Sashe 41
Da Izzata Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Daga bayan su suka tsinci muryar Alhaji baba , yana cewa"ban amince ba, na riga na faɗa ko bayan raina ban amince Aslam ya auri Asma'u ba dan haka ina nan akan bakata , idan kai ka hakura ka janye ka bar masa ni ban janye ba,maganar yafiya kuma daya nema zan yafe masa amma da sharaɗi zan kuma yi masa zabi a karo na biyu, idan har ka amince da zabi na na yafe maka Aslam, Allah ya yafe mana baki daya, kuma kowa ma a nan ina son ya dubi girman Allan daya hada mu dashi ya yafe masa, amma maganar auren Asma'u kam babu shi, na fada na kara, zabina na biyu kuma za'a hada bikin tare da nasu kamalu ne, iya alfarman da zan iya maka kenan" Sakai yayi ya fice daga dakin abin shi ko jiran Alhaji Mallam da suka zo tare baiyi ba,.
Shiru falon ya dauka kowa da irin tunanin da yake sakawa a zuciyar shi, Alhaji Mallam ne yayi gyaran murya, dukkansu suka maida hankalin su a kanshi , Cikin muryar shi ta dattijan da tsantsar ilimin addini ya ratsasu ya soma cewa"a gaskiya Aslam ka aikata babban kuskure a baya amma alhamdulillahi tunda har ka gane gaskiya kuma ka nemi yafiyar wadanda ka bata wa, saidai abinda zan fada maka shine kayi hakuri da Asma'u, tunda kaga haka watakila ita ba alkhairi bace a gare ka , maganar zabin da Alhaji baba yace zai maka ina mai baka shawara da ka karba da hannu bibbiyu , na tabbata zata zame maka farin ciki, kuma ta sakaka ka manta da cewa ka taba son Asmah a rayuwar ka,"
Aslam ya sauke ajiyar zuciya cikin sanyin murya yace"Alhaji a halin yanzu na Riga na cire rai da rayuwata, tunda har na rasa Asmah, domin kuwa itace rayuwata, amma duk da haka nayi farin ciki da zabin ku kuma na karba da hannu bibbiyu , kuma insha Allah zakuyi alfahari da ni a karo na biyu, nasan baza ku taba zabar min abinda zai cutar dani ba wancen karan ma , kuruciya da wauta ne ya sakani aikata aikin danasani,"
Alhaji baba dake laɓe a bakin kofa yana sauraran komai sauke ajiyar zuciya yayi sanna yasa kai ya wuce abinshi bai jira Mallam ba don fushi yake yi da shi ko mai ya hada su ohoo nan gaba zamuji.
~MALAYSIA~
Yau kimanin sati uku kenan da barowarta 9ja , tunda ta saka kafarta a cikin gidan bata kara lafiya ba, hoton yanayi da ta baro Aslam a ciki a police station ya ki fita daga kwakwalwarta, kullum Daren duniya kuka take kwana , ji takeyi da da hali da ta koma 9ja gurin mjinta ta rungume abinta da hannu bibbiyu, amma ina lokaci ya kure mata domin iyayenta babu abinda suka tsana sama da Aslam a duniya wayar ta ma tuni Dad ya amsa ya canja mata wani da wasu layukan, yanzu bata da buri daya wuce ta samu lambar beebalo ta kirata tasan beebalo mai kaunarta Ce zata iya mata duk abinda ta saka ta, mom ne ta turo kafar dakinta ta shigo hannun ta dauke da plat shake da kayan marmari yankakku, masu sanyi, zama tayi a bakin gadon da take ta mika hannun ta taba wuyanta, jikin na nan da zafin kau kamar ko yaushe , tunda ta dawo Malaysia bata kara lafiya ba ga kukan da ta aura tanayi kullum dare ,ga kuma rashin cin abinci,ko ruwa bata iya sha saita amayar fruit kadai take iya CI ta zauna lafiya shima idan taci da yawa sai sun dawo, ga kuma wani tsinkakken miyau dake addabarta, wannan lamari ya matukar daga hankalin iyayen zee, sunje asibiti ance fever ne,.
