Sashe 32
Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tashi yayi , ya shiga toilet yayi alwala ya tafi masallaci, yana dawowa ya biya dakin zee tana nan kwance kamar gawar sababi, har aka gama kiraye kirayen sallah, aka tada sallah aka idar ko motsi batayi ba, tashinta yayi, ta hanyar zuba mata duka a cinya, a firgice ta farka bako addu'a,
Tsaki yaja ya fice daga dakin, cikin sauri ta duro daga kan gadon tunawa da tayi, yau beebalo zata rakata asibiti , a zubar da cikin nan tun kafin ya bayyana, ta yadda kwallon mangoro ta huta da ƙuda, dan itama akan batun cikin nan jiya daƙer tayi bacci , saida ta kira iyayen ta ta gaya musu, dukkansu cewa sukayi taje ta zubar , wai bata isa haihuwa ba,
.yana shiga dakin shi ya zauna yayi azkar , da karatun alkur'ani mai tsarki a karshe ya dukufa yana ta kai kukan shi gurin mahakiccin shi, cikin kaskantar da kai da mika wuya,
Kafin gari yayi haske kuwa , ya samu sauki sosai a cikin ranshi, damuwa da baqin cikin da yake ciki ya ragu fiye da kaso hamsin cikin dari, har yana jin yau zai shiga office Wanda rabonshi da office din har ya manta, sai assistant shi ke tafiyar da komai na kamfanin,
Wanka yayi ya shirya cikin shirin fita office, yana gamawa kuwa ya leka ɗakin zee ya sallameta, dama dai ba batun karyawa a gida,
Shiga motar shi yayi ya nufi gurin da yake zuwa yayi parking kullum dan ganin Asmah ,yau kam taci sa'a ya samu ganin ta, sabanin wataran da ko yazo bazai ganta ba, saboda wani bin lecture rana take dashi ,
Suna wucewa shima ya dauki hanyar zuwa office, message ne ya shigo wayar shi , sharewa yayi dan yasan kila , kamfanin layi ne,
Saida ya isa kamfani ,ya samu shiga office ya zauna tukun , sannan ya dauki wayar shi da niyar kiran P A dinshi ya tuna da message d'in, budewa yayi ya fara karantawa tun kan yakai karshe yaja wani mugun tsaki , indai irin wadanan sakonnin ne ya saba cin karo da su jifa jifa,
Sakone na kalaman soyayya zafafan daga beebalo, delete din sakon yayi ya ci gaba da duba aiyukan dake gabanshi,
Can kuma wani massage din ya sake shigowa, kamar bazai duba ba sai kuma zuciyar shi ya dinga azalzalan shi akan ya bude sakon ya gani, budewa yayi ya fara karntawa, tun kan ya ƙarasa karanta, sakon yaji kanshi na juya mishi, a fili ya furta"whattttt! Impossible, cikin nawa zata zubar tana hauka ne hala," zama yayi daɓass akan kujeran shi mai jujjuyawa,
Can kuma ya zabura ya mike , yasan zee zata aika, yanzu mai zaiyi dan ya dakatar da ita,
Number da aka turo mai sakon ya shiga kira, acan bangaren beebalo ta daga kiran cikin kisisina, tace "amincin Allah ya tabbata a gareka ya kai Aslam tauraron zuciyata," ckin tsawa ya katse ta da cewa"wacece ke me kuma kika sani game da matata," murmushin barikanci tayi"matar ka ko maƙiyarka, lallai aslam har zainab kake kira da mata, to bari na gaya maka zaune kake da kasungumar makiyarka baka sani ba," katseta yayi da cewa "ba abinda na tambayeki kenan ba, kin tabbatar abida kika fad'a min gaskiya ne , don idan nayi bincike na gane wani abu daban rashin ki ya bushe, wlh matuqar kina cikin duniyar nan baki mutu ba ko ina kika shiga sai na lalubo ki," ya karashe maganar cikin wani irin razanannan tsawa tare da dukan table din gabanshi, saida takardun dake kai suka warwatse,
Cikin beebalo ne ya bada wani sauti ,kulululululululululu, alamar zawo na haduwa , dan ba karamin firgitata kalaman aslam da tsawan daya da ka mata yayi ba,
