Sashe 56
Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gidan Aslam haka rayuwar su yaci gaba da tafiya, kullum cikin bauta ma Asmah yakeyi da abinda ta saka shi da Wanda bata sakashi ba duk yi yakeyi, girki kafin ta tashi da safe ya gama breakfast, ya gyara gida ko ina yadau kanshi,ita dai baza tace mai sannu ba bare na gode, abinci kam zama takeyi taci hani'an idan ya girka, aikin gida kam duk ta sakar mai saidai tayi wanka taci kwalliya na fitar hankali ta kame a falo tana charting haka zaita kallonta yayta lasar laɓɓa, kamar tsohon maye, wanki da gugan kayanta duk ya dauke mata, batun zuwa office kuwa tuni ya jingine shi gefe sai assistant dinshi ne ke tafiyar da komai.
Asmah kam zuwa yanzu ta rage mugun tsanar da tamai ada yanzu dai kadaran kadahan takejin shi, itadai bayajin tsanar shi kamar da kuma bata jin sonshi a ranta ko kaɗan, tasan dai yana mugun bata tausayi,
Yau data kama ranar Sunday da misalin karfe takwas da rabi na safe taji ana mata knocking, ko bata tambaya ba tasan Aslam ne tashi tayi ta bude kofar ganin shi tayi dauke da tsintsiya da moppa a hannu, fuskar shi dauke da murmushi yace"gud morning mrs Asmah" amsawa tayi da "morning" yace "dama nace yau bari na share miki dakinki ne" har zatace ya barshi, don duk share sharen shi bai taba share mata dakinta ba, wata zuciyar tace ,barshi yayi Allah ne ya kama miki shi ya zama bawanki, cemai tayi"bismillah" tana kuacemai a hanya ya shiga, wow ya furta aranshi dakinta ya hadu sosai gashi a gyare tsab ba wani tarkace komai kimtse a muhallin sa, uwa uba kuma daddaɗan kamshi dake tashi mai saka nutsuwa dayake tashi hade da zabar Ac, kai gaskiya ita tanada tsabta ba kamar zee ba komai nata tsab stab, irin wannan wayewar yake nema yaje yayi lalube cikin duhu a baya.
Toilet dinta ya shiga ya fara wanke wa shima fess yake kara dai daurayewa yayi sama Sama, sannan ya dawo bedroom din nanma ya gyare shi tsab, ya ko iya gyara gado kamar wani klinan hotel, yana gamawa ya kunna heater ya hada mata ruwan wanka don yaga alamar batayi wanka ba ko.
A falo ya sameta yace "mrs Asmah nace na gama gyara dakin, saura wanka ko zaki tashi muje na taya ki na riga ma na sirka ruwan" harara ta watsamai, nan yayi fuskar tausayi tare da cewa "pls mrs Asmah wlh zan cuɗa ki da kyau" dariya ma ya bata, aiko ta shiga darawa, nan ya shagala yana kwallonta kamar yasa harshe ya lashe ta haka yakeji don so...........
Naceba wai baza ku tambayeni ina babyn Adam bane😤
Oum ummeetarh
07041130088
Share
And
Comment
Fisabillilah🙏
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARINE MALLAKINANE BAN YARDA WATA KO WANI SU JUYAMIN LABARI TA KO WACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌❌❌
(In👂👂👂yaji, gangar jiki ya tsira👌 a kiyaye pls)
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu}
Page 95
~BABYN ADAM~
Har Barr ya gama kwanaki bakwai daya kamata miji mai mata yayi a dakin amaryarsa budurwa,babu abinda ya shiga tsakanin su, na auratayya, saidai a yan kwanakin nan ba karamin sabo sukayi da juna ba, ta riga ta gama sakin jiki da shi duk dari darin da takeyi dashi da yanzu ta dena,yakan dan taba wasa da ita amma iyakanshi kenan bai taba nuna yana son wuce hakan ba, wannan yasa hankalinta ya kwanta, ta saki jiki da shi tunda abinda take ma tsoron, taga baida alamar yi, da amala dai ita nata miji ba dan air bane.😛
Har yayi kwana bakwai a dakinta bata fara girki da kanta ba daga gidan su ake aikowa, dan maryama cewa tayi baza tayi ba,
Duk motsinsu akan idon maryama, ta sanya musu ido sosai sometimes har labe take musu, ta fahimmci babu abinda ya shiga tsakanin su har yanzu, hakan kuwa ba karamin daɗi ya mata ba.