Yau dai sukayi da wani babban likitan mata Dr habu sarki, kan cewa zaizo har gida ya dubata, kwararren likita ne da samun ganin shi ko Malaysia sai wane da wane, yasan aikinsa sosai ba karamin wuya Dad yasha ba kafin ya samu Dr habu sarki ya amsa gayyatar shi, saida ya zube makudan kudade bana wasa ba,.
Tasar da ita mom tayi tana bata fruit din abaki tana sha kadan kadan , suna cikin haka dad ya shigo dakin , ya sanar dasu isowar Dr, mom tace saidai ya shigo nan ya dubata kaga jikin ba karfi baza ta iya sauka kasa ba ,
Haka ko akayi Dr ya shiga har dakin zee, babu kayan kirki a jikinta kayan bacci ne mai shara shara kanta babu dankwali amma iyayen ta ko a jikin su, dauke kai Dr yayi daga kallonta domin shidai musulmine dan 9ja kuma ba fasiki bane hasalima tare yake da iyalinsa suke zaune anan Malaysia,
Tambayoyi ya shiga mata akan abinda ke damunta tana bashi amsa, yana rubutawa,akan yanayin da take ji ajikinta, bayan ya gama ya bukaci miyanta da fitsari ba bata lokaci aka bashi na'urorin daya zo dashi ya dauka ya shiga gwaje gwaje akan miyau da fistarinta , yana gamawa bayan ya samu amsar abinda yake nema ya kalli Dad yace"Alhaji abdussalam, daughter ka tana dauke da juna biyu ne karami, Wanda ke bata wahala ,duk wadannan abubuwan da takeji a jikinta saboda ciki ne laulayi takeyi"
Cikin tsnananin tashin hankali da kiɗami dad da mom har suna hada baki wurin cewa ciki kuma Dr, Dr yace" yes tana da ciki tabbas" mom tace"Dr wani irin ciki kuma kadai sake gwadawa dakyau"nanta labarta mishi batun zubar da cikin da zee tayi, Dr yace "ana samun haka Ai alluran da wancen likitan ya mata bamai karfi bane kuma ba'ayi wankin ciki ba , to cikin na nan baiyi komai ba saidai yadan koma baya ,ma'ana ya zuba, watannin shi sun ragu,".
Dad da mamaki ya gama kashe shi yace to Dr yanzu abinda nake so dakai"allura zaka mata Wanda zai wanke shegen cikin nan , domin ni bana bukatar hada zuri'a da wannan dan iskan yaron,da daughter ta haife wannan cikin gara taje ta yo cikin shege a waje ta haifa, yafi min alheri akan ta haifi cikin wannan tsinanan yaron Aslam".
Zee tunda Dr ya ambaci cikin jikin ta nanan wani irin farin ciki ya lullubeta , ta shiga yiwa Allah godiya, amma jin kalaman dake fitowa daga bakin Dad yasa ta saurin dagowa ta kalle shi,.
Dr mamakin dad ne ya cika shi kicin mamaki yace"ba cikin aure bane, ma'ana cikin sunnah" dad yace "eh" Dr yace "meyasa make son a zubar ku barshi mana , idan aka kara mata wani alluran zubar da ciki akan Wanda akayi da mahaifarta baida kwari zai iya samun matsala" dad yace" ba komai ayi ranar biyan buqata rai ba'a bakin komai yake ba, na gwammace ta rasa mahaifar ma gaba daya da ta haifi wannan la'a nannen cikin" Dr yace "A'a fa Alhaji rabo yana kisa fa , tunda kaga cikin nan duk gwagwar mayar da yasha bai fita ba Allah ya kaddara rayayye ne idan ka matsa akan a fitar dashi akwai matsala" Dad cikin rufewar ido yace" kayi abinda na umarce ka Dr ko nawane zan biya ka," daga kafada Dr yayi alamar l don't care tunda na gaya maka gaskiya kaki ji ɗinan,.
Wani ruwan allura ya zuka a sirinji, ya saita daidai adadin yawan da ake so na alluran ya nufo zee dashi........... ..
Oum ummeetarh
07041130088
Share
And
Comment
Fisabillilah🙏.