Amma kasancewar ta gogaggan yar duniya yasa ta dake ta fashe da kukan munafurci ,cikin kuka tace "wlh Aslam ni masoyiyarka ce, hakan ne ma yasa na kiraka don bazan so wani abin cutuwa ya sameka ba, ni ƙawar zainab ce mun hadu kimanin wata daya kenan da suka wuce, kuma kullum takan gayamin ita bata kaunar ka ta tsaneka. Dana sanin aurenka takeyi, ita wlh da zata samu dama kasheka zatayi har lahira, ni kuma haka kawai sai Allah ya daura min so da ksunarka na gaskiya , ni nake tausanta na hanata aiwatar da mugun nufinta akan ka, tasha kawo maka farmaki ina kare maka, kwatsam jiya ta same ni da batun cikin ka daya bayyana a jikinta, amma tace ita zubarwa zatayi, baza ta iya hada zuri'a da kaiba,na bata hakuri na bata hakuri taqi hakura, a haka muka rabu, shine d'azu da safe tazo gidan mu wai nazo na rakata ta zubar da ciki , nace baza ni, ba itama na shiga mata nasihar kar tayi haka , amma ta fice ko waiwayena batayiba wai innaga ta fasa zubar da cikin nan yau ranta ne ya fita daga gangar jikinta, tana fita nata kiran ta taqi dagawa, shine na tuna da wani number data taba bani wai number Kane , shine na kiraka ko kai zaka iya dakatar da ita, amma na rantse maka bayan wannan bayanin da na maka bansan komai ba a game da wannan magana," ta karashe maganar cikin fashewa da matsanancin kuka, kamar da gaske
Aslam da gaba daya jiri ke diban shi ya koma da baya ya zauna akan kujeran shi daya tashi, daɓasss, cikin matuqar sanyin jiki yace, "wani asbiti tace miki zata je " cikin sheshsheka tace"bansan wani asibiti zataje ba bata gaya min "
Godiya yama beebalo kafin ya katse kiran , maganar beebalo yayi tasiri sosai a zuciyar shi, kusan minti ashirin ya kwashe zaune a gurin yama rasa ta ina zai fara,
Can kuma kamar an tsikare shi ya dauki wayar shi da sauri ya shiga kiran lambar zee.
Beebalo na gama waya da Aslam ta kwashe da wani irin maketacin dariya, saida tayi mai isarta, sanan ta saisaita kanta , komawa tayi cikin wani karamin asibitin kudi , da sukeje don zubar da cikin,zee nanan zaune a inda beebalo ta barta , tace ta jirata,
Dawowa beebalo tayi gurin zee tace "ƙawa dan Allah kiyi hakuri nadan tsaya gaisawa da wani yayana ne" zee tayi murmushin yaƙe tace "ba komai ƙawa"
Duk jikinta a mace yake ji takeyi kamar ta fasa zubar da cikin nan dan haka kurum takejin gabanta na faduwa, kallon beebalo tayi tace,"kawa ji nakeyi kamar na fasa zubar da cikin nan wlh, haka kawai nakeji a jikina akwai matsala game da wnnan lamari, gara kawai na barshi ,idan ckin ya isa haihuwa sai amin aiki kawai a ciro shi ba sai na haihu da kaina ba, kinga sai a dinga ba babin madaran yara a samo mishi nanny ba shikenan ba"
Beebalo tace "tab wlh karki kuskura kiyi wannan gangancin na barin cikin nan idan har kina so kici
gaba da zama da Aslam, dan wlh yana gane akwai cikin nan ya dinga wulakanta ki kenan, karshe ma ya sake ki a banza akan wani dan qaramin ciki, bakisan maza yanzu basa son mace da anyi aure tayi ciki ba, kuma kinaga zaki iya rainon ciki akwai wahala fa mata da yawa suna mutuwa ta wannan hanyar, kawai tunda mun riga munzo ki zubar da wannan kawai in yaso idan kin samu wani cikin sai ki barshi ,"
Zee dai duk da hankalinta bai kwanta ba haka ta yarda da shawaran beebalo,
Dr din da suke jira ne ya ƙaraso, sun riga sun gama magana da beebalo a waya, ta gayamai harda irin alluran da takeson ama zee,
Binshi office sukayi, beebalo ta kara mai bayani sannan ta fice daga office din ta barshi da zee , dake kawance akan gadon dakin donya gwada ta yasan irin alluran da zai mata,