Tsakanin ta da Barr kuwa babu zaman lafiya kwata kwata, kullum cikin tayar mai da hankali take, gaba daya lamarin ta ya isheshi, kawai daurewa yakeyi yana kai zuciya nesa.
Yau ta kama zai koma ɗakin uwar gida ya gama kwanakin shi bakwai a dakin amarya, zahra harda kukanta shaɓe shaɓe haka yasa ta a jikin shi yana lallashi kamar wata jinjira, da'ker ya samu tayi shiru, tashi yayi ya shiga toilet ya haɗa mata ruwan wanke, yace tayi wanka ta same shi a dakin shi zai hada ta da maryama ya musu nasiha daga nan kuma yaji ra'ayin su,yanayin kwanakin da zasu raba.
Bayan fitar sa ta tashi ta shiga toilet d'in ta sheka wankanta da sabulanta masu kamshi na gyaran jiki, ta wanke dogon gashinta ta fito, zama tayi kan kujeran gaban mirror tayi shafe shafen ta, na mayukanta da turarukanta haɗaɗɗun gaske, tsantsararren makeup ta ɓata lokaci tayi a fuskarta, lokaci ɗaya ta dauki wani irin mugun kyau kamar wata balarabiya, dama ko batayi kwalliya ba mai kyauce balle kuma, lace ta ciro tsantsararre maroon color sai ratsin peach, ɗinki riga da skirt, dinki ya dan kamata haka yasa ya fito mata da shape sosai, dass ta fito kamar wata yar tsana, dauri ta kashe mai kyau na yayi, mayafinta karamin ta dauka peach ta ratayeshi a kafaɗa, turare ta dauka ta kara fesawa a kayanta, ta zura takalmanta mai tsini mahadin mayafinta ta dauki handset dinta ta nufi sashen Barr.
Bayan shigan shi daki wayar shi ya dauka ya danna ma Maryama kira, ringing wayar keyi tana kallo taki dagawa, har ya katse kara kira yayi saida ya kusa yankewa ta daga, ta kara a kunne batace ƙala ba, jin haka yasan baza tayi magana bane,don wani bin ji take da izza kamar wata jinin sarauta, da kausasheshen murya yace"na baki nan da 10 ki kimtsa ki sameni a part ɗina" kit ya kashe wayar sa, yanayin yadda taji muryarsa tasan ba wasa a maganar shi yasa ta tashi ba wani kimtswan da tayi kayan bacci ne a jikinta riga da wando da hulla haka ta taho abinta, Maryama ba kazama bace, amma tunda akayi mata kishiya ta dauki wahalallan kishi ta daura ma kanta shikenan komai nata yaja baya, har a gurin miji kimarta ya ragu, saboda wannan haukan da tajeyi da sunan kishi, saiyaji duk ta fice mai a rai, duk ta sukurkuta kanta a banza a wofi, tunda gashi dai duk tsiyar ta bai hana shi aure ba kuma bai hanashi kawo amaryar cikin gidanta ba,
( pls mata a kiyaye asan irin kishin da za'a dingayi ba kishin da zaki zubar ma kanki mutunci a gurin miji ba, duk sonki da miji idan ya tashi aure, kiyi hakuri ki danne kishinki, ba'ace karkiyi kishin mijinki ba amma kisan irin Wanda zakiyi, idan kika kama girmanki sai kiga duk wani abinda zai gudanar a lamarin aurenshi saida yardan ki, kece zaki zama bai bashi shawara komai zaiyi saiya gaya miki saiya nimi shawaran ki, tunda yaga kin bashi goyan baya, anan saiki yagi abinda kika yaga,amma in kika yi hauka zaki tashi a tutar babu ne, wasu ne can zasuci moriyar lamarin, idan kikayi kishin hauka kika tayar mai da hankali, kimar ki zaki zubar a idanun shi da idanun dangin shi,idan akwai wacce Baku shiri cikin yan uwanshi, ta samu hanyar da zata kuntata miki,saidai kiga ana abubuwa baki da labari, amma kin kama kanki, sai ki kange komai, komai sai anbi ta hannun ki, ya sakar miki ragamar komai, dan Allah a kiyaye kuma duk tsiyar da zakiyi bazai hanashi auren da yayi niyya ba, kijama kanki raini a gurin kishiya may be ma kin girmeta kin fita komai, Allah yasa mu dace).