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu}
Page 79 & 80
Wani uban tsalle zee ta daka, nan take sai gata a bakin kofar toilet, kamar ba ita bace kwance shame shame ba lafiya, da kallon mamaki duk suka bita, Dad yace"meye haka daughter ki tsaya ya miki allura mana, ki rabu da wanna cikin da ke wahalar min dake" girgiza kai tayi tace"no Dad bana so kar a zubar inason abuna, zan haifeshi inason cikina" sanƙare wa Dad yayi yama kasa furta ko kalma ɗaya tsabagen mamakin, yace "daughter pls kar muyi haka dake, ki taimakeni a cire cikin nan kinfi kowa sanin yadda na tsani mahaifin cikin nan , bazan iya jurar haɗa zuri'a dashi ba," maƙe kafaɗa tayi kamar wata karamar yarinya yar two years, mom Ce ta kara da cewa"haba daughter kizo mana kinga munbar Dr a tsaye fa " still kin zuwa tayi haka suka shiga rarrashinta da tsoratar da ita akan maganar haihuwa da irin azabar da zata sha, amma ta.musu ƙememe, ta gwammace ta sha ko wacce irin azaba Ce indai baza ta mutu ba akan ta sha azabar rabuwa da Aslam, tasan idan Allah ya taimaketa ko ta dalilin wannan cikin na jikinta dole wata rana zata sake haɗuwa da Aslam ɗinta.
Dr kam ganin sunata lallshinta ta ki yarda , ya ajiye sirinjin ya zare safar dake hannun shi, ya shiga haɗa kayan shi don yana da gurin zuwa da yawa.
~9ja~
Yau Aslam ya cika kwana uku da farkawa, jiki alhamdulillahi yana samun sauki sosai, dan zuwa yanzu yakan mike tsaye da kanshi ya shiga toilet, yana samun kulawa sosai gurin likitoci da kuma yan uwanshi,.
A gida kuwa shirye shiryen biki ake tayi ba kama hannun yaro , tuni baƙi sun fara sauka daga garuruwa mabanbanta, ranar asabar da karfe goma ne za'ayi daurin aure a babban masallacin juma'a dake minna.
Gayyata kam ko ta ina yinsa ake gaba ɗaya gari ya dauka da maganar wannan daurin aure na amare biyar ya gama baibaye garin minna da kewaye , hatta gidajen radio maganar da suke yi kenan a yan kwanakin na, haka gidan TV. NTA minna, duk wata kafar sada zumunta , saida maganar bikin nan ya leka,.
Ba wani program za'ayi sosai ba, saboda matsalar rashin lafiyan Aslam badan haka kam , program din da suka shirya yi yakai bakwai, yanzu kam ummi ta shirya mother's day , sai walima, sai kumbo, sai kuma kidan kwarya da za'ayi ranar yinin biki.
Shiru falon ya dauka kowa da irin tunanin da yake sakawa a zuciyar shi, Alhaji Mallam ne yayi gyaran murya, dukkansu suka maida hankalin su a kanshi , Cikin muryar shi ta dattijan da tsantsar ilimin addini ya ratsasu ya soma cewa"a gaskiya Aslam ka aikata babban kuskure a baya amma alhamdulillahi tunda har ka gane gaskiya kuma ka nemi yafiyar wadanda ka bata wa, saidai abinda zan fada maka shine kayi hakuri da Asma'u, tunda kaga haka watakila ita ba alkhairi bace a gare ka , maganar zabin da Alhaji baba yace zai maka ina mai baka shawara da ka karba da hannu bibbiyu , na tabbata zata zame maka farin ciki, kuma ta sakaka ka manta da cewa ka taba son Asmah a rayuwar ka,"
Aslam ya sauke ajiyar zuciya cikin sanyin murya yace"Alhaji a halin yanzu na Riga na cire rai da rayuwata, tunda har na rasa Asmah, domin kuwa itace rayuwata, amma duk da haka nayi farin ciki da zabin ku kuma na karba da hannu bibbiyu , kuma insha Allah zakuyi alfahari da ni a karo na biyu, nasan baza ku taba zabar min abinda zai cutar dani ba wancen karan ma , kuruciya da wauta ne ya sakani aikata aikin danasani,"
Alhaji baba dake laɓe a bakin kofa yana sauraran komai sauke ajiyar zuciya yayi sanna yasa kai ya wuce abinshi bai jira Mallam ba don fushi yake yi da shi ko mai ya hada su ohoo nan gaba zamuji.
