← Book details Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 61 OF 126

Sashe 61

Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Bayan sun gama cin abinci dan fira suka taba ya tashi ya wuce dakinshi dan yayi shirin bacci, itama haka tayi,ta wuce dakinta ta sheka wanka , tsayawa tayi gaban wardrobe ta zabi wani kayan bacci mai shegen kyau irin na turawa dan karami ta saka, wani kwalbar turare ta dauka,ɗan karami , daya daga cikin wanda Ummou Aslam na dama ta biyu fans ta aiko mata dashi, shu'ummin turarene duk yadda mace ta digashi ko kadan ne hmmmmm ba magana............

Masu comments inayinku iri sosai dinnan, kar ku damu inada dogon list na sunayenku.

Oum ummeetarh
07041130088

Share
And
Comment
Fisabillilah🙏.
💖DAMA TA BIYU💖

BY

~AYSHA NALADO~

FREE BOOK

DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARI NE MALLAKINA NE, BAN YARDA WANI KO WATA SU JUYAMIN LABARI TA KOWACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌

(In 👂👂👂 yiji, gangar jiki ya tsira 👌 a kiyaye pls)

(Nasadaukar da wannan book din ha duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu)

Tallah!💖 Tallah!! 💖Tallah!!!💖

Albishirinku manyan mata! ma'abota kwalliya da
_Rantsattsun lesussuka💃,
_Atamfofi manya da k'anana💃
_Galla gallan shaddodi manya da k'anana muna da su kowani iri💃
_Akwai kuma yadiddikan maza kamarsu koranza,plan yard dadai sauransu💃
_Munada mayafai, takalman maza da mata,sarqoqi, awarwaraye,da duk sauran nau'ikan kayan ado na maza da mata muna dasu 💃
Akanfaninmu na""R & U""Global Enterprise Dake Nan Garin Minna Niger State, saikunzo..........

Ga numbern mu kamar haka👇
08062160424
08066891424.....

Sayan day'a ko sari acikin farashi mai sauqi👌
Kubamu odern ku,danshine aikimmu akoda yaushe da yardar Allah........👌
Sai an gwada akansan na kwaraiiii💃💃💃.....

Page 98

Tana nan tsaye gaban mirror ya shigo dakin cikin shirin baccin shi, bakin shi dauke da sallama, amsawa tayi, ba tare ta kalle shi.

Direct inda take ya nufo a hankali ya mika hannunshi ya ya zàgayeta dashi ya daura kanshi a dokin wuyanta,lumshe ido yayi jin wani irin sihirtaccen kamshin daya doki hancinsa, a kasalance ya buɗe idanu, kallon juna suka shiga yi ta cikin mirror na wasu sakanni kafin, kuma a tare suka sakar ma juna murmushi.

A hakan da suke ya janyetà daga gaban mirror , suka koma bakin bed,zama yayi yana rumgume da ita ta gaban shi, hakan ya bata daman zama akan cinyar shi.

Hancinshi ya manna sosai a wuyanta yana sunsunan wannan daddaɗan turaren na jikinta yana lumshe idanu ji yakeyi kamar tuñda yake bai taba jin turaren daya kaishi daɗin kamshi a duniya ba.

A hankali ya miƙa hannunshi dake zagaye da ita, ya ɗage dan ficilin rigar bacci dake jikinta, ware tafikan hannunshi yayi akan shafeffen cikinta, yana shafawa a hankali.

Jin yau yakeyi na musamman a gareshi, ji yakeyi wani irin ƙaunarta da matsanancin sha'awarta na azalzalan shi, fiye da na kullum.

Lumshe ido zahra tayi lokacin da taji ya mika hannayenshi sama ya sauke su akan boobs dinta, ita kanta yau ta fahimci lamuran nasa na musamman ne.