Samun shi tayi zaune a falo yana amsa call a waya, guri ta samu a kujeran dake facing nashi ta zauna tana cika tana batsewa, ci gaba yayi da wayar shi ko kallonta shima baiyi ba, zaman ta kamar da minti biyar zahra tayi sallama cikin zazzakar muryarta mai dadin amo, daidai lokacin kuma Barr ya gama wayar da yakeyi, kamshinta ne fara musu sallama kafin a natse ta ɗago labulen falon ta shigo, da idanu suka bita yuuuu, kowa da irin kallon da yake mata, maryama ganin zahar da irin wankan data dauka ga wani zazzafan kamshi dake tashi a jikinta, saida gabanta ya yanke ya fadi rasss, take ta raina kanta a wurin ji tayi duk ta muzanta, kishi da ƙyashi da baƙin ciki suka mata kawanya a lokaci daya, take ta shiga aunawa zahra wani irin mugun kallo mai cike da tsantsar tsana.
Shiko Barr wani irin kallon so da tsananin ƙauna yake binta dashi, ji yake kamar ya tashi ya taro ta ya saka a kirjinshi, ko zaiji saukin zillon da zuciyar shi take mai akanta, yana tsananin son uwar gidan shi sosai amma sonda yakema zahra special ne.
Murmushi ya shiga jifanta dashi, hakan yasa itama ta shiga mayar mai da martani, matsawa yayi daga tsakiyar kujeran da yake zaune 2 sitter ya koma gefe, ganin haka zahra direct kusa dashi ta zauna a daya gefe.
Har ta zauna Maryama nabinta da wannan mugun kallon, cikin sakin fuska ta kalleta tace"yaya Maryama ina kwana" wani mugun tsaki taja kamar bakin ta zai tsinke, a madadin ta amsa gaisuwar ta sai cewa tayi"wlh kaji kunya Adam yanzu ɗan wannan abun ka iya cire kudinka ka bada sadaki da sunan kana so, kazo ka ajiye kana kwanciya da ita, yarinyace fa ƙarama Wanda na tabbata da kayi auren wuri da ka haifeta, wannan abin kunyar dame yayi kama, na tabbata wannan yarinyar idan ta girmi hanan(yar su ta fari)da nisa ta bata shekara biyar, yanzu kai baka jin kunyar ka tube zindir a gaban yar cikin ka, kalli kanka ka fa har furfura kake dashi" tsaki taja kafin taci gaba da cewa "suma iyayenta ne basu da hankali wannan ai child abuse ne".
Asmah kam zuwa yanzu ta rage mugun tsanar da tamai ada yanzu dai kadaran kadahan takejin shi, itadai bayajin tsanar shi kamar da kuma bata jin sonshi a ranta ko kaɗan, tasan dai yana mugun bata tausayi,
Yau data kama ranar Sunday da misalin karfe takwas da rabi na safe taji ana mata knocking, ko bata tambaya ba tasan Aslam ne tashi tayi ta bude kofar ganin shi tayi dauke da tsintsiya da moppa a hannu, fuskar shi dauke da murmushi yace"gud morning mrs Asmah" amsawa tayi da "morning" yace "dama nace yau bari na share miki dakinki ne" har zatace ya barshi, don duk share sharen shi bai taba share mata dakinta ba, wata zuciyar tace ,barshi yayi Allah ne ya kama miki shi ya zama bawanki, cemai tayi"bismillah" tana kuacemai a hanya ya shiga, wow ya furta aranshi dakinta ya hadu sosai gashi a gyare tsab ba wani tarkace komai kimtse a muhallin sa, uwa uba kuma daddaɗan kamshi dake tashi mai saka nutsuwa dayake tashi hade da zabar Ac, kai gaskiya ita tanada tsabta ba kamar zee ba komai nata tsab stab, irin wannan wayewar yake nema yaje yayi lalube cikin duhu a baya.
Toilet dinta ya shiga ya fara wanke wa shima fess yake kara dai daurayewa yayi sama Sama, sannan ya dawo bedroom din nanma ya gyare shi tsab, ya ko iya gyara gado kamar wani klinan hotel, yana gamawa ya kunna heater ya hada mata ruwan wanka don yaga alamar batayi wanka ba ko.