~MALAYSIA~
Yau kimanin sati uku kenan da barowarta 9ja , tunda ta saka kafarta a cikin gidan bata kara lafiya ba, hoton yanayi da ta baro Aslam a ciki a police station ya ki fita daga kwakwalwarta, kullum Daren duniya kuka take kwana , ji takeyi da da hali da ta koma 9ja gurin mjinta ta rungume abinta da hannu bibbiyu, amma ina lokaci ya kure mata domin iyayenta babu abinda suka tsana sama da Aslam a duniya wayar ta ma tuni Dad ya amsa ya canja mata wani da wasu layukan, yanzu bata da buri daya wuce ta samu lambar beebalo ta kirata tasan beebalo mai kaunarta Ce zata iya mata duk abinda ta saka ta, mom ne ta turo kafar dakinta ta shigo hannun ta dauke da plat shake da kayan marmari yankakku, masu sanyi, zama tayi a bakin gadon da take ta mika hannun ta taba wuyanta, jikin na nan da zafin kau kamar ko yaushe , tunda ta dawo Malaysia bata kara lafiya ba ga kukan da ta aura tanayi kullum dare ,ga kuma rashin cin abinci,ko ruwa bata iya sha saita amayar fruit kadai take iya CI ta zauna lafiya shima idan taci da yawa sai sun dawo, ga kuma wani tsinkakken miyau dake addabarta, wannan lamari ya matukar daga hankalin iyayen zee, sunje asibiti ance fever ne,.
Yau dai sukayi da wani babban likitan mata Dr habu sarki, kan cewa zaizo har gida ya dubata, kwararren likita ne da samun ganin shi ko Malaysia sai wane da wane, yasan aikinsa sosai ba karamin wuya Dad yasha ba kafin ya samu Dr habu sarki ya amsa gayyatar shi, saida ya zube makudan kudade bana wasa ba,.
Tasar da ita mom tayi tana bata fruit din abaki tana sha kadan kadan , suna cikin haka dad ya shigo dakin , ya sanar dasu isowar Dr, mom tace saidai ya shigo nan ya dubata kaga jikin ba karfi baza ta iya sauka kasa ba ,
Haka ko akayi Dr ya shiga har dakin zee, babu kayan kirki a jikinta kayan bacci ne mai shara shara kanta babu dankwali amma iyayen ta ko a jikin su, dauke kai Dr yayi daga kallonta domin shidai musulmine dan 9ja kuma ba fasiki bane hasalima tare yake da iyalinsa suke zaune anan Malaysia,
Tambayoyi ya shiga mata akan abinda ke damunta tana bashi amsa, yana rubutawa,akan yanayin da take ji ajikinta, bayan ya gama ya bukaci miyanta da fitsari ba bata lokaci aka bashi na'urorin daya zo dashi ya dauka ya shiga gwaje gwaje akan miyau da fistarinta , yana gamawa bayan ya samu amsar abinda yake nema ya kalli Dad yace"Alhaji abdussalam, daughter ka tana dauke da juna biyu ne karami, Wanda ke bata wahala ,duk wadannan abubuwan da takeji a jikinta saboda ciki ne laulayi takeyi"
Cikin tsnananin tashin hankali da kiɗami dad da mom har suna hada baki wurin cewa ciki kuma Dr, Dr yace" yes tana da ciki tabbas" mom tace"Dr wani irin ciki kuma kadai sake gwadawa dakyau"nanta labarta mishi batun zubar da cikin da zee tayi, Dr yace "ana samun haka Ai alluran da wancen likitan ya mata bamai karfi bane kuma ba'ayi wankin ciki ba , to cikin na nan baiyi komai ba saidai yadan koma baya ,ma'ana ya zuba, watannin shi sun ragu,".
Dad da mamaki ya gama kashe shi yace to Dr yanzu abinda nake so dakai"allura zaka mata Wanda zai wanke shegen cikin nan , domin ni bana bukatar hada zuri'a da wannan dan iskan yaron,da daughter ta haife wannan cikin gara taje ta yo cikin shege a waje ta haifa, yafi min alheri akan ta haifi cikin wannan tsinanan yaron Aslam".
Zee tunda Dr ya ambaci cikin jikin ta nanan wani irin farin ciki ya lullubeta , ta shiga yiwa Allah godiya, amma jin kalaman dake fitowa daga bakin Dad yasa ta saurin dagowa ta kalle shi,.