Tana fita wayar zee dake hannun ya fara qara dubawa tayi taga , lambar Aslam ne murmushi mugunta tayi tare da qin daga kiran
Kira yake yana sake kira a haukace, bata daga ba daga baya ya tura mata da message na karta kuskura tayi gangancin zubar mai da ciki, beebalo na karanta message din tayi delete dinshi a wayar ta kashe wayar gaba daya,
Sake kiranta yayi, yaji wayar a karshe take hankalin shi ya kara tashi, miqewa yayi da wani irin sauri ya fita daga office ya shiga motar shi ya figeta da wani irin mahaukacin gudu,
Dr na gama gwada zee ya kalleta da wani irin tausayawa, alluran da beebalo ta biya shi makudan kudi danya ma zee sun mata karfi da yawa zasu iya hallakata har lahira,
Har ya dakko zai mata yaji tausayin ta ya canza alluran ya mata Wanda bai kaishi karfi ba,
Kiran beebalo yayi yace tazo angama, su wuce gida maza maza, zee kam tuni ta fara ganin jiri jiri, kafin su qarasa mota har ta hada wani uban zuba ,beebalo sai zuba mata sannu takeyi cikin matuqar tausayawa,
Beebalo ne taja motar kasancewar zee bata cikin haiyacin ta, har gidan ta kaita mai gadi wa wangale mata get , tana parking ta tallabo zee har cikin falon kwantar da ita tayi akan dogon kujera, kafin ta juya ta fice daga falon da sauri,
Kaman kar beebalo tabar falon wani irin matsanancin ciwon Mara ya tasowa zee, birgima takeyi tana malelekuwa a cikin falon, tafi minti takatin a haka kafin jini ya balle mata da mugun karfi harda guda guda, kan kace kobo falon yayi faca faca da jini kamar an yanka ƙaramin dabba ,
Aslam saida ya je asibiti ashirin yana Neman zee dana kudi Dana gwamnati amma ko mai kama da ita bai gani ba, gashi wayar ta a kashe , duk da haka bai daina karanta ba,
Sai yamma ya dowa gida a galabaice,tunda ya danno kan motarshi ya hango motar zee fake a parking lot,
Ko gama parking din kirki baiyi, ya balle murfin motar ya fito da gudun tsiya , burin shi yaga bai wuce ace yana shiga ya tarar duk karya ne abinda beebalo ta fad'a mai ba,
saidai kash yana shiga falon ya hangi zee kwance a kasa cikin jini face face, a fili ya furta"ya furta innalillahi wainnailaihi Rajiun, shikenan ta faru ta kara, "
Tsaki yaja ya fice daga dakin, cikin sauri ta duro daga kan gadon tunawa da tayi, yau beebalo zata rakata asibiti , a zubar da cikin nan tun kafin ya bayyana, ta yadda kwallon mangoro ta huta da ƙuda, dan itama akan batun cikin nan jiya daƙer tayi bacci , saida ta kira iyayen ta ta gaya musu, dukkansu cewa sukayi taje ta zubar , wai bata isa haihuwa ba,
.yana shiga dakin shi ya zauna yayi azkar , da karatun alkur'ani mai tsarki a karshe ya dukufa yana ta kai kukan shi gurin mahakiccin shi, cikin kaskantar da kai da mika wuya,
Kafin gari yayi haske kuwa , ya samu sauki sosai a cikin ranshi, damuwa da baqin cikin da yake ciki ya ragu fiye da kaso hamsin cikin dari, har yana jin yau zai shiga office Wanda rabonshi da office din har ya manta, sai assistant shi ke tafiyar da komai na kamfanin,
Wanka yayi ya shirya cikin shirin fita office, yana gamawa kuwa ya leka ɗakin zee ya sallameta, dama dai ba batun karyawa a gida,
Shiga motar shi yayi ya nufi gurin da yake zuwa yayi parking kullum dan ganin Asmah ,yau kam taci sa'a ya samu ganin ta, sabanin wataran da ko yazo bazai ganta ba, saboda wani bin lecture rana take dashi ,
Suna wucewa shima ya dauki hanyar zuwa office, message ne ya shigo wayar shi , sharewa yayi dan yasan kila , kamfanin layi ne,