A falo ya sameta yace "mrs Asmah nace na gama gyara dakin, saura wanka ko zaki tashi muje na taya ki na riga ma na sirka ruwan" harara ta watsamai, nan yayi fuskar tausayi tare da cewa "pls mrs Asmah wlh zan cuɗa ki da kyau" dariya ma ya bata, aiko ta shiga darawa, nan ya shagala yana kwallonta kamar yasa harshe ya lashe ta haka yakeji don so...........
Naceba wai baza ku tambayeni ina babyn Adam bane😤
Oum ummeetarh
07041130088
Share
And
Comment
Fisabillilah🙏
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
DAMA TA BIYU💖 ƘIRƘIRARREN LABARINE MALLAKINANE BAN YARDA WATA KO WANI SU JUYAMIN LABARI TA KO WACCE SIGA BADA IZININA BA❌❌❌❌❌
(In👂👂👂yaji, gangar jiki ya tsira👌 a kiyaye pls)
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya Allah kajiqan iyayen mu}
Page 95
~BABYN ADAM~
Har Barr ya gama kwanaki bakwai daya kamata miji mai mata yayi a dakin amaryarsa budurwa,babu abinda ya shiga tsakanin su, na auratayya, saidai a yan kwanakin nan ba karamin sabo sukayi da juna ba, ta riga ta gama sakin jiki da shi duk dari darin da takeyi dashi da yanzu ta dena,yakan dan taba wasa da ita amma iyakanshi kenan bai taba nuna yana son wuce hakan ba, wannan yasa hankalinta ya kwanta, ta saki jiki da shi tunda abinda take ma tsoron, taga baida alamar yi, da amala dai ita nata miji ba dan air bane.😛
Har yayi kwana bakwai a dakinta bata fara girki da kanta ba daga gidan su ake aikowa, dan maryama cewa tayi baza tayi ba,
Duk motsinsu akan idon maryama, ta sanya musu ido sosai sometimes har labe take musu, ta fahimmci babu abinda ya shiga tsakanin su har yanzu, hakan kuwa ba karamin daɗi ya mata ba.
Tsakanin ta da Barr kuwa babu zaman lafiya kwata kwata, kullum cikin tayar mai da hankali take, gaba daya lamarin ta ya isheshi, kawai daurewa yakeyi yana kai zuciya nesa.
Yau ta kama zai koma ɗakin uwar gida ya gama kwanakin shi bakwai a dakin amarya, zahra harda kukanta shaɓe shaɓe haka yasa ta a jikin shi yana lallashi kamar wata jinjira, da'ker ya samu tayi shiru, tashi yayi ya shiga toilet ya haɗa mata ruwan wanke, yace tayi wanka ta same shi a dakin shi zai hada ta da maryama ya musu nasiha daga nan kuma yaji ra'ayin su,yanayin kwanakin da zasu raba.
Bayan fitar sa ta tashi ta shiga toilet d'in ta sheka wankanta da sabulanta masu kamshi na gyaran jiki, ta wanke dogon gashinta ta fito, zama tayi kan kujeran gaban mirror tayi shafe shafen ta, na mayukanta da turarukanta haɗaɗɗun gaske, tsantsararren makeup ta ɓata lokaci tayi a fuskarta, lokaci ɗaya ta dauki wani irin mugun kyau kamar wata balarabiya, dama ko batayi kwalliya ba mai kyauce balle kuma, lace ta ciro tsantsararre maroon color sai ratsin peach, ɗinki riga da skirt, dinki ya dan kamata haka yasa ya fito mata da shape sosai, dass ta fito kamar wata yar tsana, dauri ta kashe mai kyau na yayi, mayafinta karamin ta dauka peach ta ratayeshi a kafaɗa, turare ta dauka ta kara fesawa a kayanta, ta zura takalmanta mai tsini mahadin mayafinta ta dauki handset dinta ta nufi sashen Barr.
