tace mishi ta yarda, ta samu ta lallabashi ya tafi ranar farko daya fara zuwa, yana isa ko office bai shiga ba ya kirata ƙin ɗagawa tayi dan burinta a halin yanzu bai wuce ya maida hankali kan aikinshi ba, cikin abinda baifi awa daya ba ya mata missed call yafi hamshi ta share, aiko dai ko Rabin a waya bai kara ba saijin horn din motar shi tayi ya dawo, washe gari kuwa kin tafiya aikin yayi, ganin dai da gaske yakeyi, yasa itama ta ɓata rai ta daina kula shi ta fita sabgarshi, ta daina kwana tare dashi, kwana biyu suka kwashe a haka gaba dayan su sunji jiki, ba shiri yace mata yaji ya yarda zai koma aiki, amma sai inzasu dinga yin waya duk bayan awa ɗaya, ba yacce ta iya haka ta amice, amma da sharidin duk kira ɗaya bazai wuce 5 minutes ba, shima haka ya amince, da haka ta samu ya koma office.

Har zuwa wannan lokacin babu abinda ya shiga tsananin su, ta bangaren auratayya saidai zuwa yanzu an samu ci gaba sosai dan sukan sha romance dinsu na fitar hankali, saidai fa iyakar ta nan, ita kanta tana mamakin yadda akayi ya kasa nemanta har yanzu tun abin bai damunta har ya fara dan damunta, har take tunanin anya ma sonda yace yana mata da gaskene kuwa, dan indai akwai soyayyan dole zaiso su zama Abu guda ai, Allah sarki Asmah bata San Aslam yama fita bukatar hakan ba, saidai yana nan akan bakanshi, na cewa saita nemi hakan da kanta tukunna.

Gaba daya Aslam ya manta da wata zee a babin rayuwarsa, Asmah ce kawai a gabanshi a halin yanzu.

Yau gaba daya familin sun tashi da tsantsar farin cike, ba komai bane kuwa face haihuwan da akayi musu gagarumi, yayansu Rabi'a ce ta haihu maman hanifa, ta samu ɗa namiji wannan karon, da safiyar yau mami ta kira su dukkansu daya bayan daya tana gaya musu, duk wacce ta kira ,sai taji ta daka tsalle tana murna tare da tambayarta dama tana da ciki ne, tasan duk abinda sukema wannan tsallen murnan koba komai zasu zo gida zasu haɗu da juna, to ai dole, wata biyar fa ba kwana biyar ba, duk da suna waya da juna, da kuma iyayen nasu......

Oum Ummeetarh
07041130088

Share
And
Comment
Fisabilillah🙏.

💖DAMA TA BIYU💖

BY

~AYSHA NALADO~

FREE BOOK

{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu}

Page 119

Sudai shiru sukayi bakin su kanin kafar su, burin su bai wuce su gansu sun fita daga wannan kasurgumin kauyen ba.

Ko bi takan kunun da uwargidan mallam kamsusi ta ajiye musu basuyi ba, kimtsawa suka shiga yi duk in suka tuna uban tafiyar dake kansu sai gaban su ya yanke ya fadi, kanwar mamar su inna ta kalli beebaloo tace "wlh beebaloo baki ma kanki adalci ba, duk mazan duniya nan da tarin maneman ki,ki rasa Wanda zaki aura sai wannan mutumi, ki rasa inda zaki karkare rayuwar ki sai wannan kasurgumin kauyen, to nidai munyi sallama kenan dan keda kara ganina sai dai in kin kawo mana ziyara, amma nidai bazan sake zuwa wannan kauye ba, ni abin dayafi bani mamaki ma shin a ina kika hadu da wannan mutumin har kuma daidaita har ya kaiku da aure" taɓe baki kanwar ta tayi tace "hmmm inna ai Allah ne ya kama yaya beebaloo, ki duba kiga mazajen data aura a baya masu rufin asiri amma taki zama, ki duba irin zawarawan yaya beebaloo amma, duk ciki wai ba Wanda ya mata, ita sai kyakkyawa mai kudi dan babban gida, to ai ga kyakkyawa ta samu wanke hannu ka taɓa, karewar dan babban gida ma wannan shi karan kanshi ne babban." Ta karashe maganar tana kunshe dariyar da ke son kubce mata, inna ko duk da halin da take ciki na fargaban tafiyar dake gaban su saida ta dara tare da cewa "Allah ya kyauta Allah yasa wannan ya zama izna ga masu irin halin ki, kedai ga naki karshen kin gani."

karfe tara sun gama kimtsawa, beebaloo kam sai binsu da kallo take a ranta tanajin kamar ta bisu amma babu hali, dan tunda ta saka kafar ta cikin gidan ko marmarin fita kofar gida bata kara yi ba.

Sunyi sallama da sauran matan mallam kamsusi, sai godiya suke zuba musu kamar wadanda suka kawo wa wata gagarumar kauta ba kishiya ba.
Chapter 95 · 0% Book details