Kasa daurewa yayi , daura bakinshi yayi a kunenta çikin shakakkiyar murya yace"babyn Adam" cikin kasallaliyar murya tace"na'am" yace "ya sunan wannan turaren naki ne" ita karan kanta bata San sunan shiba, kawai yadda ta ganshi kenan cikin farin karamin kwalba yar ɗuri, tsintar bakinta tayi da cewa "fatima zahra" dan ware idanun shi da suka rine zuwa launi ja yayi tare da cewa "Wow no wander, dole ya kasance da irin wannan sihirtaccen kamshi, tunda ya amsa suna Fatima zahra, kinsan wani Abu?" Kasa buɗe baki tayi ta bashi amsa jin irin yadda yake sarrafa albarkatun kirjin ta cikin wani irin salo mai birkita tunanin duk wata lafiyayyar mace, sai girgiza mai kawai tayi alamar A'ah bata sani ba,yace "tunda nake a duniya ban taba jin turaren daya kaishi daɗin kamshi ba, kema ko?" ya tamabayeta, wannan karon kam kasa bashi amsa zahra tayi, gaba ɗaya ta gama yin laushi, ta gama mika wuya, wani irin sako jikinta ke amsa na musamman, shima bai kara cewa komai ba da lamura sukayi nisa, dama duk sambatune, to yanzu lamarin ma ya wuce na sambatu.

Zuwa yanzu kam Abun yayi kamari daga bakin bed an koma tsakiyar bed, saida ya tabbatar gaba ɗaya ya gama fitar da ita daga duniyar mu zuwa duniyar sama'u, sannan ya dauki hanya, tsayawa kuma yayi kome ya tuna ohoo.

A wahalce ya bude rinannun idanunshi, ya kalli kyakkyawan fuskarta ta cikin hasken dim light da suka bari, idanunta a runtse suke, gashinta ta gaba daya ya hargitse ya rufe mata kusan rabin fuska, dakyar ya buɗe bakin shi yace"Fatima zahra" a hankali ta ware idanunta itama , saidai idanunsu na haduwa ta mayar da nata ta runtse da sauri, dan murmushi yayi ya kara cewa"kin amince min yau na mayar dake cikakkiyar mace, kin amince min yau dani dake mu zama Abu guda, kin amince min yau nazama ke, kizama ni?".

Saida gabanta ya fadi jin tambayar da yake mata, tana matukar tsoron wannan ranar, dan tasha karantawa a novels da yawa yadda, lamarin yake wasu har suma sukeyi wasu kuma su samu tear sai an musu ɗinki, wasu har gado ake basu a asibiti, gadai abubuwa da yawa dake biyo bayan lamarin, kamar tace A'a dukda ita karan kanta tana da muradi, sai kuma maganar ummi da sukayi rannan ya fado mata a rai.

Daurewa tayi, tayi ƙundinbala ta girgiza mai kai alamar e ta amince,wani kayataccen murmushi ya saki, kafin kuma a bayyane taji ya furta"Allahumma jannabnin shaidani, wa janabash shaidani ma razaktana,".

Barr yayi namijin kokari gurin bin Zahra a hankali, ba tare da garaje ba, har komai ya kammala wato ya maidata shi , shi kuma ya zama ita.

Zahra tayi matukar mamakin yanda nata lamarin yazo mata da matukar sauki haka, dukda taji zafi sosai matsyinta na virgin, amma yadda tasama kanta bargabar lamarin bata zaton zaizo mata da sauki haka ba.

Aiko bata tsaya ragonta ba, ita ta ma kanta komai da safe, ba tare da ta nemi taimakon kowa ba, har shi Barr, ba yadda baiyi ta bari ya mata wanka ba taki yarda.

(To Fatima zahra asha amarci lafiya Allah ya kawo kazantar daki😍)

~BATOOL~

Saida ya tsaya a R & U global enterprise, suka yi ma maah tsaraba sosai na manyan zannuwa, da lesuka, da turaruka masu kyau da tsada, suma kannen shi su Afifa batool bata barsu ba saida ta siya musu dankunnaye da abun wuya fashion masu kyau kala bibbiyu, suma ta hada musu da turaruka, sannan suka kama hanya.