Dr mamakin dad ne ya cika shi kicin mamaki yace"ba cikin aure bane, ma'ana cikin sunnah" dad yace "eh" Dr yace "meyasa make son a zubar ku barshi mana , idan aka kara mata wani alluran zubar da ciki akan Wanda akayi da mahaifarta baida kwari zai iya samun matsala" dad yace" ba komai ayi ranar biyan buqata rai ba'a bakin komai yake ba, na gwammace ta rasa mahaifar ma gaba daya da ta haifi wannan la'a nannen cikin" Dr yace "A'a fa Alhaji rabo yana kisa fa , tunda kaga cikin nan duk gwagwar mayar da yasha bai fita ba Allah ya kaddara rayayye ne idan ka matsa akan a fitar dashi akwai matsala" Dad cikin rufewar ido yace" kayi abinda na umarce ka Dr ko nawane zan biya ka," daga kafada Dr yayi alamar l don't care tunda na gaya maka gaskiya kaki ji ɗinan,.
Wani ruwan allura ya zuka a sirinji, ya saita daidai adadin yawan da ake so na alluran ya nufo zee dashi........... ..
Oum ummeetarh
07041130088
Share
And
Comment
Fisabillilah🙏.
💖DAMA TA BIYU💖
BY
~AYSHA NALADO~
FREE BOOK
{Nasadaukar da wannan book din ga duk wacce ta rasa mahaifiya, Allah kajiqan iyayen mu}
Page 79 & 80
Wani uban tsalle zee ta daka, nan take sai gata a bakin kofar toilet, kamar ba ita bace kwance shame shame ba lafiya, da kallon mamaki duk suka bita, Dad yace"meye haka daughter ki tsaya ya miki allura mana, ki rabu da wanna cikin da ke wahalar min dake" girgiza kai tayi tace"no Dad bana so kar a zubar inason abuna, zan haifeshi inason cikina" sanƙare wa Dad yayi yama kasa furta ko kalma ɗaya tsabagen mamakin, yace "daughter pls kar muyi haka dake, ki taimakeni a cire cikin nan kinfi kowa sanin yadda na tsani mahaifin cikin nan , bazan iya jurar haɗa zuri'a dashi ba," maƙe kafaɗa tayi kamar wata karamar yarinya yar two years, mom Ce ta kara da cewa"haba daughter kizo mana kinga munbar Dr a tsaye fa " still kin zuwa tayi haka suka shiga rarrashinta da tsoratar da ita akan maganar haihuwa da irin azabar da zata sha, amma ta.musu ƙememe, ta gwammace ta sha ko wacce irin azaba Ce indai baza ta mutu ba akan ta sha azabar rabuwa da Aslam, tasan idan Allah ya taimaketa ko ta dalilin wannan cikin na jikinta dole wata rana zata sake haɗuwa da Aslam ɗinta.
Dr kam ganin sunata lallshinta ta ki yarda , ya ajiye sirinjin ya zare safar dake hannun shi, ya shiga haɗa kayan shi don yana da gurin zuwa da yawa.
~9ja~
Yau Aslam ya cika kwana uku da farkawa, jiki alhamdulillahi yana samun sauki sosai, dan zuwa yanzu yakan mike tsaye da kanshi ya shiga toilet, yana samun kulawa sosai gurin likitoci da kuma yan uwanshi,.
A gida kuwa shirye shiryen biki ake tayi ba kama hannun yaro , tuni baƙi sun fara sauka daga garuruwa mabanbanta, ranar asabar da karfe goma ne za'ayi daurin aure a babban masallacin juma'a dake minna.
Gayyata kam ko ta ina yinsa ake gaba ɗaya gari ya dauka da maganar wannan daurin aure na amare biyar ya gama baibaye garin minna da kewaye , hatta gidajen radio maganar da suke yi kenan a yan kwanakin na, haka gidan TV. NTA minna, duk wata kafar sada zumunta , saida maganar bikin nan ya leka,.
Ba wani program za'ayi sosai ba, saboda matsalar rashin lafiyan Aslam badan haka kam , program din da suka shirya yi yakai bakwai, yanzu kam ummi ta shirya mother's day , sai walima, sai kumbo, sai kuma kidan kwarya da za'ayi ranar yinin biki.