Saida ya isa kamfani ,ya samu shiga office ya zauna tukun , sannan ya dauki wayar shi da niyar kiran P A dinshi ya tuna da message d'in, budewa yayi ya fara karantawa tun kan yakai karshe yaja wani mugun tsaki , indai irin wadanan sakonnin ne ya saba cin karo da su jifa jifa,
Sakone na kalaman soyayya zafafan daga beebalo, delete din sakon yayi ya ci gaba da duba aiyukan dake gabanshi,
Can kuma wani massage din ya sake shigowa, kamar bazai duba ba sai kuma zuciyar shi ya dinga azalzalan shi akan ya bude sakon ya gani, budewa yayi ya fara karntawa, tun kan ya ƙarasa karanta, sakon yaji kanshi na juya mishi, a fili ya furta"whattttt! Impossible, cikin nawa zata zubar tana hauka ne hala," zama yayi daɓass akan kujeran shi mai jujjuyawa,
Can kuma ya zabura ya mike , yasan zee zata aika, yanzu mai zaiyi dan ya dakatar da ita,
Number da aka turo mai sakon ya shiga kira, acan bangaren beebalo ta daga kiran cikin kisisina, tace "amincin Allah ya tabbata a gareka ya kai Aslam tauraron zuciyata," ckin tsawa ya katse ta da cewa"wacece ke me kuma kika sani game da matata," murmushin barikanci tayi"matar ka ko maƙiyarka, lallai aslam har zainab kake kira da mata, to bari na gaya maka zaune kake da kasungumar makiyarka baka sani ba," katseta yayi da cewa "ba abinda na tambayeki kenan ba, kin tabbatar abida kika fad'a min gaskiya ne , don idan nayi bincike na gane wani abu daban rashin ki ya bushe, wlh matuqar kina cikin duniyar nan baki mutu ba ko ina kika shiga sai na lalubo ki," ya karashe maganar cikin wani irin razanannan tsawa tare da dukan table din gabanshi, saida takardun dake kai suka warwatse,
Cikin beebalo ne ya bada wani sauti ,kulululululululululu, alamar zawo na haduwa , dan ba karamin firgitata kalaman aslam da tsawan daya da ka mata yayi ba,
Amma kasancewar ta gogaggan yar duniya yasa ta dake ta fashe da kukan munafurci ,cikin kuka tace "wlh Aslam ni masoyiyarka ce, hakan ne ma yasa na kiraka don bazan so wani abin cutuwa ya sameka ba, ni ƙawar zainab ce mun hadu kimanin wata daya kenan da suka wuce, kuma kullum takan gayamin ita bata kaunar ka ta tsaneka. Dana sanin aurenka takeyi, ita wlh da zata samu dama kasheka zatayi har lahira, ni kuma haka kawai sai Allah ya daura min so da ksunarka na gaskiya , ni nake tausanta na hanata aiwatar da mugun nufinta akan ka, tasha kawo maka farmaki ina kare maka, kwatsam jiya ta same ni da batun cikin ka daya bayyana a jikinta, amma tace ita zubarwa zatayi, baza ta iya hada zuri'a da kaiba,na bata hakuri na bata hakuri taqi hakura, a haka muka rabu, shine d'azu da safe tazo gidan mu wai nazo na rakata ta zubar da ciki , nace baza ni, ba itama na shiga mata nasihar kar tayi haka , amma ta fice ko waiwayena batayiba wai innaga ta fasa zubar da cikin nan yau ranta ne ya fita daga gangar jikinta, tana fita nata kiran ta taqi dagawa, shine na tuna da wani number data taba bani wai number Kane , shine na kiraka ko kai zaka iya dakatar da ita, amma na rantse maka bayan wannan bayanin da na maka bansan komai ba a game da wannan magana," ta karashe maganar cikin fashewa da matsanancin kuka, kamar da gaske
Aslam da gaba daya jiri ke diban shi ya koma da baya ya zauna akan kujeran shi daya tashi, daɓasss, cikin matuqar sanyin jiki yace, "wani asbiti tace miki zata je " cikin sheshsheka tace"bansan wani asibiti zataje ba bata gaya min "
Godiya yama beebalo kafin ya katse kiran , maganar beebalo yayi tasiri sosai a zuciyar shi, kusan minti ashirin ya kwashe zaune a gurin yama rasa ta ina zai fara,
Can kuma kamar an tsikare shi ya dauki wayar shi da sauri ya shiga kiran lambar zee.