A tafkeken coumpound d'in gidan yayi parking, fitowa sukayi a tare ya bude back sit ya kwaso manyan manyan ledodin siyayar da sukayi mai dauke da tambarin R & U global enterprise, gaba ya shiga tana biye da shi a baya, har suka isa kofar da zai sada ka da babban falon dake baban part d'in da yafi kowanne part girma a gidan.

Doorbell ya danna, jim kadan Afifa autar su ta buɗe kofar, ganin su yasa ta daka wata uwar sufa ta rungume batool, tare da cewa da karfi"Oyoyoooo anty batool Oyoyoooo my anty" hakan ya jawo hankalin Afnan da Afrah harma da maah da suke zaune a falo, suma a guje suka taso suka rungume ta, Dr bash kam girgiza kai yayi yana murmushi ya shige ciki ya barsu, muryar hajiyan da suke kira da maah suka tsinta daga ciki tana cewa "wai meye haka kukeyi saikun kayar da itane, harda ke Afrah gotai gotai dake ko" sai lokacin suka saketa tare da kamo hannun ta suka shigo da ita ciki.

Tun da ta saka kanta a fallon maah ta fara tafa hannu tana cewa "lale lale da ɗiyata batula maraba lale lale" a kunyace ta karasa gaban maah zata duka ta gaisheta, da sauri maah ta tarota ta jawota jikinta ta rungume ta daga zaune da take, kusa da ita ta mata mazauni, sannan ta kalli Afifa dake tsaye tana ta faman fara'a tace "auta akawo mata ruwa da abun tabawa" da sauri Afifa ta nufi haryar kitchen, dan kawo mata.

Dr bash yana zaune yana binsu da kallo ba Wanda yabi ta kanshi, duk sun rude takan batool kawai sukeyi, kamar ma sun manta tare suke da batool d'in, inda dane da bai auri batool ba, da duk rawan jikin nan shi zasu dinga wa.

Gyaran murya yayi duk suka juyo suna kallonshi yace"OK tunda ni ba mace bace shine ake nuna min wariyar launin fata a gidan nan ko, ba damuwa nasan zamana da kowa daga yau " duk dariya suka sa masa Afrah tace "sorry big bro wlh anty batool ne ta dauke mana hankali, kuma dama yanzu nakeson gaishe da kai, shine ka rigani magana" hararan wasa ya wurga mata, nan ta kwashe da dariya, sannan ta shiga gaishe shi, afnan ma gaishe shi tayi, ya amsa musu yana tambayarsu ya karatu, suka amsa da lafiya lau yayanmu.

Tashi yayi yaje gaban maah ya duƙa har kasa ya gaisheta, fuskarta a sake dauke da fara'a tana binshi da kallon so da kauna ta amsa mishi tare da tambayar lafiyar shi Dana batool, ya amsa da lafiya qalau, murmushin jin daɗin hakan ta saki, sannan takai hannu ta shafa mishi kanshi mai dauke da tarin kyakkyawan suma tace"Allah yai maka albarka bashir, Allah ya baka zuri'a ɗayyaba,".

Daidai nan Afifa ta fito daga kitchen hannunta dauke da tray shake da kayan ciye ciye da shaye shaye, ta dire a gaban batool, batool data kasa sakewa saboda kunyar maah dake wurin ta kalli Afifa tace "nagode sister, jazakillahu khair".

Zama su Afnan sukayi suka saka ta a tsakiya sai fira suke mata, maah dake gefe tana Kallon su tana murmushi, ganin zahra bata ci komai tace "daughter kici, wani Abu mana, Afnan ki zuba mata juice ki bata," da sauri batool tace "A'a Afnan barshi, maah nagode," maah tace "ki saki jikin ki fa daughter nan gidanku ne, kici abinda kike, oya Afifa zuba mata" batool ganin maah ta dage yasa ta hakura ta amsa saidai ta rike a hannu taki sha, ganin haka yasa maah ta saki wani kayataccen murmushi.
Chapter 61 · 0% Book details