Bayan shigan shi daki wayar shi ya dauka ya danna ma Maryama kira, ringing wayar keyi tana kallo taki dagawa, har ya katse kara kira yayi saida ya kusa yankewa ta daga, ta kara a kunne batace ƙala ba, jin haka yasan baza tayi magana bane,don wani bin ji take da izza kamar wata jinin sarauta, da kausasheshen murya yace"na baki nan da 10 ki kimtsa ki sameni a part ɗina" kit ya kashe wayar sa, yanayin yadda taji muryarsa tasan ba wasa a maganar shi yasa ta tashi ba wani kimtswan da tayi kayan bacci ne a jikinta riga da wando da hulla haka ta taho abinta, Maryama ba kazama bace, amma tunda akayi mata kishiya ta dauki wahalallan kishi ta daura ma kanta shikenan komai nata yaja baya, har a gurin miji kimarta ya ragu, saboda wannan haukan da tajeyi da sunan kishi, saiyaji duk ta fice mai a rai, duk ta sukurkuta kanta a banza a wofi, tunda gashi dai duk tsiyar ta bai hana shi aure ba kuma bai hanashi kawo amaryar cikin gidanta ba,
( pls mata a kiyaye asan irin kishin da za'a dingayi ba kishin da zaki zubar ma kanki mutunci a gurin miji ba, duk sonki da miji idan ya tashi aure, kiyi hakuri ki danne kishinki, ba'ace karkiyi kishin mijinki ba amma kisan irin Wanda zakiyi, idan kika kama girmanki sai kiga duk wani abinda zai gudanar a lamarin aurenshi saida yardan ki, kece zaki zama bai bashi shawara komai zaiyi saiya gaya miki saiya nimi shawaran ki, tunda yaga kin bashi goyan baya, anan saiki yagi abinda kika yaga,amma in kika yi hauka zaki tashi a tutar babu ne, wasu ne can zasuci moriyar lamarin, idan kikayi kishin hauka kika tayar mai da hankali, kimar ki zaki zubar a idanun shi da idanun dangin shi,idan akwai wacce Baku shiri cikin yan uwanshi, ta samu hanyar da zata kuntata miki,saidai kiga ana abubuwa baki da labari, amma kin kama kanki, sai ki kange komai, komai sai anbi ta hannun ki, ya sakar miki ragamar komai, dan Allah a kiyaye kuma duk tsiyar da zakiyi bazai hanashi auren da yayi niyya ba, kijama kanki raini a gurin kishiya may be ma kin girmeta kin fita komai, Allah yasa mu dace).
Samun shi tayi zaune a falo yana amsa call a waya, guri ta samu a kujeran dake facing nashi ta zauna tana cika tana batsewa, ci gaba yayi da wayar shi ko kallonta shima baiyi ba, zaman ta kamar da minti biyar zahra tayi sallama cikin zazzakar muryarta mai dadin amo, daidai lokacin kuma Barr ya gama wayar da yakeyi, kamshinta ne fara musu sallama kafin a natse ta ɗago labulen falon ta shigo, da idanu suka bita yuuuu, kowa da irin kallon da yake mata, maryama ganin zahar da irin wankan data dauka ga wani zazzafan kamshi dake tashi a jikinta, saida gabanta ya yanke ya fadi rasss, take ta raina kanta a wurin ji tayi duk ta muzanta, kishi da ƙyashi da baƙin ciki suka mata kawanya a lokaci daya, take ta shiga aunawa zahra wani irin mugun kallo mai cike da tsantsar tsana.
Shiko Barr wani irin kallon so da tsananin ƙauna yake binta dashi, ji yake kamar ya tashi ya taro ta ya saka a kirjinshi, ko zaiji saukin zillon da zuciyar shi take mai akanta, yana tsananin son uwar gidan shi sosai amma sonda yakema zahra special ne.
Murmushi ya shiga jifanta dashi, hakan yasa itama ta shiga mayar mai da martani, matsawa yayi daga tsakiyar kujeran da yake zaune 2 sitter ya koma gefe, ganin haka zahra direct kusa dashi ta zauna a daya gefe.
Har ta zauna Maryama nabinta da wannan mugun kallon, cikin sakin fuska ta kalleta tace"yaya Maryama ina kwana" wani mugun tsaki taja kamar bakin ta zai tsinke, a madadin ta amsa gaisuwar ta sai cewa tayi"wlh kaji kunya Adam yanzu ɗan wannan abun ka iya cire kudinka ka bada sadaki da sunan kana so, kazo ka ajiye kana kwanciya da ita, yarinyace fa ƙarama Wanda na tabbata da kayi auren wuri da ka haifeta, wannan abin kunyar dame yayi kama, na tabbata wannan yarinyar idan ta girmi hanan(yar su ta fari)da nisa ta bata shekara biyar, yanzu kai baka jin kunyar ka tube zindir a gaban yar cikin ka, kalli kanka ka fa har furfura kake dashi" tsaki taja kafin taci gaba da cewa "suma iyayenta ne basu da hankali wannan ai child abuse ne".