Beebalo na gama waya da Aslam ta kwashe da wani irin maketacin dariya, saida tayi mai isarta, sanan ta saisaita kanta , komawa tayi cikin wani karamin asibitin kudi , da sukeje don zubar da cikin,zee nanan zaune a inda beebalo ta barta , tace ta jirata,
Dawowa beebalo tayi gurin zee tace "ƙawa dan Allah kiyi hakuri nadan tsaya gaisawa da wani yayana ne" zee tayi murmushin yaƙe tace "ba komai ƙawa"
Duk jikinta a mace yake ji takeyi kamar ta fasa zubar da cikin nan dan haka kurum takejin gabanta na faduwa, kallon beebalo tayi tace,"kawa ji nakeyi kamar na fasa zubar da cikin nan wlh, haka kawai nakeji a jikina akwai matsala game da wnnan lamari, gara kawai na barshi ,idan ckin ya isa haihuwa sai amin aiki kawai a ciro shi ba sai na haihu da kaina ba, kinga sai a dinga ba babin madaran yara a samo mishi nanny ba shikenan ba"
Beebalo tace "tab wlh karki kuskura kiyi wannan gangancin na barin cikin nan idan har kina so kici
gaba da zama da Aslam, dan wlh yana gane akwai cikin nan ya dinga wulakanta ki kenan, karshe ma ya sake ki a banza akan wani dan qaramin ciki, bakisan maza yanzu basa son mace da anyi aure tayi ciki ba, kuma kinaga zaki iya rainon ciki akwai wahala fa mata da yawa suna mutuwa ta wannan hanyar, kawai tunda mun riga munzo ki zubar da wannan kawai in yaso idan kin samu wani cikin sai ki barshi ,"
Zee dai duk da hankalinta bai kwanta ba haka ta yarda da shawaran beebalo,
Dr din da suke jira ne ya ƙaraso, sun riga sun gama magana da beebalo a waya, ta gayamai harda irin alluran da takeson ama zee,
Binshi office sukayi, beebalo ta kara mai bayani sannan ta fice daga office din ta barshi da zee , dake kawance akan gadon dakin donya gwada ta yasan irin alluran da zai mata,
Tana fita wayar zee dake hannun ya fara qara dubawa tayi taga , lambar Aslam ne murmushi mugunta tayi tare da qin daga kiran
Kira yake yana sake kira a haukace, bata daga ba daga baya ya tura mata da message na karta kuskura tayi gangancin zubar mai da ciki, beebalo na karanta message din tayi delete dinshi a wayar ta kashe wayar gaba daya,
Sake kiranta yayi, yaji wayar a karshe take hankalin shi ya kara tashi, miqewa yayi da wani irin sauri ya fita daga office ya shiga motar shi ya figeta da wani irin mahaukacin gudu,
Dr na gama gwada zee ya kalleta da wani irin tausayawa, alluran da beebalo ta biya shi makudan kudi danya ma zee sun mata karfi da yawa zasu iya hallakata har lahira,
Har ya dakko zai mata yaji tausayin ta ya canza alluran ya mata Wanda bai kaishi karfi ba,
Kiran beebalo yayi yace tazo angama, su wuce gida maza maza, zee kam tuni ta fara ganin jiri jiri, kafin su qarasa mota har ta hada wani uban zuba ,beebalo sai zuba mata sannu takeyi cikin matuqar tausayawa,
Beebalo ne taja motar kasancewar zee bata cikin haiyacin ta, har gidan ta kaita mai gadi wa wangale mata get , tana parking ta tallabo zee har cikin falon kwantar da ita tayi akan dogon kujera, kafin ta juya ta fice daga falon da sauri,
Kaman kar beebalo tabar falon wani irin matsanancin ciwon Mara ya tasowa zee, birgima takeyi tana malelekuwa a cikin falon, tafi minti takatin a haka kafin jini ya balle mata da mugun karfi harda guda guda, kan kace kobo falon yayi faca faca da jini kamar an yanka ƙaramin dabba ,
Aslam saida ya je asibiti ashirin yana Neman zee dana kudi Dana gwamnati amma ko mai kama da ita bai gani ba, gashi wayar ta a kashe , duk da haka bai daina karanta ba,
Sai yamma ya dowa gida a galabaice,tunda ya danno kan motarshi ya hango motar zee fake a parking lot,
Ko gama parking din kirki baiyi, ya balle murfin motar ya fito da gudun tsiya , burin shi yaga bai wuce ace yana shiga ya tarar duk karya ne abinda beebalo ta fad'a mai ba,
saidai kash yana shiga falon ya hangi zee kwance a kasa cikin jini face face, a fili ya furta"ya furta innalillahi wainnailaihi Rajiun, shikenan ta faru ta kara, "